0
Daga Rabiu Muhammad (Abu Hidaya)

Wannan rubutu ya samo asali ne daga wani kira da wani dan dan'uwa
marubuci Usman Mani Kusumawa Kargeri, yayi min game da cewa yakamata
na yi dan rubutu game da sarakunan kasarsu ta Nijar game da hibbarsu
da kuma adalcinsu ga duk wanda ya kusance su, sakamakon yadda wasu
mutane suke ganin cewa Masarautar Agadez ba ta kyauta ba don ta hana
'yan fim din Hausa(Kannywood) zuwa kasarta da sunan shirin fim, saboda
wani Fim da kamfanin 2Effect Empire suka shirya mai suna DAN SARKIN
AGADEZ fim din da ya gaza cimma manufar sakon da ake son nunawa
jama'a, hasalima fim din tozarci ne ga masarautar da al'adunta.

Babu Shakka masarautun kasar Nijar kaffatanninsu masarautu ne masu
cike da haiba da kuma dimbin tarihi kuma masu adalci ga al'ummar da
suke shugabanta.
Duk mutumin da ya kasance mai bibiyar tarihi zai yarda kuma har ma ya
aminta cewa sarakunan kasar Nijar ba su da kyashi ko baiken jin cewa
sun taimake ka wajen samar da tarihi da kuma labarin da abin da ya
shafe su, kamar yadda na zama ganau ba jiyau ba kamar yadda hausawa ke
azancin magana da cewa wai "Gani Ya Kori Ji".
Bari na fara da Masarautar Sultan ta Damagaran a shekarar 2014 na
ziyarci fadarsa a wani rangadin bincike da nake yi wanda zai kai ni
har gaba da Agadez, Sultan Abubakar Sanda wanda yake mulkin kasar
Zinder yayi matukar farin ciki da zuwa na ya kuma bani masauki tare da
bani cikakken lokacin da muka zanta da shi na wani dogon lokaci, har
ya gayyace ni zuwa tarbar Ministan cikin gidan kasar wanda zai kawo
ziyarar aiki a jihar, amma rashin lokacin da ba ni da shi ban samu
damar amsa gayyatar ba, don a daidai lokacin yakamata a ce na isa
Agadez akan lokaci, bai damu ba ya yi min wannan uzuri sannan ya bani
sakon gaisuwa zuwa ga takwaransa na Agadez wato Sultan Ouamar Ibrahim
Oumar na Agadez mun yi bankwana da fatan idan na dawo na sake biyawa
fada na sanar da shi, hakan kuwa aka yi bayan na dawo na biya masa
abin mamaki sha tara arziki aka min a wannan fada cikin barkwanci da
raha sosai mu ka yi bankwana da shi da duk mutanen fadar.
Har ila yau daga cikin karamcin wannan sarki shi ne ya dauki nauyi
taron kaddamar da kungiyar hadaka ta kasashen Afrika mai suna
GIDAUNIYAR ZUMUNCI tare da bikin al'adun hausawa na duniya a jihar
Zinder a wannan shekara ta 2018.

