Saturday 16 December 2017

AN YI BIKIN KADDAMAR DA LITTAFIN TARIHIN MARIGAYI ALHAJI ALHASSAN DANTATA

Daga Rabi'u Muhammad (Abu Hidaya)



Bikin kaddamar da littafin Alhaji Alhassan Dantata ya samu tagomashin
halartar manyan mutane daga sassa daban-daban na kasar Nijeriya, taron
dai an fara shi da misalin karfe 10am na safiyar Asabar 16\12\2017 a
babban dakin taro na Meena Event dake kan titin Lugard Road. Domin
kaddamar da littafin da aka rubuta game da rayuwar marigayi Alhaji
Alhassan Dantata tare da gudummuwarsa wajen ci gaban tattalin arzikin
Afrika.
AlHassan Dantata mahaifine ga hamshakin dan kasuwar nan na Kano wato
Aminu Alhassan Dantata shugaban rukunin kamfanonin Dantata, kuma kaka
ne a wajen fitaccen dan kasuwar nan na Afrika wato Alhaji Aliko
Dangote GCON, kafin rasuwarsa ya kasance babban dan kasuwar da ya yi
harkar kasuwanci tun daga kasar Hausa har zuwa kasashen larabawa.
An haifi Alhaji AlHassan Dantata a shekarar 1877 ya kuma rasu a watan
Satumba shekarar 1955 ya rasu ya bar 'yaya da dama, daga cikin
zuri'arsa Alhaji Aminu Alhassan Dantata ne kawai ya rage.
Marubucin wannan littafin wato Hassan Sunusi 'yan biyu Dantata, wanda
ya kasance dan'uwa ne ga Hajiya Mariya Sunusi Dantata wadda ita kuma
ta kasance mahaifiya ga Alhaji Aliko Dangote. Ya yi matukar kokari
wajen rubuta wannan littafi musamman wajen shiga lungu da sako don
tattaunawa tare da tattaro muhimman bayanai game da tasirin
kasuwancinsa da gudunmuwarsa ga Kasuwanci da 'yan kasuwar Afrika.
Tagwayen littattafan sun kasance cikin harshen Hausa da turanci, na
farkon wanda shi ne na Turanci an sanya masa suna (The Life And Times
Of Alhaji AlHassan Dantata, A Merchant Par Excellence) sai kuma na
Hausa mai suna AlHassan Dantata Tarihin Rayuwarsa Da Gudummuwarsa Ga
Tattalin Arzikin Afrika.
Alhaji Aminu AlHassan shi ne ya fara jawabi a wurin taron, inda ya ce
"duk da cewa littafin kakansa yana cike da kurakurai wanda bai kamata
a ce an yi bikin kaddamar da shi a wannan lokaci ba, kamata yayi a
bari a kammala gyare-gyaren da suke cikinsa, amma dai duk da haka
littafin ya zo a lokacin da yakamata domin tun tsawon lokaci ake ta
kira ga wasu daga cikin yaya da jikokin marigayi Alhaji AlHassan
Dantata da su yi wannan gagarumin aiki amma ba su yi ba, sai wannan
lokaci da marubucin ya yi, don haka yana alfahari da wannan aiki kuma
yana fatan alhari ga dukkan jama'ar da suka samu halartar wannan taro
kuma In sha Allah littafin za a sake duba shi domin shigar da abin da
ba a shigar ba".

Sai kuma Dakta Bello Sunusi Dantata wanda ya yi jawabin maraba ga
mahalarta taro da kuma takaitaccen jawabi na tarihin zuriar Alhaji
Alhassan Dantata.
Sai jawabi daga Dattijo Adhama inda shi ma ya bayyana irin amana da
taimakon da marigayi Alhaji Hassan Dantata ya shahara a kai.

Mamuda AlMustapha Dantata shi ne ya wakilci Alhaji Aliko Dangote
Dakta Abdullahi Umar Ganduje OFR
(Gwamnan Jihar Kano)

Malam Hassan Lamin Haidar shi ne ya yi sharhin littafin da cewa
"Wannan littafi fito da abubuwa da yawa game da kasuwa tun daga zuwan
turawa da harkar bayi da kuma bunkasar kasuwanci a Afrika, duk wanda
ya karanta wannan littafi zai samu abin dogora wajen fahimtar yadda
kasuwanci yake wato kalubalensa da kuma nasarorinsa" A karshe ya ce an
yi wannan sharhi ne a matakin farko nan gaba za a sake yin wani
sharhin bayan an gyara yan kurakuran ciki.

Bayan nan mutane da dama sun su yi jawabi a wajen taron irin su:
Gwamnan Jihar Kano
Justice Mamman Nasir
Malam Ibrahim Shekarau
Sarkin Shanun Damagaram
Mininstan Nijar
bayan kammala wadaccan jawabai kai tsaye bikin Kaddamar da Littafin aka shiga.
wadanda suka jagoraci kaddamar da su ne:
Alhaji Aliko Dangote 10M
Gwamnatin Jihar Kano 10M
Hajiya Mariya Sanusi Dantata 2M
Alhaji Aminu Alhassan Dantata 10M
Alhaji Sani Dangote 2M
Alhaji Sayyu Dangote 2M
Alhaji Tajuddeen Dantata 2M
Alhaji Sadik Dantata 2M
Alhaji Hassan Dantata 2M
'Yaya mata na Alhaji Aminu Alhassan Dantata 2
Ilyalan Alhaji Aminu Alhassan Dantata 2
Alhaji Abdussamad Isyaka Rabi'u 2.5M
Iyalan Mudi Dantata 1M
Iyalin Nasiru Dantata 1M
Janaral Abdussalam Abubakar 100k
Dan Bilki Kwamanda 100K
Alhaji Garba Sanusi Dantata100k
Alhaji Ahmad Sadauki 500k
Alhaji Mutari sanusi Dantata 100k
Iyalin amadu dantata 2M
Alhaji Alhassan Abdulkadir Dantata 1M
Durbin Kano 100k
Alhaji Nabahani 50k
Gambo Dan pass 100k
Hajiya Aishatu H Dantata 100k
Alhaji Sa'adi Hamidu Dantata 5M
Da wasu da dama wadanda suka saya.

Manyan baki da dama sun halarci taron, kadan daga cikinsu su ne:
Alhaji Aminu AlHassan Dantata
Alhaji Salisu Sambajo
Dakta Malam Ibrahim Shekarau(Sardaunan Kano)
Sheikh Ibrahim Khalil
Alhaji Dattijo Adhama
Hon. Ahmad S Aruwa
Alhaji Usman Alhaji
(Sakataren Gwamnatin Kano)
Sarakunan Zinder
Kanal Abubakar Mai Malari
(Shi ne ya wakilci tsohon shugaban kasa Janaral Abdussalam Abubakar)
Wakilin sarkin Nupe. Da sauransu.
An tashi taro da misalin karfe 1pm

No comments:

Post a Comment