Wednesday 13 December 2017

JUYIN JUYA HALIN HAUSAWA A BURKINA FASO

Daga Rabiu Muhammad (Abu Hidaya) Director Al-Huda Women Literacy
Center Kano-Nigeria Abu ne sananne cewa kasar Hausa tana girma
haka ma harshen wanda yana
cikin manyan harsunan Afrika har wasu na kiran
kasar Hausa da Biladin Sudan
kuma bincike ya nuna Hausawa suna yin fatauci
daga wannan zango-zuwa wani zango don gabatar da harkar kasuwanci da sauran
al'amuran rayuwa wannan ne
dalilin ma da wasu suke ganin hausawa sun zama
mazauna wasu kasashen saboda
dadewa ta harkar kasuwanci, har ila yau wannan
rubutu nawa zai gasgata wannan nazari na masana in da Hausawa suke a
kasar Burkina Faso kuma zai
karawa masu bincike damar sanya kasar cikin
kasashen da ake amfani da
harshen Hausa. Kamar yadda tarihi ya tabbatar bahaushe ba rago
ba ne, mutum ne da yake da
hikima da kuma yin sana'o'in dogaro da kai, a
saboda da haka ne yake yin
fatauci daga wannan gari zuwa wani gari don yin
kasuwanci, har zuwa wasu kasashen kamar Sudan, Ghana, Kamaru Chadi da
sauransu, a irin wannan
tafiye-tafiyen kasuwanci wasu suke yin aure a
wasu kasashen, wasu kuma
kasuwancinsu ya kan yi karfi a wurin sai su zauna
sai lokaci zuwa lokaci za su dinga ziyartar gida, a haka har zamani ya tafi da
su, to kamar yadda
yake a sauran kasashe haka ma ya faru a kasar
Burkina Faso Bayan tsawon
lokaci da hausawa suke zuwa kasar domin
kasuwanci lokaci ya ba su dama har sun samar da wani zango wanda ya
game ayarinsu
da kabilarsu wuri guda inda
suke gabatar da sha'aninsu cikin farin ciki da
walwala kamar bikin suna
aure da kuma sauran shagulgula na ibada kamar
bikin karamar sallah da babba har izuwa Maulidi da sauransu kuma sun auri wasu
kabilu da suke kasar,har
ila yau suna da tsarin sarki da 'yan majalisarsa a
cikin zangon. Idan ka shiga wannan wurin na zango za ka ji
cewa kamar a kasar Hausa ka
ke, domin yawan da hausawa ke da shi a wannan
wuri, sun ci gaba da wanzuwa
a wannan wuri karni bayan karni inda da dama
wasu idan aka ce su koma garuruwan da suka zo ba za su iya gane asalin
gurbin da ahalinsu suke ba,
saboda nisan lokaci, domin tun kaka da kakanni
suke wannan wuri har izuwa
lokacin mulkin shugaban Kasa Bless komfore
wanda ya rusa musu tsarin iyali da jin dadi ta hanyar rushe musu wannan gari da
suke kira zango, a
yunkurinsa na samar da ci gaban zamani a birnin
wagadugu a shekarar 2003 Wannan aiki da shugaba komfore ya yi ba karamin
rusa kabilar hausawa ya yi
ba a Burkina faso duk da cewa ya ba su sabon
wurin da za su koma amma da
yawansu ba su koma ba saboda suna ganin wurin
ya yi musu nisa, sun ce wai da a ce wurin da aka ba su ya yi hanyar kasar
Hausa ne to da za su iya
komawa amma wannan sabon wuri da aka ba su
ya kara musu nisa da gida ba za
su iya komawa ba, a sabili da haka ne sai mafi yawa
daga cikinsu suka famtsama cikin kasa, wannan shi ne farkon
rikicewar sanin kansu, kamar
yadda na fada a baya wasu daga cikin hausawan
waccan lokaci sun auri wasu
kabilun kasar to sai hakan ya bayar da damar
