0
ASALI DA GINUWAR DAIDAITACIYAR HAUSA DA KA'IDOJINTA ASALI DA GINUWAR DAIDAITACIYAR HAUSA DA KA'IDOJINTA

Daga Malumfashi Ibrahim Tarihin rubutu da karatu irin na boko a kasar Hausa da muka sani ya biyo matakai-matakai a tsawon tarihi, wanda d...

0
BULAGURON MARUBUCI BUKAR USMAN ZUWA BURKINA FASO BULAGURON MARUBUCI BUKAR USMAN ZUWA BURKINA FASO

A cikin Afirilun bana, Gidan Adana Kayan Tarihi na kasar Burkina Faso tare da hadin gwiwar Kungiyar Makaranta sun karrama marubuci Dokta ...

0
MARUBUTA MATA: JIYA DA YAU MARUBUTA MATA: JIYA DA YAU

MARUBUTA MATA: JIYA DA YAU Tare da Dokta Balbasatu Ibrahim (Mrs) Tun da Allah ya halicci duniya ya jarabi dan adam da abubuwa guda uku. W...

0
SABANI GAME DA WASU KA'IDOJIN RUBUTUN HAUSA. SABANI GAME DA WASU KA'IDOJIN RUBUTUN HAUSA.

DAGA Nasir G Ahmad, ZUWA GA FARFESA MALUMFASHI: Kamar yadda aka ba da shawara, za mu so jin ra'ayin Malam, da ma sauran malamai kan s...

0
YUNKURIN 'YAN KASUWA WAJEN KAFA MULKIN DIMOKARADIYA A NIJERIYA. YUNKURIN 'YAN KASUWA WAJEN KAFA MULKIN DIMOKARADIYA A NIJERIYA.

Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya +2348065025820 abuhidya3@gmail.com GABATARWA Wannan shi ne kundin kudiri na gamayyar tunanin kafar tur...

0
AN YI NADIN SABON SARKI A MASARAUTAR BANDE AN YI NADIN SABON SARKI A MASARAUTAR BANDE

Daga Rabi'u Muhammad Abu Hidaya Masarautar Bande wadda ta kasance masarauta mai dadadden tarihi cikin masarautun kasar Nijar ta samu ...

