0
Daga 

Mahangar Arewa: da farko za mu so mu ji takaitaccen tarihinka.

Aminu Ala: To da farko sunana Aminudden Ladan Abubukar wanda aka fi sani da Alan waka,

an haife ni a shekarar 1974 a unguwar Yakasai cikin birnin kano.

Na yi karatun zamani dana Addini dai-dai gwargwado.

Na yi karatun firamare a tudun Murtala primary school daga 1980 zuwa 1986 daga nan na wuce makarantar sakandire ta Dakata kawaji daga 1986-1992 daga nan kuma sai na samu tsaiko ban cigaba da karatuna ba sai na shiga harkar rubutun kirkira wanda daga baya kuma na shiga harkar waka ka'in da na'in inda har takai ina da kamfanin Waka mai suna Taskar Ala global.

Mahangar Arewa: A da mutane a fagen rubutu suka sanka ya aka yi ka koma harkar waka?

Aminu Ala: To gaskiyar magana waka dai ita na soma domin tun dan ina Islamiyya nake waka a wurin Maulidi amma wakar bata shiga cikin al'umma ba sai a shekarar 2003 ta kafar sadarwar gidan rediyon kano,

amma shi rubutu na fara shine a shekarar 1992 kuma bai fara fita ba sai 1999 wannan duk lamari ne na ubangiji ina waka ina rubutun littafi duk harka ce ta kirkira.

Mahangar Arewa: Matsayinka na cikakken mawaki a yau, me ya ja hankalinka ka shiga harkar ka'in da na'in?

Aminu Ala: to kamar yadda na fada maka waka na fara yin ta tun ina islamiyya inda ake koya mana karatu da wake da kuma wakokin yabon manzon Allah (S.A.W) don nuni da daraja da martabarsa, to daga haka muka fara rubuta waka har ma na rubuta wata waka mai suna raina fansa ne ga Annabi Babba dan Babba da kuma wata wakar mai suna Mai duka sa in je madina wadannan duk mu yi su ne a lokacin mauludi akan manbari kuma ni mai yawan sauraren wakoki ne tun da, ka ji dalilin da yasa na tsinci kaina a harkar waka.

Mahangar Arewa: In dai ana magana akan fitattun mawakan Hausa wadanda suka shahara dole sai an lissafa da kai, shin me kake ganin ya jawo maka wannan daukaka?

ALA: To wannan daga Allah ne, haka Allah yake ikonsa kuma babu mai hana shi idan yaso abu haka jama'a za su karbe shi, sannan kuma ina yin wakokin da suka shafi al'umma da fadakarwa akan siyasa da zamatakewa wanda in ka dauke masu wakokin madahu mafi yawa daga cikin mawakan yanzu sun fi yin wakokin soyayya da kuma na fina-finai, wannan shi yasa mutane suka fi karkata bangarenmu.

Mahangar Arewa: Yawanci wakokinka sun fi karkata ga sarakuna da wakokin fadakarwa, me yasa baka fiya wakokin siyasa ba?

ALA: To na lura wakokin siyasa suna jogarantarmu ga zubar da mutunci, baka samun komai a ciki sai ka taba mutuncin wani ko wani yasa kaci mutuncin wani ka kaskantar dashi sannan a baka wani abu wanda kuma gobe kana iya ganinsu tare, kuma ita waka ta riga ta shiga cikin kundin tarihi ka riga ka yi ta, waka tana da hadarin gaske shi yasa ko lokacin dana yi wakokin siyasa bana yin zagi na kan yi kokari na nuna mulki na Allah ne, shi yake ba wanda yaso sannan in fadi nagartar dan takara. Wannan shine dalilin daya sa na fi karkata ga sarakunan gargajiya da wakokin fadakarwa don sake fadada tarihi da Adabi.

Mahangar Arewa: Kana da Uban gida a harkar waka?

ALA:Kwarai kuwa ina da iyayen gida a harkar wakar da nake yi, wasun su mawaka ne wasun su ba mawaka bane daya daga cikin mawaka uban gidana shine Abdullahi sani Makarantar lungu malamine cikakke masanin fannoni amma kuma yana isar da sakonninsa ta hanyar wasan kwaikwaiyo a rediyo ko kuma wakoki na ilimantarwa to shine ubangidana a harkar waka sannan kuma a masana akwai farfesa Sa'idu Muhammad Gusau sai malamai na kwaleji irinsu malam Dalha da malam Aminu cigari, Malam Hassan da makamantansu wadanda idan sun ga na yi wani abu ba daidai ba sukan kira ni su min gyara, haka ma a bangaren Shari'a akwai alkali masanin shari'a Mahmud wanda zai zauna na yi masa tambayoyi akan duk abinda ya shafi shari'a.

