0
Conversations with Baba Conversations with Baba

By Jaafar Jaafar "Baba, let's go straight to the issues trending in the media. Nigerians are worried about your frequent junkets...

1
COUPLES AND MARRIAGE COUSELLING COUPLES AND MARRIAGE COUSELLING

FROM Rabiu Muhammad Abu Hidaya. *couples or marraige counselling is offered to support people in relationship who may be consedering seper...

0
ABU HIDAYA MARITAL COUNSELLINF ABU HIDAYA MARITAL COUNSELLINF

VISION: "To be the first, best, and formal marriage councilling and social relationship management center in the coutry" MISSI...

0
OVERVIEW OF IFRS OVERVIEW OF IFRS

An overview of IFRS Abstract International Financial Reporting Standards (IFRS)  shaped the  Accounting Framework in terms of measuremen...

0

Rigunan matan Hausawa? (1) Daga Malumfashi Ibrahim Ba ni da masaniya a kan batun da take son mu tattauna. Ta Intanet ta turo da baya...

0
TATTAUNAWA TA MUSAMMAN DA HAJIYA UMMA AMINU SANUSI (IYAN KANO) TATTAUNAWA TA MUSAMMAN DA HAJIYA UMMA AMINU SANUSI (IYAN KANO)

A ranar Juma'a ne 6\3\2015 Masarautar kano karkashin Mulkin Sarki Muhammadu Sanusi II ta yi nadin sarautar Iyan Kano wadda aka nada H...

0
TSAKURE DAGA CIKIN TAFIYA AGADEZ TSAKURE DAGA CIKIN TAFIYA AGADEZ

Tare da Abu Hidaya Bayan mun gama ganawa da gwamnan Aderbisanat sai kuma muka waiwayi inda motarmu take da zuwanmu muka tambaya an kamm...

0
AZANCI - 2 AZANCI - 2

AZANCI 2 Mataki na farko shine a gujewa tashin hankali. Kisa sai ta kama Allah shi ne kadai mai yankewa, shin ko ta wacce hanya c...

0
NADAMA NADAMA

Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya Na kasance yar gidan masu akwai domin mahaifina mutumne mai tarin dukiya na yi aure cikin jin dadi da walwa...

1
KIFI MUSULMIN NAMA KIFI MUSULMIN NAMA

Tattaunawa ta musamman da Masani kan kiwon Kifi a zamanance Malam Hassan Ibrahim game da yadda ake kiwon kifi da tanade-tanaden kalubalen da...

0
RIGAR ARO RIGAR ARO

LABARIN DAN JARIDA Bana mantawa da wata ranar lahadi ina wajen taro sai wayata ta fara kara cikin hanzari na sanya hannuna cikin aljihu na...

0
RAHMA SADAU BOM A INDUSTIRI RAHMA SADAU BOM A INDUSTIRI

Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya Kimanin watanni biyu kenan ana takaddamar rikicin dakatar da yar wasan Hausa jaruma Rahma sadau a masana&...

0
GANI GA WANE... GANI GA WANE...

KWANKWASO DA GANDUJE A SIYASAR KANO. Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya Yanzu dai ta tabbata Mataimakin Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar ...

Conversations with Baba

By Jaafar Jaafar
"Baba, let's go straight to the issues trending in the media. Nigerians are worried about your frequent junkets, saying there are important matters needing your attention at home."
"First of all, let me say that I was in Niger Republic to discuss with President 'Mohammed Yusif' issues of regional cooperation towards fighting insurgency. These ragtag criminals called Boko Haram will soon be eliminated. I was in Chad also, where I met with President Idris 'Baby' and discussed issues of regional alliance towards having a secure border and ending insurgency."
"But why don't you send your deputy to represent you, so that you can attend to important matters at home?"

COUPLES AND MARRIAGE COUSELLING

FROM Rabiu Muhammad Abu Hidaya.

*couples or marraige counselling is offered to support people in relationship who may be consedering seperation or seeking improved intimacy and understanding.

In couples counselling, the relationship is the focus although each partner should also expect to focus on self-improvement and self-awareness.

              When is it Recommended:
People in relationship seek counselling for any number of reasons, from pourer struggles and communication problem problems to sexual dissatisfaction and in fidelity.

Though counselling is recommended as soon as discontent arises in relationship studies show that on avarage partness will not seek theraphy untill they have been unhappy for six years and yet, the more time has passed, the more difficult it may be to repair the relationship.
In some cases, a couple who has already decided to seperate may persue theraphy in order to end the relationship amicably and respectfully.

Effective therapy will likely adress marry aspects of the relationship, although communication tends to be the primary focus of relationship therapy.

When partners repeatedly employ conflict avoidance or engage in heated pourer struggles, communication problem ensue, resentment bulds, and repair are never made.
   Counselors know that one of the first steps in inproving a relationship is to teach each person how to regulate their emotions, stay calm and use healthy communication skills to resolve problems new and old, and many partness see their communication improved as a result of counselling.

*EXPECTATION AND GOALS:-
Successful theraphy depends on each partner's motivation and dedication to the process, and couples can expect to become better listeness and communicators and to find new ways to support one another.
Goals will be established by the couple under the guidance of the therapist, and in order to achieve these objectives, each partner must be prepared to acknowledge and understand his or her role in the relationship.
It is not uncommon for comflict to arise within theraphy session, but ethical therapist will strive to remain neutral and avoid taking side.