gurbatar harshen na su ba kamar yadda suke a tsohon zangon ba, wasu ma
da suke wasu garuruwan da ba
su ci gaba da harshen ba sai ya bace musu gaba
daya sai 'yan kalilan ne
suke jin sa, wadannan garuruwa kuwa sun hada
da Koufela da Fadar Gurma da Kantchari da kuma Zangoten su dama ba su a cikin
tarayyar zangon da aka
zauna, don haka a kabila kawai suke hausawa
amma a rukunin harshen sun
baude daga harshen Hausa na asali sai dai kana iya
gane wasu daga sunayen zuriyarsu kamar Kano ko Makeri da kuma Katsina
har yanzu akwai wadanda suke
amfani da ire-iren wadannan sunaye a cikin
sunayensu. Amma duk da haka wadanda suka yi saura a cikin
birni sun ci gaba da gabatar
da zumunci kamar yadda su ke yi a tsohon zango,
misali idan aka yi wa mutum
haihuwa to a ranar suna duk inda bahaushe yake
zai zo a yi taron suna da shi haka ma bikin aure ko jana'iza da dai sauran
sabgogin lokaci zuwa
lokaci. Kamar yadda na ambata a baya wasu daga cikin
hausawan Kasar Burkina Faso
sun riga sun bace don haka ragowar da suka yi
saura suma sai guguwar da ta
tafi da yan'uwansu ta taso musu ta hanyar aurensu
da kabilar Musawa take yi wanda kuma harshen Musanci shi ne babban
harshen kasar, abin da ya faru shi
ne, cikin biyu idan har ka ji mutum ba ya faransanci
ka tabbatar musanci
yake yi domin su ne manyan harsunan da ake
amfani da su a kasar ta Burkina, amma dai ana samun wani sa'i a yi harshen Jula
(Babban harshen kasar Mali)to
wannan alakar aure da ta shiga tsakanin hausawa
da kabilar Musawa ta yi
tasiri kwarai da gaske domin za ka shiga gidan
hausawa zalla ka ji suna yin musanci, dalili kuwa shi ne, yarinyar gidan dan
kabilar Musawa take aure
don haka idan ta zo da yaranta gida dole ne ta yi
musu harshen mahaifinsu
saboda shi suke ji, su ma kuma kakanninsu
harshen dai za su yi musu kenan, wani karin cin karfi da harshen
Musanci ya yi wa
harshen Hausa a Burkina
Faso shi ne auren kabilar musawa ba shi da
wahala, kusan ana iya cewa duka
dauka ne, wato su da ka ga yarinyarsu kana so to
ba su damuwa da abin da ka ke da shi duk kankantar abin hannunka kawai za a
daura aure, wani sa'in ma
daga wajen tambayo auren ake daura auren,
wannan sauki ya sa da dama daga
cikin hausawa maza sun auri mata kabilar Musawa
to da yake hausawa ba su da yawa sosai a kasar kuma sun warwatsu cikin kasa
sai matayensu ba su jin
harshen Hausa don haka wajibi ne duk namijin da
ya auri Bamusa ya ci gaba
da yin harshen musanci da ita a gidansa haka ma
idan ta haifi yaro da wannan harshen zai tashi domin ita ke reno da
kuma hira da shi a ko da
yaushe, a bangaren matan hausawan ma haka
idan Bamushe ya aure ta to wajibi
ne Musanci za ta yi da shi haka 'ya'yansu, wannan
abu ba karamin ci wa dattawan hausawan Burkina faso tuwo yake a
kwarya ba, suna ji suna gani
harshensu zai mutu, wasu da suka ga haka sai
suka nufi garuruwansu da ke
kasar Hausa kamar Zamfara, Sokoto, Katsina Kebbi
da kuma Kano cikin ikon Allah wasu sun samu danginsu daga nan suka yi
zamansu a gida, dama hausawa
na cewa"komai dadin garin wasu naka ya fi shi".