Haka ma jihar Agadez bayan na isa masarautar na sanar da sultan zuwana
sai na wuce zuwa masaukina don hutawa saboda gajiyar hanya, bayan
kwana daya da zuwana,ina bacci da rana sultan ya aiko yana son za mu
gana ta hanyar Yariman Agadez Malam Ousseini dan Abbo, Sultan na
Agadez mutum ne mai cike da kwarjini da haiba ga izza wadda za ta nuna
maka shi cikakken sarki ne mai daraja ta farko, duk da cewa mu hudu ne
a fadar ta shi amma baya magana da ni kai tsaye hasalima bana jin abin
da yake fada sai idan ya yi magana a gaya min abin da ya ce, a haka
muka tattauna muhimman batutuwa, wani abin burgewa da wannan sarki shi
ne son jama'ar kasarsa da kyautata musu, mun yi tafiya da shi zuwa
dazuka (idan aka je daji a kasar Nijar ana nufin wasu garuruwa da suke
cikin duwatsu da sahara) don halartar taron addu'a na karshen shekara
da ake a kasar don neman zaman lafiya da wanzuwar arziki a kasar,
motarmu tana gaba ta sultan tana bayanmu sai muka wuce wasu mata da
kananan yara a hanya ga dukkan alamu wani garin da ke gaba da su za su
je, a cikin motarmu sai sakataren Malaman Jihar Agadez Malam Namadina
Alhaji Ousseini ya ce "Zai wahala Sultan bai tsaya yasa a dauko
mutanen nan ba", haka kuwa aka yi ba mu yi nisa ba sai muka ga ana
alamta mana cewa mu dakata, bayan mun tsaya muka dawo baya sai muka ga
Sultan ya sauko da kansa ya sanya an ba wadannan mutane mota guda
wadda ta dauke su tare da kayansu ta kai su garin da za su je.
Wannan abin ya matukar burgeni na kuma ji na kara kaunar wannan sarki.
A tsawon kwana uku da muka yi a dajin nan wallahi kusan ko yaushe duk
abin da aka kaiwa Sultan sai ya sanya an kawo mana da yake masaukanmu
suna dab da juna. Bayan an kammala wadannan addu'o'i ba fadarsa ya
dawo ba sai da ya wuce zuwa wasu garuruwa don ya gansu ya kuma
tattauna da su, bincikena ya gano cewa wannan sarki kusan koyaushe
yana cikin wadannan ayyuka na ziyarar mutanensa da kuma gabatar da
ayyukan da suka shafi ci gaban kasarsa duk da cewa akwai sarkin da aka
sanya don lura da wadannan garuruwa da ake kira A'ir mai suna Muhammad
Suleyman Anastafident, bayan mun dawo sarkin ya sake tambayata akwai
wani abu da nake bukata wanda ban samu ba? Na amsa da babu duk wani
aiki da ya kai ni na kammala shi har da ma ribar kafa.
A bangaren mutanen Agadez da Nijar kuwa babu wani abu da zan bayyana
su da shi sai dai na ce su mutane ne masu son jama'a da kuma girmama
baki da kaunar junansa, wani abu da ya sa nake kara yaba musu shi ne
yadda suka rike al'adunsu da kuma girmama tarihinsu.

A shekarar 2016 ma na ziyarci fadar sarkin Maradi tare da wani babban
dan kasuwa da ke Nijeriya don bude reshen harkar kasuwancinsa garin
Maradin babban abin da ya burge ni shi ne yadda mutanen fadar suka
karbe mu da karamci tare nuna jin dadinsu game da wannan abin alheri
da zai zo kasarsu, haka ma mahukunta jihar su ma sun nuna jin dadinsu
don har wakilin gunduma ya ba mu gayyata ta musamman zuwa gidansa amma
da yake muna sauri za mu wuce zuwa Niamey ne, ba mu samu zuwa ba, a
wannan bangare ma na yaba musu kwarai.

A saboda a haka a matsayina na Marubuci kuma Dan Jarida nake rokon duk
wani marubuci ko dan Jarida kai har ma da masu shirya fim su kasance
masu bibiyar tarihi da bincike tare da bibiyar masana kafin yin duk
wani aiki wanda zai shiga hannun jama'a saboda gudun irin abin da ya
faru a baya game da Fim din Dan Sarkin Agadez, da ma wasu daga cikin
rubuce-rubucenmu, Allah Ya jikan marigayi Gambu mijin Kulum mai wakar
barayi mun taba hadu da shi a jami'ar jihar Kaduna muna zantawa yake
nuna min rashin jin dadinsa da abin da wani marubuci yayi masa na
rashin adalci, ya ce marubucin ya rubuta karya game da shi da sunan
tarihinsa ba tare da kyakkyawan bincike ba.
Bana mantawa lokacin dana ziyarci wata fada a kasar Nijar din dai ta
sarki Ahmad Aghali Ibbah sarkin Tanhiya sun sanar da ni tarihinsu
tare da cewa duk abin da suka gaya min haka zan rubuta kar na rage kar
na kara, kun ga wannan ai shi ne adalci, wani abu da ya sake burgeni
da mutanen kasar shi ne lokacin da na je shan ruwa wajensu an samu
matsala, amma da na bayyana musu cewa ni bakon sarki ne sai suka kyale
ni na tafi abina.(Cikakken rahoton yana cikin labarin ziyararmu birnin
Tanhiya) A nan ma ya nuna cewa wannan sarki zaune yake da al'ummarsa
lafiya suna kaunarsa yana kaunarsu.
Da fatan wannan tsokaci zai sanya mu amfana wajen yin abin da zai zama
karbabbe a kan komai da za mu yi.

Post a Comment

Dear readers, after reading the Content please ask for advice and to provide constructive feedback Please Write Relevant Comment with Polite Language.Your comments inspired me to continue blogging. Your opinion much more valuable to me. Thank you.