(*Both couple have childrens from previous marraige, how would you advise them on how to stay together?.)

                           TERMS
*COMMUNICATION:- The imparting or interchange of thoughs, opinions or information by speech, writting, or signs.

*RELATIONSHIP:-A connection assocition or involvement.

*TIME:- The system of those sequential relations that any event has to any other as past, present, or future; indifinite and continous duration regarded as that in which events succed one another.

MISTAKE:- An error in action calculation, opinion,or judgment coursed by poor reasoning carelessnees insufficient knowledge, etc.

JAHILCI: daban yake da rashin ilimi) yana nufin fahimtar kuskure.

KARATU/ILIMI:-(Educated illitrate cannot read or write but do things morally, living a normal life with good norms and values.

Undeducated literate; can read and write but did not understand knowledge, nor do they live a good moral life blow std in norms and values etc, living irrationally.).

EDUCATION:- The act or process of impreting or acquiring particular knowledge or skills, as for a profession.

KNOWLEDGE:-acquaintance with facts truths, or principles, as from studies or investigation, general erudition: knowledge of many things.(erudition:knowledge acquired by study, reseach etc.)

PARENT:- A father or a mother/protector or guadian(to protect,parent children with both love and discipline.)COUPLES AND MARRAIGE COUSELLING.

*couples or marraige counselling is offered to support people in relationship who may be consedering seperation or seeking improved intimacy and understanding.

In couples counselling, the relationship is the focus although each partner should also expect to focus on self-improvement and self-awareness.

              When is it Recommended:
People in relationship seek counselling for any number of reasons, from pourer struggles and communication problem problems to sexual dissatisfaction and in fidelity.

Though counselling is recommended as soon as discontent arises in relationship studies show that on avarage partness will not seek theraphy untill they have been unhappy for six years and yet, the more time has passed, the more difficult it may be to repair the relationship.
In some cases, a couple who has already decided to seperate may persue theraphy in order to end the relationship amicably and respectfully.

Effective therapy will likely adress marry aspects of the relationship, although communication tends to be the primary focus of relationship therapy.

When partners repeatedly employ conflict avoidance or engage in heated pourer struggles, communication problem ensue, resentment bulds, and repair are never made.
   Counselors know that one of the first steps in inproving a relationship is to teach each person how to regulate their emotions, stay calm and use healthy communication skills to resolve problems new and old, and many partness see their communication improved as a result of counselling.

*EXPECTATION AND GOALS:-
Successful theraphy depends on each partner's motivation and dedication to the process, and couples can expect to become better listeness and communicators and to find new ways to support one another.
Goals will be established by the couple under the guidance of the therapist, and in order to achieve these objectives, each partner must be prepared to acknowledge and understand his or her role in the relationship.
It is not uncommon for comflict to arise within theraphy session, but ethical therapist will strive to remain neutral and avoid taking side.

(*Both couple have childrens from previous marraige, how would you advise them on how to stay together?.)

                           TERMS
*COMMUNICATION:- The imparting or interchange of thoughs, opinions or information by speech, writting, or signs.

*RELATIONSHIP:-A connection assocition or involvement.

*TIME:- The system of those sequential relations that any event has to any other as past, present, or future; indifinite and continous duration regarded as that in which events succed one another.

MISTAKE:- An error in action calculation, opinion,or judgment coursed by poor reasoning carelessnees insufficient knowledge, etc.

JAHILCI: daban yake da rashin ilimi) yana nufin fahimtar kuskure.

KARATU/ILIMI:-(Educated illitrate cannot read or write but do things morally, living a normal life with good norms and values.

Undeducated literate; can read and write but did not understand knowledge, nor do they live a good moral life blow std in norms and values etc, living irrationally.).

EDUCATION:- The act or process of impreting or acquiring particular knowledge or skills, as for a profession.

KNOWLEDGE:-acquaintance with facts truths, or principles, as from studies or investigation, general erudition: knowledge of many things.(erudition:knowledge acquired by study, reseach etc.)

PARENT:- A father or a mother/protector or guadian(to protect,parent children with both love and discipline.)

ABU HIDAYA MARITAL COUNSELLINF

VISION: "To be the first, best, and formal marriage councilling and social relationship management center in the coutry"

MISSION
STATEMENT: "To contribute possitively in maintaining a healthy and strong marriage life and ensure that childrens enjoy the right of growing through a normal family circle, which will help them to contribute to the development of the society"

OVERVIEW OF IFRS

An overview of IFRS


Abstract
International Financial Reporting Standards (IFRS)  shaped the  Accounting Framework in terms of measurement, recognition, presentation and revelation transactional requirement as well as articles reflected in the financial statements. It employs a uniform, single consistent accounting framework that is gravitating towards General Accepted Accounting Practice (GAPP) in the future.
Rigunan matan Hausawa? (1)
Daga
Malumfashi Ibrahim
Ba ni da masaniya a kan batun da take son mu tattauna. Ta Intanet ta turo da bayanan da take son mu yi magana kan su, sa’annan ta nemi na sanar da ita me ya sa matan Hausawa rigunan da suke sanyawa ba su da yawa ko kuma suke sanya rigunan ba daidai ba. Ta kuma nemi da na kara mata haske game da yadda matan Hausawan za su iya bin matakin ganin sun sa rigunan nan kamar sauran matan duniya.