ASALI DA GINUWAR DAIDAITACIYAR HAUSA DA KA'IDOJINTA

Daga Malumfashi Ibrahim
Tarihin rubutu da karatu irin na boko a kasar
Hausa da muka sani ya biyo matakai-matakai a
tsawon tarihi, wanda daga nan ne aka samar da
ka'idojin rubutun da kuma samar da Daidaitacciyar Hausa. Tun daga
farko dai abin da ya dace mu
fahimta shi ne tun kafin zuwan Turawa an rubuce
Hausa cikin wasu haruffan da ba na Turawa ba;
akwai dai masu hasashen an rubuce Hausa cikin
Girkanci, daga baya kuma aka sake rubuce ta cikin
Larabci da Ajami. Da yake ba wani rubutun Hausa da muka gani a kasa na
Girkanci har zuwa yau, za
mu iya cewa an fara daidaita rubutun Hauda ne da
Ajami, wato da haruffan Larabci. Wannan
dadaddiyar hanya ita ce Turawan Mishau suka iske,
suka gyara, suka bi domin kokarin daidaita
rubutun Hausa a cikin Romanci ko Latinanci a cikin littattafansu da suka samar.
Ke nan za mu iya cewa an soma yin rubutun Hausa
ne da kuma daidaita shi a cikin Ajami, zuwan Boko
ya kara masa muhibba da martaba a tsakanin
masana, saboda haka muna iya cewa daga abin da
Ajami ya tanadar ne aka samar da tsarin rubutun Bokon Hausa.
Ka'idojin farko na rubutun Boko da aka samu a
rubuce su ne wadanda R. H. Robinson ya gabatar a
1848 karkashin kungiyar CMS, inda bayan samar
da bakaken Hausa da wasullansu an fito da batun
haruffan nan da ke da lankwasa, wato d da k da b wadanda aka dinga yi
masu digo a karkashi domin
a bambanta da wadanda ba su da lankwasa.
Bayan Robinson sai kuma Raberan Schon wanda
ya rayu tsakanin 1803-1889, ya yi rubuce-rubuce
da dama da suka hada da:
Vocabulary of the Hausa Language (1843) Dictionary of the Hausa Language (1876)
Grammar of the Hausa Language (1862)
Magana Hausa (1885)
Duk da cewa Schon bai ziyarci kasar Hausa kai
tsaye ba, amma ta hulda da wadanda suka ziyarta
da kuma 'yan kasa da ya hadu da su a cikin rayuwarsa ya sa ya shiga
cikin aikin raya da rubuta
Hausa domin na baya. Shi ma ya tabbatar da kusan
dukkan bakake da wasullan Hausa da Robinson ya
samar, wadanda kuma har yau ana amfani da su,
sai dai babbar matsalar da ya fuskanta ita ce ta
haruffa masu lankwasa da ya bari kamar yadda Robinson ya samar da su,
don ya rasa yadda zai yi
da su. Haka kuma ya ci karo da matsalar hamza,
wato haruffa irin su:
/Tsami/, wanda ya rubuta kamar haka, /Sami/
/'Ya'ya/ da ya rubuta kamar haka /Yaya/
/Waje/ ya rubuta kamar haka, /Waze/ Wani da ya yi wa rubutun Hausa
bauta shi ma shi
ne Charles H. Robinson (1861-1925), shi ma
manazarcin harshe ne kuma dan Mishau, ya iya
Larabci sosai, ya kuma nakalci Ajami gwargwado.
Ya yi rubuce-rubuce da dama da suka hada da:
Specimen of Hausa Literature (1896) Hausa Grammar (1897)
Dictionary of the Hausa Language (1899)
Tun farkon nazarinsa ya san da haruffa masu
lankwasa, saboda haka ya bar su da digo a
karkashin haruffan d da b da k. Sai dai shi ma ya
samu matsala wajen raba da kuma hada kalmomi ta yadda da yawa suka ba
shi ruwa. Alal misali yana
rubuta wasu jimloli kamar haka:
/Akakama/ a maimakon /Aka kama/
/Anayaki/ a maimakon /Ana yaki/
Wani dan Mishau da ya taka rawar gani wajen
rubuta da daidaita Hausa shi ne Hans Vischer Dan Hausa (1876-1945). Da
farko aikin Mishau ya fara,
daga baya kuma ya shiga aikin mulkin mallaka,
inda ya zauna a kasar Hausa, ya nakalci Hausar da
al'adun Hausawa har aka dinga kiran sa Dan Hausa
saboda sajewar da ya yi. Shi ne ya samar da
makarantar Boko ta gwamnati ta farko a kasar Hausa, ya kuma kasance
jami'i mai kula da sha'anin
Ilimi a kasar Hausa. Shi ne ya fito da ka'idonjin
rubutun Hausa na farko a shekarar 1912, wato
Rules for Hausa Spelling, inda ya tabbatar da
bakake da wasullan Hausa da muke gain yanzu, ya
kuma nemi ya gyara matsalar haruffa masu lankwasa, inda a maimakon
yadda ake rubuta su a
da a karkashin haruffan d da b da k sai ya maido a
sama da alamar hamza, domin a gan su a fili a kuma
fade cikin sauri wajen karatu. Ga yadda ya tsara su
da sauran wasu daga cikin dokokin da ya samar.
/'b/ /'d/ /'k/ /Mache/ a maimakon /Mace/
/'Ya/ a madadin /Y/
/Rigas Sarki/ a maimakon /Rigas Sarki/
/Sayam Masa/ a madadin /Sayar Masa/
/Farri/ a matsayin /Fari/
/Fatta/ a madadin /Fata/ /Sayesaye/ a madadin /Saye-saye/
Wanda ya biyo layi shi ne Raberan G.P Bargery
(1876-1960), shi ma kamar sauran da ya biyo
bayansu ya bauta wa Mishau, a cikin haka ya
inganta rubutun Hausa da ka'idojinsa. Babbar
gudunmuwar da ya bayar ita ce ta samar da kamus na Hausa-English
Dictionary and English–Hausa
Vocabulary. A cikin wannan gagarumin aiki da ya
yi a shekarar 1934, ya ci gaba ne daga inda Hans
Vischer ya tsaya, ta amincewa da haruffa masu
lankwasa, sai dai shi ma ya rubuta su a saman
haruffa da hamza, kamar yadda Vischer ya yi. Sai dai ya sake canza
wasu haruffa masu aure ko
tagwaye, irin su /Ch/ ta koma /C/, wato ya rubuta /
Caca/ a maimakon /Chacha/, ya soke amfani da
nannagen haruffa a cikin kalmomi wato irin su /sh/
ko /ts/ a tsakanin kalma ya mayar da su zuwa /s/
ko /t/ alal misali, /shashshaka/ ake rubutawa a da, shi kuma ya rubuta
kamar haka, /shasshaka/ ko
kuma /tsatstsafa/ ya mayar da ita kamar haka, /
tsattsafa/. Haka kuma shi ne ya fara bayani a fili
bambanci tsakanin ka'idojin rubutun Hausa na
Karin Harshe da Daidaitacciyar Hausa, inda yake
bambanta su a cikin aikinsa, misali: /Sayar da shi/, a maimakon /Sayad
da shi/ wanda
Katsinanci ne.
/Rigar Sarki/, a maimakon /Rigas Sarki/ wanda
Katsinanci ne.
Bargery ne kuma ya fara tabbatar da samuwar
karin sauti a cikin rubutun Hausa, yana sanya alamar – a karkashin
kowane harafi mai dauke da
karin sauti na kasa, na sama saboda yawan fitar sa
a cikin harshen bai ba shi wata alama ba. Haka
