0
WATA MARUBUCIYA TA KALUBALENCI SASHEN HAUSA NA BBC MASU SHIRYA GASAR RUBUTUN MATA TA HIKAYATA. Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya WATA MARUBUCIYA TA KALUBALENCI SASHEN HAUSA NA BBC MASU SHIRYA GASAR RUBUTUN MATA TA HIKAYATA. Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya

A jiya juma'a 26\10\2018 aka yi bikin bayar da kyautar zakarun gasar hikayata ta bbc Hausa. Bikin wanda ya gudana a dakin taro na Ladi K...

1
SARDAUNAN KANO VANGUARD SUN GANA DA SARDAUNAN KANO A KADUNA SARDAUNAN KANO VANGUARD SUN GANA DA SARDAUNAN KANO A KADUNA

A jiya laraba 10\10\2018 kungiyar Sardaunan Kano Vanguard suka gana da Dakta Malam Ibrahim Shekarau sardaunan Kano kuma wazirin raya kasar N...

WATA MARUBUCIYA TA KALUBALENCI SASHEN HAUSA NA BBC MASU SHIRYA GASAR RUBUTUN MATA TA HIKAYATA. Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya

A jiya juma'a 26\10\2018 aka yi bikin bayar da kyautar zakarun gasar hikayata ta bbc Hausa.
Bikin wanda ya gudana a dakin taro na Ladi Kwali a birnin tarayya Abuja wanda ya samu halartar manya baki daga sassan jihohin tarayyar Nijeriya.
A wajen bikin bayar da kyaututtukan gasar wanda sashen Hausa na bbc yake shiryawa duk shekara, fitacciyar marubuciyar Hausa kuma mace ta farko da ta fara rubuta littafin kagaggen labari na Hausa hajiya Hafsat M. A Abdulwahid ta kalubalenci sashen Hausa na bbc cewa bai kamata a ce an samu namiji a cikin alkalan da suke tace labaran ba, inda ta ce "an ce abu na mata ne zalla a dauki kane na Malumfashi an dora an ce shi ne shugaban tace labaran, mu gaskiya wannan bai yi mana ba. Tunda harka ce ta mata a nemi mace ta yi shugabanci, ba mu hana a sa shi a ciki ba, amma harka ta mata a sa mata, muna da mata fitattu da suka yi Hausa da sauransu" Sannan ta yi kira ga sashen cewa a daina gwamutsa Turanci da Hausa a lokacin bikin bayar da kyaututtukan.
Wannan dai shi ne karo na uku da sashen Hausa na bbc ya samu kalubale a tsawon shekara uku da yake shirya wannan gasa, shekarar farko kasar Nijar ta yi korafi da cewa gasar ta 'yan Nijeriya ce kawai, kuma alamu sun nuna hakan.
Shekara ta biyu wani manazarci daga jihar Katsina ya kalubalenci alkalan gasar gaba dayansu cewa labarin da ya zo na daya bai cancanci haka ba.
Sai ga shi a bana ma an samu irin wannan korafi ga sashen Hausa din da fatan masu ruwa da tsaki za su duba lamarin.

SARDAUNAN KANO VANGUARD SUN GANA DA SARDAUNAN KANO A KADUNA



A jiya laraba 10\10\2018 kungiyar Sardaunan Kano Vanguard suka gana da Dakta Malam Ibrahim Shekarau sardaunan Kano kuma wazirin raya kasar Nufe.
Taron wanda aka fara tunda misalin karfe goma na safiya a dakin taro na Marskhala Hotel da ke unguwar Kurmin Mashi a jihar Kaduna.
Bayan gabatar da jawabin maraba da mukaddashin shugaban kungiyar na kasa ya yi sai kuma uban taro wanda shi ne jagoran shirya taron wato Alhaji Nura Abdullahi Jos ya karbi abin magana ya sake yi wa mahalarta taro barka da zuwa da kuma babban bako mai jawabi Sardaunan Kano malam Ibrahim Shekarau.
Ya bayyana manufar taron da cewa don a taya mai girma sardaunan Kano murnar komawa jam'iyyar APC ne da kuma taya shi murna samun tikitin takarar dan majalisar Dattijai mai wakiltar kano ta tsakiya da jawabai masu yawa.
A jawabin nasa Sardaunan Kano ya bayyana babban jin dadinsa ga wanda ya shirya taron da kuma irin fuskokin da ya gani a taron ya kuma ce zai ci gaba da alfahari da mutanensa a ko'ina suke a Nijeriya da duniya baki daya.

Bayan kammala jawabinsa mahalarta taron sun yi masa tambayoyi masu yawa game da abin da ya shafi Nijeriya da ci gabanta a harkar siyasa, inda shi kuma ya bayar da amsa daya bayan daya.

Taron dai ya samu halartar duka shugabannin kungiyar Sardaunan Kano Vanguard na jihohi talatin da shida(36 States) da suke Nijeriya.
An tashi taro da misalin uku na yamma inda aka dauki hoton gamayya na mahalarta taron.