TATTAUNAWA TA MUSAMMAN DA HAJIYA UMMA AMINU SANUSI (IYAN KANO)

A ranar Juma'a ne 6\3\2015 Masarautar kano karkashin Mulkin Sarki Muhammadu Sanusi II ta yi nadin sarautar Iyan Kano wadda aka nada Hajiya Umma Aminu Sanusi a wannan matsayi, Ni Rabiu Muhammad Abu Hidaya na samu tattauna da ita a gidan Sarki na Gandun Albasa game da takaitaccen tarihinta da kuma asalin wannan sarauta ta Iya da aka yi mata kuma ta gaya mi ni har da ayyukan da wannan sarauta za ta yi a masarautar kano, a sha karatu.

TSAKURE DAGA CIKIN TAFIYA AGADEZ

Tare da Abu Hidaya
Bayan mun gama ganawa da gwamnan Aderbisanat sai kuma muka waiwayi inda motarmu take da zuwanmu muka tambaya an kammala komai aka tabbatar mana da cewa komi ya kammala,
daga nan muka azawa mota giya muka yiwa garin Tanout tsinke da nufin idan mun je mu tsaya mu kwana a can da safe mu wuce Damagaram.

AZANCI - 2

AZANCI 2
Mataki na farko shine a gujewa tashin hankali.
Kisa sai ta kama
Allah shi ne kadai mai yankewa,
shin ko ta wacce hanya ce zai dauki raina.
A yanzu na lura babu wani dalili da zai sa mu zama kausasa.
Sam babu dabara cikin nacewa abinda bashi da amfani.
Suna kashe danginsu akan tabbatuwar mulkinsu.
Ni kuma zan bada nawa ran akan ko wani nawa.

NADAMA

Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya

Na kasance yar gidan masu akwai domin mahaifina mutumne mai tarin dukiya na yi aure cikin jin dadi da walwala duk da cewa bani kadai ba ce a gidan mijina akwai kishiyata amma kuma na fita fada a gunsa domin sai abinda na ce ganin bana rabo da yan silalla a tare dani kuma ana yawan aiko min da kayan alatu daga gidanmu.

Duk da cewa bani bace uwargida amma sai mijina ya mai dani uwargidan sai abinda na ce.

Duk duniya ba abinda na tsana irin kishiya na tsani koda jin labarinta sai gashi wai ni ce a gidan kishiya in banda kaddara.

Wannan damar dana samu a gurin mijina sai na yi amfani da ita wajen musguna mata ita da yaranta.

Ya'yan kishiyata uku biyu mata daya Namiji.

Ni kuwa ina da yara biyu duk maza
wannan ne dalilin da me gidana ya kara sona ganin daga zuwa na haifa masa yara biyu duk maza.

Na lura wannan al'amari ba karamin batawa kishiyata rai yake ba kawai sharewa take ni kuwa dana ga haka sai na shiga sabon salon kara kunsa mata bakin ciki domin kusan kullum sai na canja sabbin kaya kuma yawanci shi nake baiwa dinki ya kai min haka nan duk ranar da aka ce girki na ne sai in sa ya yo min cafane mai kyan gaske mu ci ni da yayana.

Haka kawai sai in kirkiri sharri in yi mata a gun mijinmu shi kuma ya yi ta mata masifu kala-kala har da barazanar saki, kullum ta Allah kafin in gaisheta ta gaishe ni.

Duk wani hakki da aka ce nawa ne kishiyata ta biya min kai hatta duk haihuwar dana yi kusan ita ke dawainiya da ni amma wannan bai sa na ji ina tausayinta ba kullum dada gallaza musu nake ita da ya'yanta.

Ana tsaka da wannan al'amari sai ciwo ya kamata wai ciwon zuciya da hawan jini an je asibiti sai aka ga ashe har zuciyarta ta kumbura kafin wani kwakkwaran mataki tace ga garinku nan.

Bayan rasuwarta da kamar wata biyu sai rikon yaranta ya dawo hannuna.

Ganin wannan damar ta dawo hannuna sai tsanar uwar yaran ta dawo kansu.
Na shiga gallaza musu ba dare ba rana kusan kullum sai na zane su haka kuma idan na ba 'ya'yana abinci da yawa su sai in basu kadan
kasancewar yaran suna zuwa makaranta sai Allah ya basu Nasibin haddace duk abinda aka koya musu kullum naga yaran nan sai in ji tsanar su ta kara kamani kai da abin ya ishe ni rana daya na fito na gayawa mijina cewa ni gaskiya ba zan iya zama da su ba dan haka yasan yadda zai yi dasu kasancewar babu yadda ya iya dani haka ya kwashi yaran ya mai da su can kauyensu wajen danginsa.

Wata rana na kwanta sai na yi mafarki wai gani na mutu an sanya ni a wuta ana ta yi min azaba kala-kala sakamakon tozarta kishiyata dana yi da kuma rukon sakainar kashin dana yiwa marayu.

Wannan mafarki ba karamin tsorata ni ya yi ba.
Kusan kullum cikin tunani nake wallahi abin ya tsaya min a rai.

Dan haka na rubuto muku wannan labarin nawa Aunty Lami ku bani shawara dan Allah ya zan yi?

KIFI MUSULMIN NAMA

Tattaunawa ta musamman da Masani kan kiwon Kifi a zamanance Malam Hassan Ibrahim game da yadda ake kiwon kifi da tanade-tanaden kalubalen da ke cikin harkar.

Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya

Da farko za mu so mu ji takaitaccen tarihinka?

Malam Hassan: to assalamu alaikum jama'a, da farko dai sunana Hassan Ibrahim na yi karatuna na fimare a magwan Firamare daga nan na wuce sakandiren GSSS Kawaji amma a Kwalejin Rumfa  na karasa sakandirena bayan nan kuma sai na shiga makarantar koyon aikin noma ta Audu Bako da ke Dambatta a kano bayan na kammala sai na wuce A.B.U Zariya na yi karatun babbar Difiloma akan aikin Noma(HND) sai kuma na shiga aiki koyarwa a sakandiren Maza ta Kimiyya da fasaha da ke Lauta a Gumel jihar Jigawa, ban jima ina koyarwa ba sai na bar su na dawo kwalejin Ilimi ta tarayya (F.C.E) kano wanda a yanzu haka a nan nake aiki.

Kamar in na fahimceka da kyau a cikin ilimin da kai kafi kwarewa akan abinda ya shafi noma da kiwo a zamanance haka ne ko?

Malam Hassan: haka ne.

Yauwa abinda na ke so mu yi magana a kai shi ne harkar kifi da kiwonsa a zamanance,(Fisheries) idan mutum yana so ya fara sana'ar kifi wasu abubuwa ne yakamata ya tanada don fuskantar harkar?

Malam Hassan: to da farko idan mutum zai fara sana'ar kiwon kifi ko nomansa yana da kyau a fara samun filin(Land) da zai yi wannan harka domin wannan fili shi ne mafi muhimmanci a ko wani sha'ani na harkar noma walau na kifi ko na noman iri, bayan samun filin sai kuma jari(Capital) da ma'aikatan gudanarwa(Labour) to shi wannan fili da za'a yi kiwon kifin ya kasu kashi uku  kamar haka:

1-Concrete Font(Dan karamin kududdufin da za'a gina da bulo)
2-Azalt font(ramin kasa wanda ba'a zuba siminti a ciki ba) a kuma tabbatar kasar ba mai tsotse ruwa ba ce dan kada a wahalar da kifayen
3-Plastic font(Tanki na musamman domin kiwon kifi)

akwai kuma wuraren kiwon kifi na musamman (Captured areas) shi kuma yawanci gwamnati ke hurumin yin wannan kiwon shine manya koguna da kududdufai.

Manona: duk wannan jawaban da ka yi sai na lura kamar na masu karfi ne shin idan talaka wanda bai da ikon bin wadancan hanyoyi da ka fada ya zai yi a bashi masu sauki?

Malam Hassan: na'am! To ga mai karamin karfi zai iya fara kiwon kifinsa ko a gida amma ya tabbatar da cewa akwai wadataccen ruwa a gidan saboda shi kiwon kifi sai da ruwa domin kifin yana son canjin ruwa akai-akai a kalla duk kwana biyu ko uku a canja masa ruwa ya danganta da kyan ruwan da kuma yawan kifayen, idan suna da yawa za su dinga kashi a ruwan ka ga zai dinga sauri baci kenan.

Manona: ga mai fara yin wannan sana'a shin akwai wata ka'ida da zai bi domin fara wannan sana'a?

Malam Hassan: to ga mai fara wannan sana'a zai iya farawa da kifaye 50 ko 100 ba'a son mutum idan bai kware ba ya kwaso su da yawa, to in sha Allah idan ya fara da wadannan ya kuma kiyaye canja musu ruwa da kuma basu abinci akan kari zai ji dadin kiwon na su.

Manoma: da wani yakamata a dinga ba su abinci?

Malam Hassan: sau biyu a rana ko sau uku da safe da rana da kuma yamma, amma dai kifi an fi so a bashi abinci da sanyin safiya da kuma la'asar irin rana ta yi sanyi sosai.
Sannan wajen canja masa ruwa ba'a son lokaci guda a canja masa ruwa wannan yana illatar da kifi sosai, ana so a lokacin da ake zubar da tsohon ruwan a dinga zuba sabo, saboda canjin yanayi(Tamparature) na kifin, ba'a son sai an zubar da tsohon tsaf sannan a zuba sabo, ba mamaki tsohon ruwan ya fi sabon dumi dan haka ake so a lokacin da ake zubar da tsohon a dinga zuba sabon dan ya saje da yanayin da kifin ke ciki.

Manoma: akwai wata illa ne a tare da canja ruwan lokaci guda?

Malam salisu: kwarai kuwa akwai illa kasan shi kifi yanayinsa yana canjawa da ruwan daya tsinci kansa a ciki(Cold Blood Animal) idan ruwa mai zafi ne yanayin jikinsa yana komawa mai sanyi hakama idan mai zafi ne yanayinsa yakan koma mai zafi, dan haka ba'a son lokaci guda a sauya masa ruwa, sai dai a hankali a hankali.

Manoma: ta ya ya za'a iya canja ruwan kifin ba tare da an zubar da tsohon ba?

Malam Hassan:(dariya) ai duk wanda zai fara wannan sana'a akwai dan tanki da aka tanada domin fara wannan sana'a shi kuma wannan tanki a jikinsa akwai hanyoyin fitar da ruwa da kuma shigarsa(Outlet da Inlet).

Manoma: ga wanda zai fara wannan sana'a shin akwai wasu nau'in kifiye da ake so ya fara da su?