yana nuna yadda ake rubuta dogo da gajeren
wasali.
Daga Bargery sai dalibinsa R. C. Abraham (1890-1963), ma'aikacin
gwamnatin mulkin
mallaka ne wanda ya taba zama ADO a Kano. Ya
bauta wa Hausa gwargwadon iyawarsa, inda ya
rubuta littattafai da suka hada da Principles of
Hausa a 1934 da A Modern Grammar of Spoken
Hausa a 1941 da Dictionary of the Hausa Language a 1949 da kuma The
Language of Hausa People a
1959. Kodayake aikin Abraham ya kasance na
zamani, duk da haka daga abin da Bargery da
Gwamnatin Arewa ta shirya ne ya gina nasa. Sai dai
ya kasance mai kawo nasa canjin shi ma domin shi
ne ya fara rubuta haruffan Hausa masu lankwasa kamar yadda suke a
halin yanzu, wato a shekarar
1938. Haka kuma ya bambanta tsakanin haruffan /
n/ biyu, wato ra-gare da ra-kade, misali a hanci da
tankade. Ya kuma nuna inda karin sauti ke fita da
tsawon wasali, inda yake sa wannan alamar – a
saman dogon wasali da kuma – a kasan harafi mai karin sauti na kasa,
kamar yadda Bargery ya yi.
Daga wannan lokaci ne aka tabbatar da samuwar
Daitattaciyar Hausa da ka'idojin rubutun Hausa.
Dukkan abubuwan da suka faru a baya za a ga
daidaikun mutane ne ke yi da kulawar hukuma, sai
dai hukuar ba ta sa baki ba sosai da sosai sai a shekarar 1955 da aka
kafa Hukumar Kula Da
Lamurran Hausa, wadda hukuma ce da ta yi
kokarin daidaita Hausa da samar da ka'idojin
rubuta Hausar. Ta yi abubuwa da dama, ita ce ta
gyara da tantance duk wadansu kalmomin aro da
na kimiyya da fasaha. Wannan hukuma ce kuma ta waiwayi aikin da Hans
Vischer ya yi a 1952 domin
daidaita tunani da zamani, ta samar da kundin da ta
kira Rules for Hausa Orthography a 1958. A daidai
wannan lokaci ne aka tsayar da karin Hausar Kano
a matsayin Daidaitacciyar Hausa, sai dai an shelanta
cewa duk inda aka sami kalmomi da a cikin garin Kano kadai ake furta
su, ana iya maye gurbinsu da
wadansu daga kare-karen Hausa can daban da
suka fi karbuwa.
Bayan da Turawan mulkin mallaka suka bar kasar
Hausa, an yi ta kokari daga 'yan gida a daidaita
rubutun Hausa. Taro na farko da aka yi shi ne a birnin Bamako na kasar
Mali a shekarar 1966,
karkashin jagorancin Hukumar UNESCO, inda aka
tattauna yadda za a daidaita rubutun Hausa a
Yammacin Afrirka. A wannan taron ne aka amince a
rubuta Hausa kamar haka.
Haruffa masu lankwasa /b/ da /k/ da /d/ kamar yadda suke yanzu.
Aka samar da tagwayen haruffa /sh/ da /ts/ da /
gy/ da /ky/ da /ky/ da /gw/ da /kw/
A kuma raba /su/da /na/ wato /su na/ ko /ka na/
ko /ki na/ da /ya na/ dss
A shekarar 1970 kuma an yi wani taron a jami'ar Ahmadu Bello, Zaria
inda aka sake kallon aikin da
Hukumar Kula Da Lamurran Hausa ta yi a 1958, aka
samar da sababbin bayanai kamar haka:
A dinga rubuta /ko'ina/ ba /ko ina/ ba
Haka a rubuta /yake/ ba /ya ke/ ba, ko /yakan/
ba /ya kan/ ba, /suna/ ba /su na/ ba. Da kuma /mutum/ ba /mutun/ ba
Da /malam/ ba /malan/ ba
/Ranar kasuwa/ ba /ranak kasuwa/ ba
A shekarar 1972 kuma an sake gudanar da wani
taro a a jami'ar Bayero Kano, wanda shi ma ya yi
kokarin daidaita ka'idojin rubutun Hausa, an amince da 'yan
gyare-gyare da dama, wadanda za
iya cewa su ne har yau ake amfani da su a duk
fadin duniyar Hausa.
Ga kadan daga abubuwan da aka amince da su a
wurin taron, kamar yadda M.K.M.Galadanci ya
kattaba. Universal nouns are written as one word
/komai/ ba /ko mai/ ba
/kowa/ ba /ko wa/ ba
/koyaushe/ ba /ko yaushe/ ba
Where the pre-verbal pronoun precedes the tense
marker it is written as one word. /yakan/ ba /ya kan/ ba
/yana/ ba /ya na/ ba
Where the tense marker precedes the pre-verbal
pronoun it is written separately.
/za mu/ ba /zamu/
/za su/ ba /zasu/ ba A short possessive is joined to the preceding
nominal
/dokina/ ba /doki na/ ba
/rigarsa/ ba /rigar sa/ ba
/zanenta/ ba /zanen ta/ ba
But the long possessive is written separately /wani doki nawa/ ba
/wani dokinawa/ ba
/wata riga tawa/ ba /wata rigatawa/ ba
/wani zane nata/ ba /wani zanenata/ ba
The pronoun object is written separately
/ya ba ni/ ba /ya bani/ ba
/mun sa shi/ ba /mun sashi/ ba /ana kiran ka/ ba /ana kiranka/ ba
Haka kuma an jaddada cewa /saboda/ da /
watakila/ kalmomi ne a cure wuri guda, ba a
rubuta su a ware ba, wato /sabo da/ ko /wata kila/
ba da sauran su.
Taron karshe da aka yi na daidaita rubutun Hausa shi ne wanda aka yi a
Niamey, a kasar Nijar a
shekarar 1980, karkashin jagorancin Kungiyar
Hada Kan Afirka, (OAU). An shirya wannan taro ne
don a mayar da hankali wajen daidaita rubutun
Hausa a Nijeriya da Nijar, shi ma wannan taro ya
amince da muhimman bayanai da suka hada da: An tabbatar da gajerun
wasullan Hausa: i,e,a,o,u
An tabbatar da dogayen wasullan Hausa:
ii,ee,aa,oo,uu
Da kuma bakaken Hausa kusa 33
Daga lokacin da aka kashe Hausa Language Board
(Hukumar Kula Da Lamurran Hausa) da aka kafa a 1958 sai aka mayar da
yawancin ayyukanta ga
Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya da ke karkashin
Jami'ar Bayero, Kano, ita ce mai kula da ka'idoji da
daidaita rubutun Hausa, kuma tun daga 1982 ta yi
iyakacin kokarinta na yin wannan aiki tukuru. Ita
ce ke shirya tarurrukan inganta harsunan Nijeriya (musamman na Hausa
da Fulfulde da Kanuri), ta
kuma samar da aikin fassara kalmomin zamani
zuwa Hausa da kuma Kamusun Hausa da ta buga a
shekarar 2007, bayan sama da shekara 30 ana
bincike da nazari da bita.
Inda muke ke nan yanzu, ba wani taro kuma da aka kara yi har zuwa yau
da na sani domin daidaita
ko sake shata ka'idojin rubutun Hausa, wanda da
zarar an samu wannan dama duk wata matsala a
nan za a tattauna ta, a kuma samar da matsaya
domin amfanin sauran al'umma. Allah shi ne
masani!