Haka ma a rubutu akwai irin su Ado Ahmad Gidan Dabino da Farouk Lawan Da'u wanda yake abokinmu ne, amma mutumne mai ilimi da saukin kai gashi baya rowar abinda ya sani, duk suma in muka yi kuskure sukan taimaka mana wajen gyara, wannan a takaice kenan.

Mahangar Arewa: Tsawon lokacin da ka diba kana waka zaka iya gaya mana adadin wakokin da ka yi?

ALA: To wannan tambayar ana yawan yi min ita amma dai amsar wannan tambayar sai manazarta domin sune suke bin diddigin abinda mawaki ya yi don taskancewa, ni kuma waka faruwa take kuma kullum yi nake ina yin wakokin talla ina yin na sa kai, sannan ina yin wakoki na sarauta wanda samun wani abin alfahari ga sarki sai ya a yi masa waka inda zai baka jawabinsa, saboda haka ka ga wasu wakokin al'umma ne suke samar dasu dangane da faruwar wani al'amari, wasu kuma fadowa suke kana tafe, wannan shi yasa ban san adadin wakokina ba, ba kuma dan basu da adadi ba, amma dai nasan ina da kaset din hadakar wakokina wanda sun kai a kalla ashirin da biyu a kasuwa.

Mahangar Arewa: Daga cikin wakokin daka rubuta wacce ce tafi baka wahala kuma ba zaka manta da ita ba?

ALA:To wakar data fi bani wahala kwanan nan ne ma na yi ta Mai suan Budaddayir wasika ga shugaban kasa, saboda na rubutata a cikin lokaci kankani sai kuma na kasa karasawa sai washe gari kuma na kasa karantata an yi kida an gama har na fara na yi rabi sai kuma na kasa karasa ta haka nasa aka goge kidan na sake na yi na gama na ji kuma bata yi min ba, sai bayan na dena jinta cikin yan kwanakin nan ina tafiya a mota ina jinta sai kuma na ji ta yi min.

Mahangar Arewa: Daga cikin wakokinka wacce ce bakandamiyarka?

ALA: Bakandamiyata a baya ita ce lu'ulu'u a cikin juji saboda in aka ce bakandamiya ana nufin wakar data shafi abubuwa da yawa kuma ta shafi mawaki, amma yanzu ina cewa Alfiyya wadda ake kira Shahara sanadin sanina ita ce bakandamiyata.

Mahangar Arewa: A cikin ko wani abu akwai kalubale shin wani kalubale ka taba fuskanta a wannan sana'a ta waka?

ALA: Gaskiya mun fuskanci kalubale wanda a cikin kalubalen nema har kurkuku mun je, daga cikin kalubalen dana fuskanta nema na yi wakar shahara wanda mutane suke son su shahara abinda basa lura shine idan ka daukaka baka da ikon yin abinda wasu mutane zasu yi baka da ikon zama akan hanya ko cin abinci lalle ita daukaka kamar wata kurkuku ce, zaka yi alheri so dubu a ki kalla amma sharrinka daya sai ya zama abin magana saboda haka kullum muna cikin kalubale na rayuwa, sai dai kawai godiyar Allah.

Mahangar Arewa: A cikin wannan sana'ar taka wani alheri ka taba samu gagarumi da kake jin ba zaka manta dashi ba?

ALA: Wannan ita ce karramawar da sarkin kano Dakta. Ado Bayero ya yi min a shekarar daya cika shekara arba'in da biyar akan mulki sai kuma karramawar dana samu a jami'o'i irinsu B.U.K da kuma Danfodiyo inda suka bani jakadan Hausa da Jami'ar A.B.U da kwalejoji to wadannan sune kyaututtukan da bazan taba mancewa dasu ba.

Mahangar Arewa:A cikin mawaka su waye gwanayenka?

ALA: Ni ma'abocin jin wakokine iri-iri amma ina son wakokin su Narambada, Mai daji sabon Birin Dan Anace da Mamman shata gami da Dan kwairo.

A fagen larabci kuwa ina son wakokin Nancy da kuma Aisha Fallatiya irinsu Muhammad Wardi da Sahwa kai har da su Itofiya,

a mawakan yabon manzon Allah(S.A.W) kuma ina son wakokin Rabiu Usman Baba, Bashir Dandago, amma fitaccen gwanina a mawaka shine Marigayi Sa'adu Zungur saboda kaifin basirarsa da iliminsa.