Malam Hassan:eh akwai amma ba su wuce kala biyu ba, akwai MARI akwai kuma TARWADA kusan danginsu daya (Family) amma akwai dan bambanci ita Mari ta fi Tarwada girma domin tana girma sosai domin idan ta girma zata iya kaiwa kamar cinyar mutum, ita ma Tarwada tana girma amma dai bata kai Mari ba, to wadannan sune nau'ikan kifayen da ake so mutum ya kiwata domin suna da juriya da saurin girma da kuma riba.

Manoma: akwai nau'ikan kifaye da yawa a duniya shin ko za mu yi sanin hakikanin yawansu a duniya da kuma dalilin da yasa aka zabi wadannan jinsi biyu domin kiwonsu?

Malam Hassan: to a lal hakika kifayen da suke duniya suna da yawa, ka ga ana samu a koguna ana samu fadamu ana samu a rafi da kududdufai da kuma teku. Duka wadannan abubuwan dana lissafa maka a kwai nau'ikan kifayen da ake samu a kowannensu, a kalla kifayen da mu ke da su a duniya wadanda kididdiga ta ba mu damar sani sun kai kimanin 600 amma shahararru wadanda aka fi sani a kasar hausa akwai:
Tarwada.
Karfasa.
Mari.
Qawara, da sauransu.

Manona: bari mu dan dawo baya kadan shin akwai wasu kwanaki da aka ware wadanda za'a soma kiwata kifayen da kuma adadin kwanakin da za'a fitar dasu a siyar a kasuwa?

Malam Hassan: eh to yawanci an fi so idan za'a soma kiwon kifin a soma da wanda tsayinsa bai wuce girman dan yatsa ba(Finger ling) ko kuma (Post Finger ling) su kuma sun fi na farko girma akwai kuma Jumbo shi Jumbo babba ne sosai ya dai danganta da karfi da mutum ke dashi amma dai yawanci an fi so a zuba (Finger ling ko Juba nil) domin su sun yi dan kwari ba za'a yi asarar sosai ba, amma in suka cika kankanta to wajen rainon nasu wasu za su mutu da yawa to idan aka zuba wadannan kifaye daga ranar da aka zuba su idan akwai kulawa ta sosai wata biyar zuwa shida sun isa a kwashe su a siyar ko a ci.

Manoma: akwai wasu magunguna da ake son a dinga basu ko kuma wata ka'ida da za'a bi don ingantuwar kiwonsu?

Malam Hassan: to shi dai kifi bai da wata matsala a kiwonsa sosai matukar an bi wadancan ka'idojin dana fada a baya na canja masa ruwa da bashi abinci akan ka'ida shi kiwon ba kamar na kaji bane bai da wasu cututtuka da yawa, amma ana so idan an zuba ruwan akwai wani magani na (anti biotic)da ake zubawa a ruwan wanda ko akwai wasu kwayoyin cututtuka shi wannan(anti biotic) zai kashe su haka kuma ko da wasu daga cikin kifayen wasu sun kamu za su warke.
Akwai kuma wani maganin da ake kira(booster) shi kuma ana zuba musu a cikin abincinsu a basu yana taimaka musu wajen saurin girma.

Manoma: Mun Gode.

Malam Hassan: Ni ma na gode.

RIGAR ARO

LABARIN DAN JARIDA

Bana mantawa da wata ranar lahadi ina wajen taro sai wayata ta fara kara cikin hanzari na sanya hannuna cikin aljihu na dauko wayar, lambar ba suna.

A kunnena na kara tare da fadin hello muryar mace naji bayan mun gaisa sai take bayyana min wai mai bibiyar shafina ce a jaridar da nake rubutu tana min fatan alkhairi da kuma jinjina game da yadda nake fadar gaskiya a rubutuna, na mata godiya tare da tambayar sunanta? ta fada min sunanta Aisha muka yi sallama na mayar da wayata aljihu. Na cigaba da sabgata ba tare da tunanin komai ba domin kusan kullum sai na karbi waya makamanciyar wannan daga masoyana ma'abota karanta shafina a jarida.

Washe gari da safe ina shirin tafiya ofis sai ta sake kirana muka gaisa kamar jiya, amma wannan karon yanayin maganar ya dan tsawaita domin har tambayoyi tayi min.

Tun daga wannan rana kusan kullum sai mun yi waya da Aisha.

Gaskiya yarinyar tana da hankali da kuma iya magana wannan ne dalilin daya sa nake bata lokacina idan ta kira, a hankali har takai nima ina kiranta mu dade muna hira.

So shu'umi kwanci tashi kwana nesa sai soyayya mai karfi ta kullu tsakaninmu da Aisha a kalla yau mun shafe kimanin wata biyar muna soyayya, amma tsawon wannan lokaci ban taba zuwa gidansu ba kasancewar muna da yar tazara tsakaninmu tana kaduna ni ina kano.

Mun shaku kwarai da juna kuma muna tsananin son juna idan bama waya to zaka samu daya yana rubutawa daya sakon text a waya, a wannan halin Aisha zata min cake ko wani abinci ta je tasha ta baiwa direban da zai zo kano ya kawo min.

Watarana wani babban aminina zai tafi kaduna sai na bashi adireshin gidansu ya je su gaisa, daga nan ni kuma sai na gaya mata ga wani abokina nan zai zo gurinta su gaisa in zai yi yu ina so ta bashi hotonta ya taho min dashi? Ta ce ba damuwa.