BULAGURON MARUBUCI BUKAR USMAN ZUWA BURKINA FASO

A cikin Afirilun bana, Gidan Adana Kayan Tarihi
na kasar Burkina Faso tare da hadin gwiwar
Kungiyar Makaranta sun karrama marubuci
Dokta Bukar Usman da kambin girmamawa,
bisa la'akari da gudunmowarsa wajen bunkasa
Adabin Hausa da kuma jaddada zaman lafiya tsakanin al'ummar Hausa da
duniya baki daya.
Bayan ya dawo, ya rubuta wannan tsaraba ga
masu karatu, kamar haka: Ita dai Kungiyar Makaranta, kungiya ce mai zaman
kanta, wacce ba ta gwamnati ba kuma al'ummar
Hausawa mazauna kasar Burkina Faso ce ta kafa ta
a 2006, da nufin bunkasa al'adu, ilimi,
zamantakewa, tattalin arziki da kuma harshen
Hausa a kasar. Domin tabbatar da wannan kuduri nata, sai kungiyar ta
shirya gagarumin biki, wanda
ya hada da kalankuwa, baje kolin kayan gargajiya,
babban taron masana daga ko'ina a duniya da
kuma karrama wasu muhimman 'yan Afrika da
suka taimaka wajen bunkasa al'ummar Hausawa.
Ina daya daga cikin wadanda aka zaba, domin karramawa. Haka kuma, ba
yan ni kaina, an kuma
zabi Sanata (Injiniya) Rabi'u Musa Kwankwaso,
tsohon Gwamnan Jihar Kano. Sanata Kwankwaso da ni kaina, mun halarci
bikin a Babban Birnin Burkina Faso, Ouagadougou
(Wagadugu). Ma'anar sunan birnin nan shi ne
'Wurin da ake karrama da girmama mutane' - babu
shakka birnin ya ci sunansa, domin kuwa hakika
ana girmama baki da daraja su. An karrama ni da kambi tare da takardar
shaida mai taken 'Jakadan
Adabin Hausa.' Wannan taro na kasa-da-kasa, an yi masa lakabi
da "Gudunmowar Al'adun Hausa Wajen Wayar Da
Kan Al'ummar Afirka." Kasar Hausa ta yi fice wajen
saka da rini da kira da jimar fata da ginin tukwane
da sauran ayyukan fasaha da zayyana, wadanda
ake sayarwa har wajen kasar ta Hausa. Harshen Hausa na daya daga cikin
manyan harsunan
duniya. Adabin Hausa na ci gaba da bunkasa,
musamman ana samun rubuce-rubuce a fannoni
da dama na ci gaban al'umma, duk kuwa da cewa
akwai bukatar a rika amfani da na'urorin zamani
tare da tsarin dauri wajen taskance harshen da al'adunsa domin amfanin
gida da ma al'ummar
duniya baki daya. An nuna sha'awar sanin ainahin
sunayen da ake amfani da su a kasar Hausa, kafin
zuwan Musulunci, sannan kuma aka nuna takaici
da yadda yara kan gaza yin magana da harshen
iyayensu. A yayin bikin nunin kayan al'adun gargajiya na
Hausa, wanda Ministan Al'adu Da Shakatawa na
Burkina Faso, Mista Tahirou Barry ya bude, an baje
kolin kayayyaki daban-daban, har ma da abincin
gargajiya. Kayan sun hada da zayyane-zayyane da
aka yi na fata, duwatsu, tabarmi da mafutai, kayan aikin noma, kayan
girki da na cin abinci, korai,
sakakkun suturu da kuma tukwane iri daban-
daban da aka yi wa zayyana masu kyau. Haka
kuma akwai ingantattun magungunan gargajiya
da sake-saki, nama iri-iri da kayan sha na gargajiya
daban-daban. An sha kallo kuma an nishadantu da kade-kade
da wake-waken gargajiya na Hausa, ga wasanni,
musamman na kokowa da aka gudanar. Wasan
kokowa na daya daga cikin wasanni masu tashe a
kasar Burkina Faso. Tawagar karfafa kuma
gwanayen kokowa daga Jamhuriyyar Nijar ta halarci bikin. A yayin da
aka gudanar da tarukan
kara wa juna ilimi a ranakun 14-16 na watan Afrilu,
an ci gaba da baje kolin kayayyakin gargajiya,
wanda zai dore har zuwa tsakiyar Yunin bana. Zan iya tunawa, a
lokacin da nake makarantar
sakandare, a 1960, na samu labarin madaukakun
Daulolin Mossi Dagomba da ke yankin Tsakiyar
Afrika ta Yamma. A wannan zamani a yau, a
Burkina Faso, irin wadannan dauloli da suka
bunkasa, sun ci gaba da bunkasa har zuwa lokacin da Turawan mulkin
mallaka na Faransa suka
murkushe su a wajajen 1896. Wannan dalili ma na
daga cikin dalilan da suka sanya na yi kwadayin
ziyartar kasar, musamman domin in tantance
wadannan kayatattun labarun da suka shafi kasa
da al'ummomin Burkina Faso, kamar yadda aka gaya mana a can baya.
A sakamakon tsawon lokacin da na yi ina
nazarin tsarin al'umma, na fahimta da cewa duk mai
son ya fahimci tarihi da al'adun al'umma, zai iya
samun ilimi mai yawa daga almara da
tatsuniyoyinsu. Wannan ya sanya a lokacin da na
sauka a birnin Wagadugu, tun ma kafin in sauka a masaukina na otel,
sai na yi wa shagon sayar da
littattafai tsinke, domin in samu littafin da ya yi
bayani game da kasa da al'ummar Burkina Faso.
Tabbas kuwa na ga littattafai da yawa da za su yi
mani amfani, amma abin takaici, babu ko daya da
aka rubuta da Ingilishi. Na yi kokarin tambayar inda zan samu littattafan
da nake nema, amma ban dace ba. Don haka sai na
maida hankali ga intanet, inda na samu bayanai irin
na kunne-ya-girmi-kaka. Na fahimta da cewa a
kasar, manyan yarukan da ake amfani da su, su ne
Moore da Djula da kuma Faransanci. Burkina Faso na da kabilu 63,
cikinsu har da Fulani da Yarabawa
da Ibo, tare da shugabanninsu. Burkina Faso, wadda ke nufin 'kasar mutane
masu gaskiya' tana da tarihi mai tsawo. Tarihinta ya
faro ne tun 1896, lokacin da Faransa ta yi tunga a
yankin a matsayin mallakinta. A 1904, Faransa ta
mallaki kasar Upper Senegal da Yankin Nijar a
Afrika ta Yamma, inda birnin Bamako ya kasance hedikwata. Daga bisani
aka canja wa yankin suna
zuwa French Upper Volta mai hedikwata a
Wagadugu, a 1919. A shekarar 1932 aka rushe
wannan tsari, aka karkasa kasashen zuwa Ivory
Coast da Sudan da Nijar. An sake maida ta tsarin
baya a 1947, inda aka dawo da yankin Upper Volta, aka mayar mata da
iyakokinta. An ba ta
mulkin kanta a 1958, sannan aka ba ta 'yancin kai
da sunan Jamhuriyyar Upper Volta a 1960. Kamar dai yadda ta faru
a Najeriya, sojoji sun
tsoma hannunsu a mulkin Jamhuriyyar Upper Volta
a 1966, inda gwamnatin ta soja ta kare a 1976.
Sabuwar gwamnatin farar hula da ta gaji ta soja, an
tunkude ta ita ma a 1980, inda sojan suka ci gaba
da mulki zuwa 1983. Thomas Sankara da Blaise Campaore ne suka ci gaba
da mulki a kakin soja