TASIRI DA GUDUMMUWAR SARAKUNAN KASAR NIJAR WAJEN BUNKASAR AL'ADU DA ZAMAN LAFIYA A KASAR NIJAR

Daga Rabiu Muhammad (Abu Hidaya)

Wannan rubutu ya samo asali ne daga wani kira da wani dan dan'uwa
marubuci Usman Mani Kusumawa Kargeri, yayi min game da cewa yakamata
na yi dan rubutu game da sarakunan kasarsu ta Nijar game da hibbarsu
da kuma adalcinsu ga duk wanda ya kusance su, sakamakon yadda wasu
mutane suke ganin cewa Masarautar Agadez ba ta kyauta ba don ta hana
'yan fim din Hausa(Kannywood) zuwa kasarta da sunan shirin fim, saboda
wani Fim da kamfanin 2Effect Empire suka shirya mai suna DAN SARKIN
AGADEZ fim din da ya gaza cimma manufar sakon da ake son nunawa
jama'a, hasalima fim din tozarci ne ga masarautar da al'adunta.

Babu Shakka masarautun kasar Nijar kaffatanninsu masarautu ne masu
cike da haiba da kuma dimbin tarihi kuma masu adalci ga al'ummar da
suke shugabanta.
Duk mutumin da ya kasance mai bibiyar tarihi zai yarda kuma har ma ya
aminta cewa sarakunan kasar Nijar ba su da kyashi ko baiken jin cewa
sun taimake ka wajen samar da tarihi da kuma labarin da abin da ya
shafe su, kamar yadda na zama ganau ba jiyau ba kamar yadda hausawa ke
azancin magana da cewa wai "Gani Ya Kori Ji".
Bari na fara da Masarautar Sultan ta Damagaran a shekarar 2014 na
ziyarci fadarsa a wani rangadin bincike da nake yi wanda zai kai ni
har gaba da Agadez, Sultan Abubakar Sanda wanda yake mulkin kasar
Zinder yayi matukar farin ciki da zuwa na ya kuma bani masauki tare da
bani cikakken lokacin da muka zanta da shi na wani dogon lokaci, har
ya gayyace ni zuwa tarbar Ministan cikin gidan kasar wanda zai kawo
ziyarar aiki a jihar, amma rashin lokacin da ba ni da shi ban samu
damar amsa gayyatar ba, don a daidai lokacin yakamata a ce na isa
Agadez akan lokaci, bai damu ba ya yi min wannan uzuri sannan ya bani
sakon gaisuwa zuwa ga takwaransa na Agadez wato Sultan Ouamar Ibrahim
Oumar na Agadez mun yi bankwana da fatan idan na dawo na sake biyawa
fada na sanar da shi, hakan kuwa aka yi bayan na dawo na biya masa
abin mamaki sha tara arziki aka min a wannan fada cikin barkwanci da
raha sosai mu ka yi bankwana da shi da duk mutanen fadar.
Har ila yau daga cikin karamcin wannan sarki shi ne ya dauki nauyi
taron kaddamar da kungiyar hadaka ta kasashen Afrika mai suna
GIDAUNIYAR ZUMUNCI tare da bikin al'adun hausawa na duniya a jihar
Zinder a wannan shekara ta 2018.