Ganin haka sai wasu daga
cikin dattawan Hausawa wadanda ba su da inda ya
wuce kasar kuma harshen na su ya zama har kasa don yana cikin harsuna sittin
da uku da kasar ta fitar
a cikin jadawalin kabilun da ta yarda yan asalin
kasar ne, kuma a nan aka
haife su har su ma sun yi jikoki ga shi kuma
kasuwancinsu da aikinsu a nan yake sai suka kafa wata kungiya wadda suka
sanyawa suna So Dangi, inda suke
tattaunawa da sauran hausawa da suke wasu
garuruwan kasar, manyan abubuwan
da suke tattaunawa shi ne yadda yaransu za su
dinga magana da harshen uwa a tsakakinsu da kuma auren junansu babban abin
da suka cimma shi ne sanyawa
inda suka fi yawa sunan tsohon wurin da suka
baro wato Zango. To da yake kowa yana sha'anin gabansa kuma
suna mabambanta wurare sai
wannan yunkuri bai yi armashi ba kamar yadda
suka yi masa fata. Hasalima
sarakunan na su suna wuraren daban-daban
kamar sarkin Zango da kuma sarkin Hausawa, haka dai aka ci gaba da
tafiya har izuwa
shekarar 2016 in da
matasan kabilar hausawa suka gano cewa jirgin da
suke ciki fa baya bisa
hanyar da ayarinsu suke fata, wannan hange ya
samu ne daga wani matashi da ake kira Abdourahmane Nagarba wanda yake da
digiri biyu a fannin harshen
Ingilishi da kuma Faransanci daga nan sai ya yi kira
ga ragowar matasan
hausawan cewa ya kamata su kafa wata
makaranta da za su dinga koyar da harshen Hausa ta hanyar rubuta shi da kuma
karanta shi, saboda su koyar da
ragowar yan'uwansu da ba su jin harshen da kuma
iya rubuta shi, wannan
tunani na sa ya samu karbuwa a wajen iyaye mata
da matasa da kuma dattawan kabilar hausawan kasar, da wannan tunani aka
kafa makarantar Hausa ta farko
a kasar Burkina Faso cikin babban birnin kasar mai
suna Wagadugu, an kuma
sanyawa wannan makaranta suna kungiyar
Makaranta wadda a turance suke kira(Association Makaranta)aka kuma damka
ragamar makarantar a hannunsa
tunda shi ne ya samar da tunanin duk da cewa ba
hausar ya yi nazari ba a
jami'a amma haka ya dukufa wajen koyawa
daliban yadda za su yi rubutu da kuma furta wasu kalmomi, ya kan yi bincike a
kafafen Intanet don samun salo
da dabarun yadda ake koyarwa ya kan kuma
tuntubi masana wadanda ya ci karo
da su a yanar gizo game da abin da ya shige masa
duhu har ila yau ya samu mallakar wasu littattafai wadanda suke masa
jagora wajen koyar da Hausar,
babban aikin da ya yi shi ne, kokarin kulla alaka da
wasu hukumomi da
ma'aikatu na ilmi a cikin Burkina Faso da wasu
kasashen ketare kamar Nijar da Nijeriya, sannu a hankali sai wannan makaranta
ta samu karbuwa a ko'ina
cikin babban birnin Wagadugu mutane da dama
suka dinga aiko da 'ya'yansu,
lokutan da ake gabatar da karatun su ne: ranakun
Asabar da Lahadi saboda yawanci daliban makarantar suna karatu a jami'a
wasu kuma sakandire. Wannan makaranta ta ci gaba da bunkasa har cikin
garuruwan kasar inda
ragowar hausawa suke. Ga sunan wasu garuruwan inda Hausawa suke da
zama a Burkina Faso kafin
zuwan turawa. koufela: Kantchary(Kan Cari) Namounou(Asalin sunan garin
shi ne Namu ne
saboda suna jin garinsu ne na
Hausawa zalla) Kaya Dori Gorom-Gorom Ouahigouya Bobo-Dioulasso da kuma
Nouna. wadannan
garuruwa bayan sun samu labarin
wannan makaranta sai suka nuna sha'awarsu
akan su ma idan da hali a je a
kafa musu wannan makaranta ta koyar da Hausa
da al'adu don suna kishirwar abi NEMAN AGAJI DAGA BURKINA FASO ZUWA
NIJERIYA Bayan da wannan kira na wadannan garuruwa ya
isa ga makarantar Hausa ta
farko da ta ke Wagadugu sai hukumar makarantar
suka nemi agajin malamin da
zai koyar da kuma inganta masu Hausar da suke
nazari a wagadugu in ya so a bai wa daliban farko horon da su kuma za su
baiwa ragowar mutanen da suke
wadancan garuruwa ma'ana su zama malamai a
can, to kamar yadda na fada a
baya shi jagoran makarantar wato Abdourahmane