Mahangar Arewa: Mafi yawa daga cikin wakokinka kana sanya azanci gami da bakin kalmomin hausa a ciki me yasa kake haka?

ALA: Wannan ai abubuwa ne na ilimi kamar yadda na gaya maka cewa daga cikin wadanda suke bani shawara akwai malaman addini dana zamani da lauyoyi, saboda haka iya wannan ya isa idan ka dauka kayi waka ya gajiyar da tunanin mai saurare, kuma ni bana raina baiwa ko ta waye wannan shine sirrin?

Mahangar Arewa: Tsawon lokacin da ka yi a masana'antar waka ka taba renon wasu mawaka wanda za'a kalla a ce kai ka kyankyashe su?

ALA:To renon mawaka muna yi kama daga bada shawarwari har zuwa samar da su irin su:

-Nasiru garkuwar Ala

-Sanin Baba tudun murtala

-Sa'id Nagudu da Abubukar mai bibiyu na kaduna wadannan duka ni nayi musu kaset na wakokinsu. Kuma wadannan mawaka ko gobe bana nan sune nake saran za su gajeni wato su dora daga irin wakokina na fadakarwa.

Mahangar Arewa:A karshe wani Fata kake dashi a wannan harka?

ALA: Muna fata gwamnati da malaman addini da kuma jama'a su marawa wannan aiki namu baya domin isar da kyakkyawan sako, idan suka abotake mu zamu dinga yin abubuwa dai-dai zamu wakilci harshen hausa da hausawa cikin nutsuwa sabanin yadda zamu dinga aro wasu abubuwan muna yafawa a ciki, saboda nisa da suka yi damu shi yasa aka bar abin kara zube wanda bashi da albarka sai daidaiku, wannan shine kirana da fatana a wannan harka Allah ya albarkaci wannan sana'a ya bunkasata fiye da tunaninmu.

Mahangar Arewa: Mun gode.

ALA: Ni ma na gode.

Post a Comment

Dear readers, after reading the Content please ask for advice and to provide constructive feedback Please Write Relevant Comment with Polite Language.Your comments inspired me to continue blogging. Your opinion much more valuable to me. Thank you.

TATTAUNAWA DA MAWAKIN ZAMANI AMINU ALAN WAKA

Daga 

Mahangar Arewa: da farko za mu so mu ji takaitaccen tarihinka.

Aminu Ala: To da farko sunana Aminudden Ladan Abubukar wanda aka fi sani da Alan waka,

an haife ni a shekarar 1974 a unguwar Yakasai cikin birnin kano.

Na yi karatun zamani dana Addini dai-dai gwargwado.

Na yi karatun firamare a tudun Murtala primary school daga 1980 zuwa 1986 daga nan na wuce makarantar sakandire ta Dakata kawaji daga 1986-1992 daga nan kuma sai na samu tsaiko ban cigaba da karatuna ba sai na shiga harkar rubutun kirkira wanda daga baya kuma na shiga harkar waka ka'in da na'in inda har takai ina da kamfanin Waka mai suna Taskar Ala global.

Mahangar Arewa: A da mutane a fagen rubutu suka sanka ya aka yi ka koma harkar waka?

Aminu Ala: To gaskiyar magana waka dai ita na soma domin tun dan ina Islamiyya nake waka a wurin Maulidi amma wakar bata shiga cikin al'umma ba sai a shekarar 2003 ta kafar sadarwar gidan rediyon kano,

amma shi rubutu na fara shine a shekarar 1992 kuma bai fara fita ba sai 1999 wannan duk lamari ne na ubangiji ina waka ina rubutun littafi duk harka ce ta kirkira.

Mahangar Arewa: Matsayinka na cikakken mawaki a yau, me ya ja hankalinka ka shiga harkar ka'in da na'in?

Aminu Ala: to kamar yadda na fada maka waka na fara yin ta tun ina islamiyya inda ake koya mana karatu da wake da kuma wakokin yabon manzon Allah (S.A.W) don nuni da daraja da martabarsa, to daga haka muka fara rubuta waka har ma na rubuta wata waka mai suna raina fansa ne ga Annabi Babba dan Babba da kuma wata wakar mai suna Mai duka sa in je madina wadannan duk mu yi su ne a lokacin mauludi akan manbari kuma ni mai yawan sauraren wakoki ne tun da, ka ji dalilin da yasa na tsinci kaina a harkar waka.