Bayan kwana biyu sai abokina ya kawo min hotunanta, gaskiyar magana a lokacin dana ga hotunan bata yi min ba, amma sai na tuna ai ita bata ganni ba amma ta sadaukar da lokacinta gareni dan haka sai tausayi ya yi aiki na samawa sonta gurbi na dindin ta karfi da yaji a zuciyata, a haka muka cigaba da gudanar da soyayyarmu mai armashi da juna.

Duk da cewa ban taba zuwa gidansu amma na san kusan kowa a danginta domin takan bani labarin wasu wasu kuma takan hada mu a waya mu gaisa, kamar Mahaifiyarta da kanenta.

Ana tsaka da wannan sha'ani ina ta shirya-shiryen zuwa garinsu Aisha katsam sai ta kirani a waya tace kada nazo na bari zata zo ranar Juma'a hakan kuwa aka yi na zauna cikin jiran tsammanin ranar da zata zo.

Ranar juma'a da yamma sai ga Aisha a garin kano sai dai ranar an samu akasi a lokacin aikin ya yi min yawa bamu samu haduwa ba amma abokina shi ya kaita gidan data sauka.

Bamu hadu da Aisha ba sai washe gari Asabar a ranar da idanuna suka yi tozali da ita sai na ji sabon sonta ya sake shiga raina, ranar kamar mu hadiye juna tsabar saukin juna mun tattauna sosai game da yadda rayuwarmu zata kasance bayan aure da kuma irin tanadin da zamu yiwa rayuwar ya'yanmu.

Washe gari lahadi da sassafe Aisha ta koma garinsu tunda Aisha ta tafi sai naji kamar ta tafi da wani bangare na jikina.

Tafiyarta tazo da wani bakon al'amari domin tunda Aisha ta koma gida sai ta dena daga min waya sai in kirata wajen sau ishirin amma da kyar zata daga sau daya idan na samu ta daga sai tace min wai ina karar mata da chaji.

Wannan abin ba karamin daure min kai ya yi ba.

Idan na mata text message sam bata bani amsa, da tsanani ya kai tsanani sai na shirya na tafi gidansu na samu na ganta na kuma nemi ta sanar dani laifin da na yi mata sai tace ban mata laifin komai ba kawai dai ita maganar soyayya ni da ita yanzu babu.

RAHMA SADAU BOM A INDUSTIRI


Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya

Kimanin watanni biyu kenan ana takaddamar rikicin dakatar da yar wasan Hausa jaruma Rahma sadau a masana'antar shirya fina-finai ta Kannywood wadda ta samo asali daga lafazin da Rahman ta yi na cewa wai Adam Zango  ya neme ta da fasikanci ita kuma taki sakamakon haka shi kuma ya cire ta daga fim dinsa da suke dauka tare, sai dai kuma bayan wani dan bincike na wucin gadi da wani kwamiti ya yi wai ya gano cewa karya Rahma take  yi wa Adamu don haka kwamitin karkashin Kungiyar MOPPAN ya dakatar da ita.
Sai  dai kuma wani abin lura a nan shi ne anya wannan kwamiti ko wannan kungiya sun yi zuzzurfan tunani kafin su dakatar da Rahma din kuwa?
Lalle idan mu ka yi duba da yadda masana'antar take ciki a halin yanzu za mu iya cewa ba wannan ne hukuncin da kungiyar yakamata a ce ta yankewa jarumar ba, duba da cewa akwai dokoki da yawa wadanda za a iya amfani da su wajen yi mata hukunci don ladabtarwa irin su. tara, gargadi ko jan kunne.
Sannan za mu yi cewa wajen yanke hukuncin an yi tuya an manta da albasa dalili kuwa shi ne kamata ya yi idan za a dakatar ita Rahma din a dakatar da ita tare da Adamun ko yaronsa mai suna Ali Atwork wanda shi ma ya shiga rigimar inda ya ciwa Jarumar mutunci amma sai ba a yi haka ba, aka yankewa Rahma hukunci ita daya, wani karin abin mamaki ga wannan kwamiti shi ne wasu masu ruwa da tsaki a harkar ta shirin Fim kuma shugabanni irin shugaban kungiyar Arewa Fim makers Baba Karami sun nuna  damuwarsu a kan yadda aka dakatar jarumar ba tare da saninsu ba, a saboda haka ne suke cewa su bada yawunsu aka yanke wannan hukunci ba don haka su a gurinsu Rahma ba dakatacciya ba ce.
Har ila yau wasu daga cikin Daraktoci sun yi kunnen uwar shegu da wannan hukunci domin sun ci gaba da saka wannan jaruma a fina-finansu wanda ake ganin mai gidanta a harkar wato Ali Nuhu shi ne ya soma karya wannan doka da aka sanya ta hana sanya jarumar a fim har tsawon wata shida bisa dalilinsa na cewa ya riga ya aika da takarda ga waccan kwamiti don bashi damar karasa fim din da suka fara dauka da ita.
Mahangar Arewa ta hanga ta hango cewa matukar masana'antar ta Kannywood idan bata yi taka tsan-tsan ba lalle wannan rikici zai iya haifar musu da marar idanu da gagarumin koma baya a harkar musamman yadda kawunansu ya rabu a wannan hukunci da aka yanke, domin wasu na ganin cewa shin Rahman ce kadai me laifi za a yankewa hukunci? Ai akwai jarumai irinta da suka aikata laifi kamar Fati Shu'uma, Ali Nuhu, Artwork da kuma shi Adamun, don haka matukar ana so a yi hukuncin da kowa zai ji an so a kamanta to tilas a koma baya don warware lauje cikin nadi,
har ila yau wasu na ganin Hukumar tace Fina-finai da Dabi'i ta jihar Kano karkashin Dahiru Ahmad Beli ta taka muhimmiyar rawa wajen sake kunna wutar gaba a tsakanin yan fim din ya yin da ta goyi bayan kungiya daya ta kuma kwayewa daya zane ta hanyar tabbatar da hukuncin da waccan kwamiti yayi na dakatar da jarumar wanda shi kuma daya bangaren na AFMAN da sauran daraktoci suke ganin sam hukumar bata yi abin da ya dace ba kasancewarta hukumar da suke bai wa girma don haka kamata ya yi idan har za a yanke irin wannan hukunci to a dinga tuntubarsu ba a dinga yanke hukunci ba da saninsu ba, wannan tamkar mulkin mallaka ne wanda kuma su ba za su taba yarda da hakan ba.