kuma wannan gwamnatin ce ma ta canja wa kasar
suna zuwa Burkina Faso a 1984. Bayan an yi wa
Thomas Sankara kisan gilla a 1987, kasar ta samu
natsuwar mulki a karkashin Shugaban Kasa Blaise
Campaore na tsawon shekara 27. An matsa masa lamba, dole ya sauka daga
mulki a 2014. Tsohon sunan kasar na Upper Volta, an samo shi
ne daga Koramar Volta, wacce ta hade har zuwa
Kogin Atilantika, wanda ya ratsa har zuwa kasar
Ghana a yanzu. Wani Baturen Fotugal ne ya rada
mata sunan "Volta" domin ya yi la'akari da yadda ta
yi ta kwana-kwana. Koramar tana da manyan bakuna uku, Farar Volta, Jar
Volta da kuma Bakar
Volta, wanda haka ke nuna launin kasar wuraren.
Launin kasar Wagadugu ja ce kuma Jar Volta na
Arewa Maso Yammacin Wagadugu. Burkina Faso a yanzu haka tana da yawan
mutane miliyan 20, inda Wagadugu ne Fadar
Gwamnati, wanda ke kunshe da yawan mutane
kimanin miliyan 2. Birnin Kasuwancin kasar,
sunansa Bobo-Dioulasso, yawan al'ummarsa na
kasa da miliyan daya ne kuma an yi kidayar jama'a ta karshe a 1982.
Mossi ita ce kabila mai mafi yawan mutane a
kasar kuma suna da karin harshe kala biyu,
Kompela da Tenkodogo. Mutanensu sun yi suna
wajen hakuri da juriya, don haka Turawan Faransa
suka rika daukar mazansu aikin soja, kuma aka
rika ba su aikin gina hanyoyin jirgin kasa da na mota. Haka ma
matansu, ba su da son jiki, suna da
kokarin neman abinci. Ba su jin nauyi, domin za ka
gan su suna tuka babur da motocin haya a babban
birnin kasar. Suna yin noma, ban ruwa a fadamu,
aikin buga bulo ko yin aikin siminti. An taba
haramta auren mace fiye da daya a zamanin mulkin Sankara amma daga
baya gwamnatin da ta gaje shi
ta dawo da shi. Wannan ya sanya mutane da suke
daraja al'ada suka rika auren mata da yawa. Duk
macen da mijinta ya mutu, ba ta fita daga gidan
aurenta, sai dai kawai ta zabi namiji daya daga
dangin mijinta, ta sake aure. Noma, shi ne babbar sana'ar mutanen kasar.
Suna noma jar dawa da gyada, haka ma suna noma
acca. Kamar Masar da Sudan, su ma Burkina Faso
suna noma auduga mai yawa da suke sayarwa
kasashen waje. Suna da ma'aidinan zinari da azurfa
da sauransu, wadanda kasashen Australia da Afrika ta Kudu da Faransa
da Japan da Ghana da
sauransu ke amfana sosai ta hanyar hako su. Kasar
tana dogaro da agajin kasashen waje ta bangaren
tattalin arziki. Otel din Laico, wanda kuma ake kira
da Hotel Libya shi ne kusan otel mafi inganci a
Wagadugu. Marigayi Muamar Gaddafi ne ya gina shi kuma yana daya daga
cikin abin alherin da 'yan
kasar ke tuna marigayin shi da shi. Wasu daga ciki
wuraren bude ido a Wagadugu sun hada har da
'Zauren Shahidai' wanda yake kan hanyar Muamar
Gaddafi. An gina shi ne domin tunawa da mutanen
da aka rasa a hautsinin da ya faru a 2014. Masu masaukina a kasar
Burkina Faso, sun
kasance tsatson Hausawa. Kakanninsu sun yo hijira
ne daga Najeriya, musamman daga Kano,
Sakkwato, Katsina, Kebbi da sauran biranen Arewa.
Sun ce sun sauka a Upper Volta ne a matsayin 'yan
kasuwa, masaka, masunta, tun kafin zuwan Turawan Mulkin Mallaka na
Faransa. Sun ce su ne
ma tun farko suka fara kai sana'ar rini da sakar
tufafi a kasar. Har zuwa yau kuwa, irin suturunsu
ne ake alfahari da su a kasar. Akwai al'ummar Hausawa da dama a biranen
kasar Burkina Faso, suna zaune ne a
unguwanninsu da ake wa lakabi ba Zango, sunan
da aka samo a sanadiyyar kasuwancin da ya
gudana shekaru masu yawa da suka shude, inda
'yan kasuwa kan keta sahara daga wannan kasa zuwa waccan a kan rakuma.
Wuraren da suke yada
zango ne ake lakaba wa sunan unguwar ta
Hausawa. A birnin Wagadugu, an canza wa Zango
na ainahi matsuguni har sau biyu, domin kuwa
ayyukan raya birnin ya shafe shi. Zango na farko
yana kusa da tashar jirgin kasa, shi kuwa Zango na biyu, inda nan
Hausawan suka zauna tsawon
shekara 85, yana cikin kawyar birnin, nisan
kilomita biyu daga Fadar Masarautar Moogo Naaba,
Sarkin Gargajiyar Mossi; wanda suke da
kyakkyawar mu'amala da shi. A 2001, Gwamnatin
Blaise Campaore ce ta canza wa Zangon wuri zuwa inda yake yanzu, kusa
da Fadar Shugaban Kasa. Kalilan daga cikin Hausawa da suka yi
karatun
Boko, sun rike manyan mukamai a Ma'aikatun
Gwamnatin Burkina Faso da sauran wurare har ma
da wajen kasar. Daga bisani ne suka farga da
muhimmancin ilimin zamani, inda suka kafa
Kungiyar Makaranta, wacce ke taimakawa wajen fadakar da al'ummarsu,
muhimmancin da ke tattare
da ilimin na zamani. Akwai abubuwa da yawa da mutum zai nazarta
kuma ya karu a kasar Burkina Faso, duk kuwa da
cewa karamar kasa ce da ba ta da yawan
albarkatun kasa kamar wasu. Suna tafiyar da
al'amuransu a kan tsari, ga su da bin doka da oda. Moogo Naaba
(Sarkin Duniya), shi ne lakanin
Sarkin Gargajiya na Mossi da ke Wagadugu. Ana ba
shi girma da daraja sosai. Kasancewar fadarsa na a
babban birnin kasar, yana da martaba ta
musamman, duk kuwa da cewa shi ne na hudu a
tsarin martabar sarakuna a Daular Mossi ta Burkina Faso. Tarihi
ya nuna cewa Daular Mossi a Burkina Faso
ta samo asali ne tun a Karni na 7. Kamar yadda
tarihin ya tabbatar, Sarkin Gambaga na kabilar
Dagomba a Arewacin Ghana, diya mace kawai ya
haifa. Bayan ta yi aure, wata rana sai ta fita kilisa a
doki, ta shiga daji kuma ta yi makuwa. Wani maharbi dan kasar Mali ya
tsince ta kuma suka yi
aure, suka haifi da namiji. Kasancewar a kan doki
aka samu mahaifiyar jaririn, sai aka rada masa suna
Ouedraogo (sunan namijin doki ke nan a Daular
Mossi). Shi Ouedraogo ne ya zama Sarki na farko a
Daular Mossi kuma shi ne ya kafa Masarautar
Tenkodogo. Sarkin Mossi na yanzu a Wagadugu,
Naaba Booggo, shekararsa 34 ke nan a kan
karaga. Shi ne sarki na 147 a jerin sarakunan
daular. Masarautar tana daraja al'ada sosai, musamman akwai wata
al'ada da har yanzu take
wanzuwa. Kamar yadda sauran sarakunan kasar
suka rika yi, duk Jumu'a, Naaba Booggo kan shiga