Haka ma jihar Agadez bayan na isa masarautar na sanar da sultan zuwana
sai na wuce zuwa masaukina don hutawa saboda gajiyar hanya, bayan
kwana daya da zuwana,ina bacci da rana sultan ya aiko yana son za mu
gana ta hanyar Yariman Agadez Malam Ousseini dan Abbo, Sultan na
Agadez mutum ne mai cike da kwarjini da haiba ga izza wadda za ta nuna
maka shi cikakken sarki ne mai daraja ta farko, duk da cewa mu hudu ne
a fadar ta shi amma baya magana da ni kai tsaye hasalima bana jin abin
da yake fada sai idan ya yi magana a gaya min abin da ya ce, a haka
muka tattauna muhimman batutuwa, wani abin burgewa da wannan sarki shi
ne son jama'ar kasarsa da kyautata musu, mun yi tafiya da shi zuwa
dazuka (idan aka je daji a kasar Nijar ana nufin wasu garuruwa da suke
cikin duwatsu da sahara) don halartar taron addu'a na karshen shekara
da ake a kasar don neman zaman lafiya da wanzuwar arziki a kasar,
motarmu tana gaba ta sultan tana bayanmu sai muka wuce wasu mata da
kananan yara a hanya ga dukkan alamu wani garin da ke gaba da su za su
je, a cikin motarmu sai sakataren Malaman Jihar Agadez Malam Namadina
Alhaji Ousseini ya ce "Zai wahala Sultan bai tsaya yasa a dauko
mutanen nan ba", haka kuwa aka yi ba mu yi nisa ba sai muka ga ana
alamta mana cewa mu dakata, bayan mun tsaya muka dawo baya sai muka ga
Sultan ya sauko da kansa ya sanya an ba wadannan mutane mota guda
wadda ta dauke su tare da kayansu ta kai su garin da za su je.
Wannan abin ya matukar burgeni na kuma ji na kara kaunar wannan sarki.
A tsawon kwana uku da muka yi a dajin nan wallahi kusan ko yaushe duk
abin da aka kaiwa Sultan sai ya sanya an kawo mana da yake masaukanmu
suna dab da juna. Bayan an kammala wadannan addu'o'i ba fadarsa ya
dawo ba sai da ya wuce zuwa wasu garuruwa don ya gansu ya kuma
tattauna da su, bincikena ya gano cewa wannan sarki kusan koyaushe
yana cikin wadannan ayyuka na ziyarar mutanensa da kuma gabatar da
ayyukan da suka shafi ci gaban kasarsa duk da cewa akwai sarkin da aka
sanya don lura da wadannan garuruwa da ake kira A'ir mai suna Muhammad
Suleyman Anastafident, bayan mun dawo sarkin ya sake tambayata akwai
wani abu da nake bukata wanda ban samu ba? Na amsa da babu duk wani
aiki da ya kai ni na kammala shi har da ma ribar kafa.
A bangaren mutanen Agadez da Nijar kuwa babu wani abu da zan bayyana
su da shi sai dai na ce su mutane ne masu son jama'a da kuma girmama
baki da kaunar junansa, wani abu da ya sa nake kara yaba musu shi ne
yadda suka rike al'adunsu da kuma girmama tarihinsu.

A shekarar 2016 ma na ziyarci fadar sarkin Maradi tare da wani babban
dan kasuwa da ke Nijeriya don bude reshen harkar kasuwancinsa garin
Maradin babban abin da ya burge ni shi ne yadda mutanen fadar suka
karbe mu da karamci tare nuna jin dadinsu game da wannan abin alheri
da zai zo kasarsu, haka ma mahukunta jihar su ma sun nuna jin dadinsu
don har wakilin gunduma ya ba mu gayyata ta musamman zuwa gidansa amma
da yake muna sauri za mu wuce zuwa Niamey ne, ba mu samu zuwa ba, a
wannan bangare ma na yaba musu kwarai.

A saboda a haka a matsayina na Marubuci kuma Dan Jarida nake rokon duk
wani marubuci ko dan Jarida kai har ma da masu shirya fim su kasance
masu bibiyar tarihi da bincike tare da bibiyar masana kafin yin duk
wani aiki wanda zai shiga hannun jama'a saboda gudun irin abin da ya
faru a baya game da Fim din Dan Sarkin Agadez, da ma wasu daga cikin
rubuce-rubucenmu, Allah Ya jikan marigayi Gambu mijin Kulum mai wakar
barayi mun taba hadu da shi a jami'ar jihar Kaduna muna zantawa yake
nuna min rashin jin dadinsa da abin da wani marubuci yayi masa na
rashin adalci, ya ce marubucin ya rubuta karya game da shi da sunan
tarihinsa ba tare da kyakkyawan bincike ba.
Bana mantawa lokacin dana ziyarci wata fada a kasar Nijar din dai ta
sarki Ahmad Aghali Ibbah sarkin Tanhiya sun sanar da ni tarihinsu
tare da cewa duk abin da suka gaya min haka zan rubuta kar na rage kar
na kara, kun ga wannan ai shi ne adalci, wani abu da ya sake burgeni
da mutanen kasar shi ne lokacin da na je shan ruwa wajensu an samu
matsala, amma da na bayyana musu cewa ni bakon sarki ne sai suka kyale
ni na tafi abina.(Cikakken rahoton yana cikin labarin ziyararmu birnin
Tanhiya) A nan ma ya nuna cewa wannan sarki zaune yake da al'ummarsa
lafiya suna kaunarsa yana kaunarsu.
Da fatan wannan tsokaci zai sanya mu amfana wajen yin abin da zai zama
karbabbe a kan komai da za mu yi.

No comments:

Post a Comment