To yanzu dai ta tabbata hukumar tace Fina-finai da Dabi'i tare da Kungiyar MOPPAN karkashin jagorancin Isma'ila Na'abba Afakallah suna nan a kan bakansu na sai jaruma Rahma Sadau ta yi wata shida sannan za a ci gaba da ganinta a fina-finai kuma yanzu muna iya cewa ta ci wata biyu saura hudu, yayinda kuma a gefe daya kungiyar AFMAN karkashin jagorancin Baba Karami da wasu daraktoci suke ganin wannan hukunci da waccan kwamiti da hukumar tamkar wasan yara ne.
To ko ya lamarin zai kare mu je zuwa "Wai mahaukaci ya hau kura".

GANI GA WANE...


KWANKWASO DA GANDUJE A SIYASAR KANO.

Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya

Yanzu dai ta tabbata Mataimakin Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje shi ne zababben gwamnan jihar kano bayan kammala zaben bana na shekarar 2015 kafin wannan zabe mutane da yawa suna ganin anya Gwamna Injiniya Rabiu Musa kwankwaso zai yarda maitamakinsa ya gaje shi a kujerar da zai bari ta gwamnan jihar kano?

Duba da irin kalaman da ya rika yi a wajen tarurruka in da yake cewa da Ganduje suka zo da shi za su koma, wadannan kalamai nasa sun sake bai wa zawaran kujerar irinsu Honarabil Abdurrahman Kawu Sumaila da Janar mai ritaya Lawal Jafar Isa damar fitowa bilhakki su nemi kujerar wala Allah ko za su samu damar samun tikitin zama halattatun 'yan takarar da jam'iyya za ta sanya a gaba don haye buzun gwamna mai bari gado.

Sai dai kuma daga baya gwamnan ya yi a mai ya lashe ya yin da rana tsaka ya bayyana yardarsa a kan mataimakin nasa Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya maye gurbinsa a gidan gwamnatin jihar kano.

Wasu masana siyasa na ganin gwamnan ya yi hakan ne ba da son ransa ba, sai don kawai tsira da mutunci bisa la'akari da yanayin siyasar Kano cewa siyasar zabi sonka ake.
Wani nazarin kuma na ganin kila gwamnan ya dauki darasi ne daga mulkin gwamnatin daya gada a  hannun malam Ibrahim Shekarau wanda ya bai wa dukkan kwamishinoninsa dama suka ci suka tada kai har ta kai suna jin suma karansu ya kai tsaikon da za su fito su mulki jihar kano a ya yin karewar wa'adin mulkin Malam Ibrahim Shekarau, hakan kuwa a ka yi mutane irinsu Sani Lawan Kofar Mata da Malam Ibrahim Kankarofi da Malam Ibrahim Khalil da kuma Mataimakin gwamna shekarau din wato Dakta Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo suka fito cikin shiri da neman jam'iyya ta tsayar da su takarar neman kujerar gwamna a 2011 a ya yin da kowannensu yake ganin idan ba shi jam'iyya ta tsayar ba to ba wanda ya dace da gurin, ana tsaka da wannan dambarwa sai malam Ibrahim shekarau ya dauko kwamishinsa na kananan hukumomi wato Malam Salihu Sagir Takai ya nuna a matsayin magajin da zai gaje shi a mulkin jihar Kano. Wannan al'amari ba karamin batawa wadancan yan takara rai ya yi ba, in da hakan tasa har wasu suka kasa jurewa suka yi canjin sheka daga Jam'iyyar ANPP zuwa wasu jam'iyyun cikin, wadanda suka sauya jam'iyya akwai matakin gwamnan Dakta Abdullahi T Gwarzo wanda ya sauya sheka zuwa jam'iyyar ACN kuma ka bashi takarar gwamna a karkashin jam'iyyar, sai kuma Sani Lawan Kofar Mata shi ma daya sauya sheka zuwa jam'iyyar adawa ta PDP ya marawa Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso baya ya yin da wasu kuma suka tsaya a jam'iyyar ta su ta ANPP amma suka yi mata zagon kasa a zaben na 2011 da a ka yi suka kayar da ita.

Masana siyasa na ganin wadannan dalilai da ma wasun su suka sanya kwankwaso ya sahalewa mataimakinsa Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya zama magajinsa a gidan gwamnatin jihar kano.