sulke, ya hau doki da nufin tafiya yaki da wasu
al'umma da ke Mali. Haka za a yi ta lallashinsa, ana
ba shi hakuri, sannan ya sauko. Wannan shauki na yaki ya zama jiki a
masarautar, duk Jumu'a. Mai martaba Naaba Booggo ya amshi
bakuncin
mu mahalarta wannan muhimmin taro. Kafin mu
kai ga ganawa da shi, sai da aka yi ta kai-komo
wajen bin ka'idoji daban-daban amma duk da
haka kwalliya ta biya kudin sabulu. Mutanen
Burkina sun yi suna wajen hakuri, don haka sun dauka bakinsu ma haka
ne. Sarkin na zaune a bisa
karaga, tsakiyar butumbutumin zakoki biyu,
hakoransu a bude, gwanin ban tsoro. Da yarensu
ya yi mana jawabi, tafinta ya rika fassara mana. Ya
yi mana jawabi ne game da rainon yara, inda ya
nuna cewa zamani ya canja, don haka akwai bukatar dattawa su maida
hankali wajen kyautata
rainon yara, domin su tashi da da'a da biyayya, a
matsayin 'yan kasa nagari. Na fahimta da cewa, irin
wannan sakon ne yake isarwa ga dukkan tawagar
da ta ziyarci fadar tasa. Domin kare martabar al'adun Masarautar Mossi,
an haramta wa kowane mutum daukar hoton wani
abu a fadar masarautar ba tare da izini ba. Sarkin
dai ya karrama mu, inda ya amince muka dauki
hoto da shi a wajen fadar. Akwai wani azancin
magana da aka rubuta baro-baro a wata hasumiyar masarautar da harsuna
uku na Moore
da Djula da Fulatanci, kamar haka: "Duk inda ka ga
dattijo, da wuya a aikata ba daidai ba a wurin." Naaba Booggo,
dan kwallo ne. Babu mamaki,
watakila shi ya sanya ma aka gina babban filin
wasa na kasa kusa da fadar masarautarsa. Na samu
bayanin cewa, shahararren dan kwallon nan na
kasar Kamaru, Samuel Eto ne ya gina shingayen
karfe da suka kewaye kofar fadar sarkin saboda nuna gamsuwa da yadda
sarkin ke sha'awar
wasan kwallon kafa. Mun karu da wasu karin azancin magana a fadar
Sarkin Hausawa a Zango. Kakakin Fadar ya ambata
cewa: "Abu ne mai sauki ka ga makiyayi yana
sarrafa garken shanu da sanda guda, a yayin da
abu ne mai matukar wahala ka mulki jama'a kamar
haka." Wannan yana yi mana ishara da yadda mulki ke da wahala.
Taron kara wa juna sani da kuma bikin,
kasancewarsu na kasa-da-kasa, an gayyaci
mahalarta daga kasashen Benin, Kamaro, Afrika Ta
Tsakiya, Chadi, Ghana, Nijar, Najeriya, Togo da
kuma Sudan kuma dukkan wadannan kasashe,
akwai al'ummar Hausawa da yawa. Taron ya samu halartar baki sosai, sai
son barka, domin kuwa
sarakunan gargajiya har uku suka zo daga kasar
Togo kadai. Ba domin matsalolin sufuri da ke
addabar nahiyar Afrika ba, da an samu mahalarta
taron fiye da kima. Amma duk da haka, taron ya
samu yabo daga mahalarta, a yayin da kasashen Togo da Senegal suka
dauki alkawarin shirya irinsa
a nan gaba. Tafiya ta jirgin sama daga Abuja zuwa
Wagadugu akwai wahala. An ba ni shawarar in
shiga jirgi zuwa Kairo (Masar), ko kuma in bi ta
wasu kasashen ma da ba na Afrika ba domin zuwa
Wagadugu. Hanya mafi gajarta, ita ce ta Lome
(Togo) ko Abdijan (Kwaddabuwa) kuma sai mutum ya kwana biyu a hanya.
Matafiya daga
Najeriya da suka biyo ta hanyar mota, sai da suka yi
kwana uku, sun yada zango a Maradi da Yamai
(Jamhuriyyar Nijar), sannan suka isa Wagadugu a
rana ta ukun saboda jidalin bincike-binciken
jami'an tsaro a iyakokin kasashen. Kodayake duk da wannan
jidalin, tafiya ta mota
na tattare da nishadi, domin kuwa mutum zai karu
sosai da sababbin abubuwa a hanya, na mutane iri-
iri da kuma wurare. Ta fannin gane-gane a hanya
kuwa, masu tafiya ta jirgi ma sun karu, domin kuwa
mutum zai samu damar ganin falalen kasa, da itatuwa nan da can da
hanyoyin kasa marasa
kwalta da kuma gidaje warwatse, nan da can. Lallai
akwai yalwar kasa, wacce ya kamata a aikata ta,
domin ceto ta daga balbalcewa. Na yi hira da wasu abokan tafiyata, wadanda
suka bayyana abubuwan burgewa game da
Najeriya. A jirgin da na shiga zuwa Abdijan zuwa
Wagadugu, wani tsohon malamin Kwalejin Fourah
Bay, Saliyo ya bayyana takaicinsa game da Najeriya.
Ya bayyana yadda Allah Ya albarkaci Najeriya da albarkatun kasa amma
saboda halin ko-in-kula na
al'ummar kasar, an kasa amfana. Domin kawo
gyara, ya ce 'Najeriya na bukatar shugaba mai
nuna karfa-karfa, amma ba mai zuciyar kisa ba.' Haka kuma mun
tattauna kan al'amuran da suka
shafi 'yancin dan Adam, musamman sakamakon
yadda wasu mutum biyu suka rika cacar baki da
juna. Daya daga cikinsu ma Bature ne. Wani mutum
ne da ke zaune a bayan Baturen, yake ta magana a
waya da karfi, shi ne Baturen ya kasa daurewa, ya shiga damuwa sosai,
ya yi korafi. Shi kuma mai
waya sai ya harzuka, ya maida masa martani mai
kaushi, sai suka fara fada. Kafin ka ce kwabo, sai
fadan ya girma har da zage-zagen juna, kowa na
nuna cewa shi ke da gaskiya. Baturen ya roki
ma'aikacin jirgin da ya sanya baki amma hakan ba ta samu ba. Haka suka
ci gaba da cacar bakinsu,
har suna cewa za su dambace, da zarar sun sauka
daga jirgin. Duk dai a cikin jirgin nan, wasu fasinjoji biyu,
daya dattijo, daya kuma budurwa ce, su ma sun yi
nasu wasan kwaikwayon. Dattijon ne yake ta buga
kwamfutarsa (laptop) abinsa, sai ita kuma matar ta
yi korafin cewa gwiwar hannunsa na tunkurinta.
Shi kuma mutumin ya yi biris da ita. Haka abin ya ci gaba, ba a samu
maslaha ba sai da matar ta canja
wurin zama. Babu shakka akwai darussa daga abubuwan
nan da suka faru. Wani babban darasi daya a nan
shi ne, a lokacin da mutum ke neman kare
hakkinsa, yana da kyau ya yi la'akari da hakkin
sauran mutane. Idan na kalli wadannan al'amura
da suka faru a jirgi kuma na duba dalilin da ya sanya aka gayyace ni
zuwa Burkina Faso domin a
karrama ni, sai na fahimta da cewa a rayuwa muna
bukatar mu kasance masu fahimtar juna, mu daraja
ra'ayin juna a mu'amala, mu daraja al'adu da
ra'ayoyin juna kuma mu yi iyaka kokarinmu wajen
wanzar da zaman lafiya a tsakanin al'umma. Dokta Bukar Usman,
marubuci ne kuma
tsohon Babban-Sakatare a Fadar Shugaban