Mahangar Arewa: In dai ana magana akan fitattun mawakan Hausa wadanda suka shahara dole sai an lissafa da kai, shin me kake ganin ya jawo maka wannan daukaka?

ALA: To wannan daga Allah ne, haka Allah yake ikonsa kuma babu mai hana shi idan yaso abu haka jama'a za su karbe shi, sannan kuma ina yin wakokin da suka shafi al'umma da fadakarwa akan siyasa da zamatakewa wanda in ka dauke masu wakokin madahu mafi yawa daga cikin mawakan yanzu sun fi yin wakokin soyayya da kuma na fina-finai, wannan shi yasa mutane suka fi karkata bangarenmu.

Mahangar Arewa: Yawanci wakokinka sun fi karkata ga sarakuna da wakokin fadakarwa, me yasa baka fiya wakokin siyasa ba?

ALA: To na lura wakokin siyasa suna jogarantarmu ga zubar da mutunci, baka samun komai a ciki sai ka taba mutuncin wani ko wani yasa kaci mutuncin wani ka kaskantar dashi sannan a baka wani abu wanda kuma gobe kana iya ganinsu tare, kuma ita waka ta riga ta shiga cikin kundin tarihi ka riga ka yi ta, waka tana da hadarin gaske shi yasa ko lokacin dana yi wakokin siyasa bana yin zagi na kan yi kokari na nuna mulki na Allah ne, shi yake ba wanda yaso sannan in fadi nagartar dan takara. Wannan shine dalilin daya sa na fi karkata ga sarakunan gargajiya da wakokin fadakarwa don sake fadada tarihi da Adabi.

Mahangar Arewa: Kana da Uban gida a harkar waka?

ALA:Kwarai kuwa ina da iyayen gida a harkar wakar da nake yi, wasun su mawaka ne wasun su ba mawaka bane daya daga cikin mawaka uban gidana shine Abdullahi sani Makarantar lungu malamine cikakke masanin fannoni amma kuma yana isar da sakonninsa ta hanyar wasan kwaikwaiyo a rediyo ko kuma wakoki na ilimantarwa to shine ubangidana a harkar waka sannan kuma a masana akwai farfesa Sa'idu Muhammad Gusau sai malamai na kwaleji irinsu malam Dalha da malam Aminu cigari, Malam Hassan da makamantansu wadanda idan sun ga na yi wani abu ba daidai ba sukan kira ni su min gyara, haka ma a bangaren Shari'a akwai alkali masanin shari'a Mahmud wanda zai zauna na yi masa tambayoyi akan duk abinda ya shafi shari'a.

Haka ma a rubutu akwai irin su Ado Ahmad Gidan Dabino da Farouk Lawan Da'u wanda yake abokinmu ne, amma mutumne mai ilimi da saukin kai gashi baya rowar abinda ya sani, duk suma in muka yi kuskure sukan taimaka mana wajen gyara, wannan a takaice kenan.

Mahangar Arewa: Tsawon lokacin da ka diba kana waka zaka iya gaya mana adadin wakokin da ka yi?

ALA: To wannan tambayar ana yawan yi min ita amma dai amsar wannan tambayar sai manazarta domin sune suke bin diddigin abinda mawaki ya yi don taskancewa, ni kuma waka faruwa take kuma kullum yi nake ina yin wakokin talla ina yin na sa kai, sannan ina yin wakoki na sarauta wanda samun wani abin alfahari ga sarki sai ya a yi masa waka inda zai baka jawabinsa, saboda haka ka ga wasu wakokin al'umma ne suke samar dasu dangane da faruwar wani al'amari, wasu kuma fadowa suke kana tafe, wannan shi yasa ban san adadin wakokina ba, ba kuma dan basu da adadi ba, amma dai nasan ina da kaset din hadakar wakokina wanda sun kai a kalla ashirin da biyu a kasuwa.

Mahangar Arewa: Daga cikin wakokin daka rubuta wacce ce tafi baka wahala kuma ba zaka manta da ita ba?

ALA:To wakar data fi bani wahala kwanan nan ne ma na yi ta Mai suan Budaddayir wasika ga shugaban kasa, saboda na rubutata a cikin lokaci kankani sai kuma na kasa karasawa sai washe gari kuma na kasa karantata an yi kida an gama har na fara na yi rabi sai kuma na kasa karasa ta haka nasa aka goge kidan na sake na yi na gama na ji kuma bata yi min ba, sai bayan na dena jinta cikin yan kwanakin nan ina tafiya a mota ina jinta sai kuma na ji ta yi min.

