Tuesday 5 December 2017

AN YI TARON AL'ADUN HAUSAWA NA DUNIYA A KASAR KAMARU(FESTI HOUSSA YOAUNDE 2017)

Daga Rabiu Muhammad(Abu Hidaya)

Babban birnin kasar Kamaru wato Yawunde ya yi cikar dango da dukkan
hausawan kasar Kamaru da wasu hausawan daga sassan duniya don halartar
taron bikin nuna al'adun Hausa da kuma bayyana matsayin bahaushe a
kasar Kamaru, taron dai wanda aka yi wa lakabi da "Festi Houssa"an
fara shi tun ranar 1 ga watan Disamba zuwa babban taron a ranar 2 ga
Disamba har zuwa 3 ga wata, kuma taron ya samu tagomashin sanya
albarka daga yan siyasar kasar da Sarakuna da 'yan Jarida da kuma masu
rike da mukaman gwamnati da manyan yan kasuwa irinsu Alhaji Aliko
Dangote da kuma al'ummar sauran jihohin kasar
a taron an gabatar da wasannin gargajiya na bahaushe da kuma jawabai
kan asalin bahaushe da kuma fitar da sarauniyar kyau da wasu
sha'anonin nishadi don nishadantar da mahalarta taro.
Taron dai an jima ana shirya shi tun a watan October 2017 kuma ya samu
karbuwa daga ko ina na kasar
kamar:
Garwa
Duwala
Yawunde
Gawondare da sauransu
kuma kasashe da dama sun samu halartar taron kamar:
Faransa
Nijeriya
Togo
Chadi
Burkina Faso
Senegal
Germany
Ghana, da sauransu, duk cewa taron ya gamu da kalubale da dama kafin a
yi shi, amma a jawabin wasu daga cikin mahalarta taron na ganin a
tarihin kasar Kamaru ba a taba samun al'ummar da ta shirya taron da
kabila daya suka hadu wuri guda ba har da na sauran kasashe kamar
wannan taro na al'adun hausawan duniya ba, taron ya samu hadin kai
daga dukkan sassan da ake ganin akwai hausawa a kasar, kuma gwamnatin
kasar ta yi namijin kokari wajen ganin an yi taron lafiya an gama
lafiya.
Kuma manyan kamfanonin sufuri da sauran ma'aikatu da masu kudi tare da
sarakuna su ma sun taka muhimmiyar rawa wajen ganin taro ya yi
armashi.
Babbar manufar taron dai ita ce sada zumunci da kuma jaddada halin
karamci da amana da jin tausayin juna tare da taimakon juna irin na
bahaushen da aka sani tun asali.
Taron dai shi ne na biyu da aka shirya game da Hausawan duniya, a
watan Afrilu 2017 ma an yi irin wannan taro a kasar Burkina Faso wanda
hukumar adana kayan tarihi da al'adu tare da hadin gwiwar kungiyar
Association Makaranta na Kasar suka shirya, ana kuma sa ran a shekarar
2018 za a yi irin wannan babban taro na al'adun hausawan duniya a
kasar Nijar jahar Damagaran.

No comments:

Post a Comment