MARUBUTA MATA: JIYA DA YAU

MARUBUTA MATA: JIYA DA YAU Tare da Dokta
Balbasatu Ibrahim (Mrs)
Tun da Allah ya halicci duniya ya jarabi dan adam
da abubuwa guda uku. Wadannan abubuwa kuwa
su ne yare, dukiya, da jinsi. Har yau da muke raye wadannan abubuwa na
ci gaba da ci wa Dan adam
tuwo a kwarya. Dalili kuwa shi ne a duk sanda aka
ce wannan shi ne yaren mutum, to zai yi kokarin
ganin cewa martaba da kwarjinin wannan yaren
nasa sun fi na kowa. Alal misali ja-in-jar da aka yi ta
yi tsakanin Turawa da bakar fata a kasar Afrika ta Kudu a shekarun
baya da kuma kisan gillar da 'yan
kabilar Hutu suka yi wa 'yan kabilan Tutsi a kasar
Ruwanda a shekara 1989, haka kuma rikicin da
ake ciki yin a halin yanzu tsakanin Larabawa da
bakar fata a Darfur ta kasar Sudan sun kasance
misalai na irin yadda yare ke tayar da takaddama tsakanin mutane.
Ita ma dukiya ko mulki kan haifar da zalunci da
danniya tsakanin masu hannu da shuni da
talakawa a cikin al'umma. Idan muka dubi irin
tsare-tsaren siyasar da aka yi ta yi a kasashen Turai,
kamar tsarin jari-hujja da na gurguzu da kuma na dimukradiyya da ake
ikirari a yanzu, sai mu ga har
yanzu ba su hutar da talakan ba, sai kara tsotse shi
ake yi, ana kara wa masu karfi, karfi.
Matsala ta uku kuwa ita ce wariyar jinsi, wadda
Jennifer (1985) ta yi bayanni cewa "ta wanzu ne a
sanadiyar ra'ayi ko akidar nan ta cewa "akwai bambancin fifiko
tsakanin namiji da mace a cikin
al'umma". Wannan matsalar ita ce take tashe a halin
yanzu a ko'ina cikin duniya. Tashenta kuwa ya
hada da fagen siyasa da na tattalin arziki da na
yanayin zamantakewa da fasaha da ilmi da sauran
su. A takaice babu bangaren rayuwar da matsalar wariyar jinsi ba ta
kutsa kai ba.
Shigowar wannan matsala ta haifar da ka-ce-na-ce
tsakanin manazarta ciki kuwa har da na adabi.
Ganin cewa bincikena ya shafi harkar bambancin
da ake iya samu tsakanin mace da namiji ta
bangaren rubuce-rubuce ko kuma adabi, na ya dace na soma da fahimtar
yadda wannan
takaddama ta samo asali da yadda take taimakawa
wajen ginawa da raya harkar nazarin ayyukan
mata.
Daga 'yan karance-karancen da na yi, sai na fahimci
cewa duk da cewa ana ta hayagaga kan wannan fage na wariyar jinsin ba
a cika aza tunanin fagen
bisa tafarkin da ya dace ba. Wannan na daga cikin
abin ya shiga cikin zuciyata a lokacin da na soma
tunanin wannan bincike. Shi ya sa ma na na ce a
zuciyata wai me zai hana in dauki fanni daya daga
cikin abubuwan da suka shafi mata in gudanar da zuzzurfan bincike a
kan sa, ta yadda ni ma zan iya
bada gudunmuwa game da irin gudunmuwar da
matan Hausawa ke bayarwa ta fuskar adabi.
Sai dai kafin na shiga cikin gonar aikin nawa ya
kamata mu san cewa wannan hayaniya ta wariyar
jinsi ba sabuwar aba ba ce, ta dade da kutso kai a tsakanin al'umma.
Wasu masana na ganin ewa ta
taso ne tun a wajajen shekarar 1960 har zuwa
shekara 1975 lokacin da Majalisar Dinkin Duniya ta
bullo da shirinta mai take "Shekarar Mata" da na
"Shekarun Mata"a shekarar 1985 aka yi taron
Majalisar na Nairobi, sannan aka yi babban taro wanda yake shi ne na
hudu irinsa da aka taba yi a
kan mata duk duniya, a birnin Beijing na kasar Sin.
Wannan taro an yi masa lakabi da " Taron
Beinjing" (Beinjing Conference), wanda shi a
shekarar 1995 aka gudanar da shi. Wannan taro ya
tattara mahalarta daga ko'ina cikin duniya, ya kuma yanke shawara a
kan sha'anin daidaita jinsi
na in-ba-ka-yi ba-ni wuri. Wato tun daga wannan
taro ne maganar daidaita jinsi take a bakin
kowa;'yan jarida ne ko masana ko manazarta ko
marubuta.
Kafin in ci gaba, na ga ya dace a san menene jinsi da kuma asalin ita
kanta matsalar a da, da kuma
yanzu a cikin al'ummomi daban-daban.
Jinsi kamar yadda aka sani shi ne bambancin da ke
tsakanin namiji da mace a halicce. Wanda kuma ya
shafi tsarin rayuwarsu ta zahiri da badini. Haka
kuma wadannan bambance-bambancen na canzawa da canjin zamani da rayuwar yau da
kullum, Graddol (1993) daga Kassam (1996).
Kodayake wasu masana suna ganin ma'anar jinsi
ba ta tsaya nan ba kawai, alal misali a ganin De
Beauvair (1973:301) "jinsi abu ne wanda mutum
ke iya zabar wa kansa". Ita a ganinta irin rayuwar da mutum ya zabar
wa kansa ita ce take nuna
jinsinsa, ba wai yadda aka halicce shi ba. Namiji na
iya daukar rayuwa irin ta mata, haka kuma mace na
iya zabar rayuwa irin ta maza, ko da kuwa al'umma
ta kyamaci wannan abu.
Haka su kuma Butler (1986.36)da Zimmerman (1991: 13-15) cewa suka yi
al'adu da dabi'un
mutum ko na al'ummarsa, su ne ke da alhakin
bayyana jinsinsa da kuma matsayinsa. Ita kuwa
Riley (1997; 2-6) tana ganin ma'anar jinsi ta wuce
bambanci halitta kawai, ta hada da bambace-
bambancen da ake samu ta bangaren abubuwan da al'umma ke shatawa a
al'adance a kan yadda ya
kamata mata ko maza su kasance. Haka kuma
wadannan ka'idojin sun shafi kowane bangare na
rayuwa, kamar yanayin zamantakewa na yau da
kullun da tattalin arziki da siyasa da neman ilmi da
makamantan su. Har wa yau kuma wadannan tsare-tsare na al'ada su ne
suke haifar da matsalar
daukakar wani jinsi a kan wani ko danniyar da ake
yi wa jinsin mata a cikin wata al'umma. Haka kuma
ana bayyana jinsi a matsayin tsare-tsaren al`umma
a kan da`bi`u da ayyuka da matsayin da ake ganin
ya dace da maza da wadanda suka fi dacewa da mata.
A fahimtata ana iya gwama wadannan ra'ayoyin na
masana a kan ma'anar "jinsi" a tayar da ma'ana
daya kamar haka, mai nufin bambancin halitta
tsakanin mace da maniji da kuma dukkan
sakamakon da wannan zai haifar ta fuskar rayuwar wadannan halitta guda
biyu a doron kasa ta fuskar
wadansu al'adu da ake shatawa ko gindayawa
domin a cimma wadansu manufofi na siyasa ko
zamantakewa.Bisa irin wannan tunani ne za mu
fahimci cewa wariya ko bambancin jinsi y hada
bambancin halitta da kuma bambancin rawar da kowane bangare zai taka
ta fuskar tattalin arziki ko
al'ada ko siyasa da dai duk wata fuska ta rayuwa.
Sai dai wannan bayani bai kasance an yi shi haka
nan sakayau ba, ya samu tubalin gina shi tun da
dadewa, kama daga addini ko siasa ko canjin
rayuwa ta yau da kullum. Saboda haka ya dace mu koma cikin tarihi
domin fahimtar yadda wannan
tunani ya ginu da kuma yadda ake daukar ko
kuma irin matsayin da ake ba wa jinsin mata cikin
al'ummomin daban-daban ta fuskoki daban-daban
.
MATA A ZAMANIN JAHILIYYA Bari mu koma cikin tarihi, mu kuma soma da nan
kusa, musamman wanda ya shafi addinin matan da
za mu yi nazari, wato Musulunci. Za mu ga tun a
zamanin jahiliyyar Larabawa8 ba a dauki mace a
bakin komai ba. Ana ganin an hallice ta kawai