Mahangar Arewa: Daga cikin wakokinka wacce ce bakandamiyarka?

ALA: Bakandamiyata a baya ita ce lu'ulu'u a cikin juji saboda in aka ce bakandamiya ana nufin wakar data shafi abubuwa da yawa kuma ta shafi mawaki, amma yanzu ina cewa Alfiyya wadda ake kira Shahara sanadin sanina ita ce bakandamiyata.

Mahangar Arewa: A cikin ko wani abu akwai kalubale shin wani kalubale ka taba fuskanta a wannan sana'a ta waka?

ALA: Gaskiya mun fuskanci kalubale wanda a cikin kalubalen nema har kurkuku mun je, daga cikin kalubalen dana fuskanta nema na yi wakar shahara wanda mutane suke son su shahara abinda basa lura shine idan ka daukaka baka da ikon yin abinda wasu mutane zasu yi baka da ikon zama akan hanya ko cin abinci lalle ita daukaka kamar wata kurkuku ce, zaka yi alheri so dubu a ki kalla amma sharrinka daya sai ya zama abin magana saboda haka kullum muna cikin kalubale na rayuwa, sai dai kawai godiyar Allah.

Mahangar Arewa: A cikin wannan sana'ar taka wani alheri ka taba samu gagarumi da kake jin ba zaka manta dashi ba?

ALA: Wannan ita ce karramawar da sarkin kano Dakta. Ado Bayero ya yi min a shekarar daya cika shekara arba'in da biyar akan mulki sai kuma karramawar dana samu a jami'o'i irinsu B.U.K da kuma Danfodiyo inda suka bani jakadan Hausa da Jami'ar A.B.U da kwalejoji to wadannan sune kyaututtukan da bazan taba mancewa dasu ba.

Mahangar Arewa:A cikin mawaka su waye gwanayenka?

ALA: Ni ma'abocin jin wakokine iri-iri amma ina son wakokin su Narambada, Mai daji sabon Birin Dan Anace da Mamman shata gami da Dan kwairo.

A fagen larabci kuwa ina son wakokin Nancy da kuma Aisha Fallatiya irinsu Muhammad Wardi da Sahwa kai har da su Itofiya,

a mawakan yabon manzon Allah(S.A.W) kuma ina son wakokin Rabiu Usman Baba, Bashir Dandago, amma fitaccen gwanina a mawaka shine Marigayi Sa'adu Zungur saboda kaifin basirarsa da iliminsa.

Mahangar Arewa: Mafi yawa daga cikin wakokinka kana sanya azanci gami da bakin kalmomin hausa a ciki me yasa kake haka?

ALA: Wannan ai abubuwa ne na ilimi kamar yadda na gaya maka cewa daga cikin wadanda suke bani shawara akwai malaman addini dana zamani da lauyoyi, saboda haka iya wannan ya isa idan ka dauka kayi waka ya gajiyar da tunanin mai saurare, kuma ni bana raina baiwa ko ta waye wannan shine sirrin?

Mahangar Arewa: Tsawon lokacin da ka yi a masana'antar waka ka taba renon wasu mawaka wanda za'a kalla a ce kai ka kyankyashe su?

ALA:To renon mawaka muna yi kama daga bada shawarwari har zuwa samar da su irin su:

-Nasiru garkuwar Ala

-Sanin Baba tudun murtala

-Sa'id Nagudu da Abubukar mai bibiyu na kaduna wadannan duka ni nayi musu kaset na wakokinsu. Kuma wadannan mawaka ko gobe bana nan sune nake saran za su gajeni wato su dora daga irin wakokina na fadakarwa.

Mahangar Arewa:A karshe wani Fata kake dashi a wannan harka?

ALA: Muna fata gwamnati da malaman addini da kuma jama'a su marawa wannan aiki namu baya domin isar da kyakkyawan sako, idan suka abotake mu zamu dinga yin abubuwa dai-dai zamu wakilci harshen hausa da hausawa cikin nutsuwa sabanin yadda zamu dinga aro wasu abubuwan muna yafawa a ciki, saboda nisa da suka yi damu shi yasa aka bar abin kara zube wanda bashi da albarka sai daidaiku, wannan shine kirana da fatana a wannan harka Allah ya albarkaci wannan sana'a ya bunkasata fiye da tunaninmu.

Mahangar Arewa: Mun gode.

ALA: Ni ma na gode.

No comments:

Post a Comment