Har ila yau tarihin siyasar kano ya nuna ba a yi wa kanawa karfa-karfa kusan idan muka koma tarihi za mu gane haka tun zamanin su Malam Aminu Kano da jam'iyyun siyasa irin su PRP da NPP da kuma NPN in da aka yi siyasar 1979 tsakanin Marigayi Muhammad Abubakar Rimi da Aminu Wali a lokacin Aminu Wali a jirgi yake kamfen amma talakawa suka nuna Rimi suke so kuma shi suka zaba, a 1983 sai kuma mutanen kano suka juyawa Rimin baya  duk da cewa shi ke da mulki a hannunsa kuma Jam'iyyarsa ta NPN ita ake ya yi suka zabi Sabo Bakin Zuwo a matsayin gwamnan kano a jam'iyyar PRP.
Haka in zamu iya tunawa a shekarar 1999 kwankwaso ya zama dan takarar gwamna a ya yin da suka yi takarar fidda gwani shi da Dakta Abdullahi Umar ganduje ba don ya fi ganduje komi ba.

Hakan ya ci gaba da faruwa a 2003 in da Shekarau ya fito neman kujerar gwamnan kanon a jam'iyyar ANPP wanda Buhari yake jagoranta ba tare da kudi ko shahara a siyasa ba, amma kanawa suka yarje masa ya zama gwamnan kano, sannan a 2007 ma sun sake ba shi irin waccan damar ya yin da aka yi ta camfin wai ba a mulkin kano sai biyu. Watakila wannan damar da Shekarau ya samu ce ta sa shi rafkanuwa a siyasarsa in da yake ganin kamar duk abin da ya ce da kanawa su yi za su yi masa ya sa ya tsayar da Malam Salihu Sagir Takai a 2011 ba don suna so ba, in da su kuma suka nuna masa cewa kada fa ya manta kano siyasar yanci ake ba mamure ba. Suka bijirewa zabinsa suka zabi Kwankwaso da Ganduje a karo na biyu don sake mulkar jihar.

Ba nan gizo ke sakar ba har ila yau wasu na kallon cewa firgicin siyasa ne ya sanya Kwankwason ya bai wa matamakinsa takarar gwamna a jihar. Babu shakka alamu sun nuna cewa Ganduje ya gina siyasarsa a kano tun sassafe a lokacin da hankalin Kwankwason ya ta fi izuwa takarar shugabacin kasa. Sai shi kuma ya siye duka kananan hukumomin jihar, dama kuma mafiya yawa daga cikin su yaransa ne, sannan kuma kaso mai yawa daga cikin ma'aikatan jihar kanon Gandujen suke so a matsayin wanda zai gaji Kwankwason ya yin barin gadon mulkin kano. Kalaman siyasa sun ci gaba da zagayawa a bakin mutane in da kalmar nan ta daga LIMAN sai NA'IBI ta karade ko ina a jahar kano, ya yin da masana siyasa suke kallon matukar Kwankwason ya nuna wani ba Ganduje ba to hakan na iya sawa mataimakin nasa ya bar jam'iyyar abin da kuma zai haifar da irin wautar da ta faru da gwamnatin baya faruwar hakan kuma watakila ya ba jam'iyyar adawa dama su samu mulki cikin sauki don haka hanya daya ce mafita ita ce Kwankwanso ya marawa Ganduje baya domin ya gaji buzunsa, haka kuma kalaman wasu daga cikin zawaran kujerar gwamnan sun nuna in dai Kwankwaso ya nuna Ganduje a matsayin wanda zai gaje shi to za su hakura su bi shi, idan kuma har ya nuna wani ba shi ba to lalle sai sun ga abin da ya turewa buzu nadi. A irin wannan turnukun siyasar ne wasu 'yan mu gani mu fada suke cewa kwankwason bisa tilas ya tsayar da Ganduje a kujerar gwamnan jihar don gudun ta bare, domin ba ya son Gandujen ya zama gwamna a Kano tunda a shekarar 2007 da aka haramta masa tsayawa takara me yasa bai dauko Gandujen ya tsaya takara ba?

Duk da haka kwankwaso ya nuna dalilin da ya sanya ya nuna goyon bayansa kan takarar mataimakinsa  Dakta Abdullahi Umar Ganduje, in da yake cewa Gandujen ne ya dace da kujerar gwamnan jihar a 2015 domin da shi a ka yi wa jihar ayyakun da mutanen kano suke gani a yau, kuma ya ce tun da har mataimakin nasa ya nuna yana son gadar buzun da zai bari to wajibinsa ne ya goya masa baya domin shi ne lamba 2 a jihar kuma ya tabbata zai karasawa jihar ayyukan alherin da suka dauko da ma wasu karin ayyukan.

To komai da mene ne Kwankwaso ya kafa tarihi a siyasar Nijeriya don shi ne gwamna na biyu da ya amincewa mataimakinsa ya gaje shi idan ya bar mulki a ya yin da tsohon gwamnan Zamfara kuma sanata a yanzu Ahmad Sani Yariman Bakura ya zama gwamna na farko da ya bai wa mataimakinsa dama ya gaje shi wato Mamuda Ali Shinkafi shi kuma ya tafi sanata amma kuma a karshe ya butulce masa.
To ko ya zata kasance a jihar kano?
Yanzu dai Ganduje ya zama Gwamna Kwankwaso kuma ya zama Sanata Allah yasa kada tarihi ya maimata kansa.