Nagarba ya yi kokari ya samu alaka da wasu kasashe da hukumomi tare da
kungiyoyi musamman masu nazarin
harshen Hausa cikin wadanda ya kulla a alaka da
su akwai Makarantar Al-Huda
Women Literacy Center da ke Nijeriya a Kano, inda
kuma ita ce makaranta ta farko da ya nemi agajinta don ta bayar da malamin
da zai ba da wannan horo,
bayan cimma yarjejeniya ni ne malamin da ya dauki
nauyin gabatar da wannan
tafiya domin bayar da wannan horo, daga nan
kuma sai kungiyar Arewa Community da ke Afrika ta yamma wadda ta ke da
babban ofis a kasar Guinee
Bissau ta bayar da tallafin guzuri ga malamin da zai
tafi. YADDA NA GA BIRNIN WAGADUGU Na isa kasar Burkina Faso cikin babban birnin
kasar wato Wagadudu ranar
alhamis 29-12-2016 babban abin da na ya burge
ni a kasar shi ne kiyaye doka
da 'yan kasar suke yi haka kuma tsaftar birnin ya
kayatar da ni kwarai kuma karamcin mutanen garin ya burgeni sosai, wani
abin mamaki da na gani shi ne
yadda mafi yawan masu hawa keke a kasar mata
ne, duk da cewa bani jin
harshen 'yan kasar amma na gabatar da komai na
wa cikin walwala, bayan na isa ba mu dau dogon lokaci ba a washe gari ranar
juma'a da misalin karfe 4
na yamma mu ka fara karatu, da yake daliban sun
iya rubutu da karatu karin
ilimi ne da horo kawai za a ba su, don haka
abubuwan da mu ka yi nazari su ne:- -Ka'idoji da dokokin rubutu da
Karatun Hausa. -Nahawu da sarfun Hausa. -Lissafi da Hausa(Tarawa/Kari,
Debewa, Ribawa da
Rabawa) -Al'adun Hausa(Bukukuwa,Wasanni,Abinci) -Koyarwar Manya. Mun
kammala wannan bita a ranar laraba
11/1/2017 wani abin burgewa a wannan makaranta shi ne
yadda daliban suke son karatun
sosai, sukan yi nishadi kwarai a lokacin da ake
gabatar musu da darasi
sannan gasu da yawan tambaya kan abin da ya
shige musu duhu, da kansu suka kafa dokar hana yin wani harshe a cikin
a ji idan ba
Hausa ba, kuma Ofishin
Jakadancin Nijeriya a kasar ya kan ziyarci dalibai
lokacin gabatar da
karatun na su, har ila yau a lokacin gabatar da
hutun rabin lokaci na karatu akan baiwa duka daliban abin ci da sha don
samun karsashinsu,
sa'annan dattawan hausawan su ma wani lokaci su
kan ziyarci wannan
makaranta a gabatar da darasin tare da su. Manufar dai kafa wannan
makaranta ita ce ceto
harshen Hausa da al'adunsa
wanda suke da barazanar bacewa daga cikin
harsunan kasar da kabilunta, da
fatan ragowar masu ruwa da tsaki game da abin da
ya shafi harshen da Hausawa a duk in da suke a duniya za su tallafawa
wannan yunkuri na
Hausawan Burkina Faso. AL'ADUN HAUSAWAN BURKINA FASO Kamar sauran
kabilu a kasar su ma hausawa suna
gabatar da al'adunsu
musamman lokacin aure da suna da kuma sauran
shagulgulan bikin karshen
shekara,sai dai yadda suke gabatar da wasu
al'adun na su ya sha bamban da yadda na ke gani a kasar Hausa, domin su idan za
su yi aure ango ne yake
yin kayan daki haka kuma a lokacin daurin aure
ango zai mike a yi masa
tambayoyi game da aure sai kuma waliyansa su
mike tare da waliyan amarya su ma kowa ya gansu sannan su gaisa kowa yana
kallo daga nan sai a dauko
abinci a raba jama'ar da suka zo daurin aure. A bangaren bikin suna ma
yana da na shi al'adar
kamar yadda na gani a ranar
suna maza kan taru a kofar gidan wanda aka yi
haihuwa a yi radin suna daga
nan sai mutane su yi ta zuwa suna taya mahaifin
jaririn murna har zuwa yamma, KARSHE Na dawo gida Nijeriya ranar
Asabar cikin farin ciki
da koshin lafiya. Ina godiya ga kungiyar Arewa Kwaminiti reshen
afrika ta yamma da kuma
Ofishin Jakadancin Nijeriya a Burkina da
takwaransa na kasar Nijar da kuma
daliban makarantar Association Makaranta, tare da
ma'aikatar Ilimin Manya ta jihar Kano a tarayyar Nijeriya da kuma hukumar
makarantar Al-Huda Women
literacy Center Kano.

No comments:

Post a Comment