domin ta yi wa maza hidima. Haka kuma ana iya sarrafa ta yadda aka ga
dama. Alal misali, zamanin
jahiliyyar Larabawa sun kasa halitta ga baki daya
zuwa gida uku, kaso na daya su ne mutane, kashi
na biyu kuwa su ba su kai matsayin mutane ba,
amma sun dara dabba, na uku kuwa su ne
dabbobi. Halittar da aka dauka ba ta kai mutum ba, amma ta fi dabba
ita ce mace. Saboda su a wurinsu
mata ba su da kima, ba su da wani zabi a rayuwa
sai yadda aka yi da su. Ana aurar da su yadda aka
ga dama ko kuma a saka su yin karuwanci ko aikin
wahala ba tare da an biya su lada ba. Har ma don
wulakanci gadonsu ake yi kamar dukiya. Wato idan mijin mace ya mutu,
idan yana da wani da
wanda ba nata ba sai ya gaje ta. A nan yana da
damar ya ajiye ta a matsayin matarsa ko baiwa ko
kuma ya sayar da ita. Haka kuma namiji yana da
damar ajiye mace ko nawa yake bukata ba tare da
wata ka'ida ba, saboda irin wulakanci da kaskanci da suka lika wa
mata, har ya kai suna binne
'ya'yansu mata masu rai tun suna jarirai idan ba su
bukata.
A tsohuwar daular Indiya kuwa a al'adar Hindu, an
dauki cewa namiji shi ne ubangijin matarsa (abin
bautarta). Idan ya mutu a tare za a kone gawarsu, alhali tana da rai.
Haka kuma har yanzu mata
mabiya addinin Hindu suna shiga halin kaka- ni-
kayi, idan mazansu sun mutu, sun bar su, domin
ana yi musu kallon "gawa", wato sun mace a
duniya, ba su da sauran jin dadin duniya. Mata da
suka shiga cikin irin wannan yanayi ba su kwalliya, ba su ma ko cin
abinci, mai kyau, ko mai dadi, sai
wanda aka zabar musu. Ba a hulda da su balle a
aure su. Sai dai dangin mijin maza su dinga yi musu
fyade (shige), idan suka ki ba su hadin kai sai a
kore su daga gidan. A halin yanzu mafi yawansu
suna gudun hijira zuwa wuraren ibada irin nasu, inda a can kadai suke
samu dan sauki. Haka kuma
a wancan lokaci a kasar Hindu akan yi matar iyali
wato idan da namiji goma ko kusa da haka a gida,
sai su dauko mace daya a matsayin matarsu su
duka.
Irin wannan ko makamancin haka ya faru a kasar Girkawa, inda aka dauki
mace tamkar dabba. Ana
iya kama ta a yanka kamar yadda ake yanka dabba
duk lokacin aka ga dama a matsayin horo. Misali
idan mace ta kuskura ta haihu ba a lokacin da ya
kamata ta haihu ba, ko ta rinka haihuwar 'ya'ya
mata zalla, to za a yanka ta. Idan kuwa ta rinka haihuwar 'ya'ya maza
kawai, to sai a rinka daukar
ta ana kai wa baye ga shahararrun baraden kasar,
kamar yadda ake kai dabba, wai don ta haihu
'ya'ya su biyo baraden a sami zaruman da za su
rinka yi wa kasa yaki.
A kasar Sin kuwa mace ita ce kasa da kowa wajen daraja, ko wajen cin
abinci ba a ba mata, sai an
tabbatar maza sun koshi. Haka ma waje bada
magani, amma kuma matan ne aka fi tura wa wajen
neman abinci.
A nahiyar Afrika ma haka lamarin ya kasance,
domin a nan ma maza ke jan ragamar al'umma a cikin kowane irin lamari.
Mace kuwa ba ta ma san
kanta ba balle ta sami bakin fada a ji cikin al'umma.
An dauki mata tamkar shanu, sai dai a debe su
zuwa gona ko nemo itace. Saboda raunin da ake
gani ga mata a kasar shi ya sa tun kafin su karbi
kowane addini suna da al'adar aure, wanda suke yi domin mace ta sami
galihu irin na maza wanda ake
ganin idan ba shi, tana iya fadawa cikin garari. Sai
dai wannan galihun da namiji ke ba mace yana da
tsada. Domin kuwa duk ita take aikin wahala,
kamar zuwa gona, nemo itace, dafa abinci, kula da
yara da dabbobi da kuma ayyukan gayya. A kasar Hausa da alama ba ta
canza zane ba, haka
aka dauki mata, har wata karin magana Hausawa
ke yi wanda suke cewa wai "namiji dutse, mace
sakaina", wannan maganar ta kara tabbatar da
matsalar jinsi kamar yadda Babba (1986) ta
bayyana. Kuma wannan ne ya kara dakushe armashin da ake ganin matan
Hausawa na da shi,
domin su ma kan su sun dauka cewa ba su iya yin
komi sai yadda jinsin ya tanada. Irin wannan
tunanin shi ya ne ya jawo koma bayan mata a cikin
al'ummar Hausawa. Haka kuma wannan ne ya sa
Hausawa suka fi kwadayin haihuwa 'ya'ya maza bisa ga mata. Har ya kai
ma aure na iya mutuwa
idan mace ba ta haihuwar 'ya'ya maza, wai babu
magaji.
Ko a addinin da suka yi tashe a duniya an sama irn
wannan tunani. Addinin Kirista na daya daga cikin
su. Domin kuwa a bisa tsarin addinin da kuma littafin da suke bi, cewa
ya yi mace ita ce uwar
zunubi, wadda ta yi dalilin fitar Annabi Adam daga
aljanna. Haka kuwa wannan addinin (na Kirista) ya
hana wa mace 'yanci kai da zarar ta yi aure, ba a
kiranta da sunanta ballantana na mahaifinta sai dai
na miji. A wani taro na Kiristoci da aka taba yi a shekarar 1856 domin
a gano mace 'yar Adam ce
ko dabba, bayan an tattauna sosai an yarda cewa
mace 'yar Adam ce, amma wadda aka halitta domin
ta bauta wa namiji. Haka kuma an sake yin wani
taro a zamanin Daular Romawa domin a gane ko
mace na da ruhi kuma ana iya sanar da ita addini. Haka dai al'amarin
mata ya kasance a mafi yawan
al'ummomin duniya, kafin zuwan addinin
Musulunci. Kuma addinin Musulunci shi ne ya
kwato wa mace "yancinta kamar yadda za mu gani
nan gaba.
MATA A CIKIN ADDININ MUSULUNCI Addinin musulunci ya 'yantar da mata daga
kukumin da dan Adam ya sa musu tun shekaru
aru-aru da suka gabata. Addinin ne ya ba mata
dama da matsayin daidai da na maza a cikin mafi
yawan al'amurra. Misali a cikin Alkur'ani mai tsarki,
Allah (S.W.T) yana cewa: "Mun halicci mutane daga namiji da mace".(Hujrat
:13)
A wata sura kuma ya ce:
"Wanda ya yi kyakkyawan aiki namji ko mace alhali
shi yana mumuni, to lalle za mu raya shi rayuwa mai
tsarki, kuma za mu saka musu ladarsu da mafi kyau abin da suka kasance
suna aikatawa" (Nahl : 97)
Da kuma inda ya ce:
"Domin Allah ya azabantar da munafukai maza, da
munafikai mata, da mushirikai maza da mushirikai
mata. Ya kuma karbi tubar muminai maza da
muminai mata. Allah kuwa ya kasance mai gafara ne, mai jin kai"(Al-ahzab:73).
Duk wadannan ayoyin suna nuna cewa ubangiji da
kansa bai bambanta mace da namiji ba, domin duk
inda ya ambaci maza sai ya ambaci mata. Haka
kuma a wajen sakayya yana saka wa kowa da abin
da ya aikata ba wani bambanci. Haka kuma Musulunci ya ba mace wasu hakkoki da
aka danne a sakamakon al'adu da kuma zalunci
irin wanda aka saba wa mata tun a zamanin
jahiliyya. Misali a can da mace ba ta da iko a kan
abin da ta mallaka sai dai mijinta. Haka kuma ba ta
gado sai dai a gaje ta, ita kashin kanta da abin da ta mallaka, amma
Allah (S.W.T) ya ce:
"Maza suna da rabo daga abin da suka tsirfata
(abin da suka nema domin amfanin kan su). Mata
ma suna da rabo daga abin da suka tsirfata.":32).
Game da gado kuma ayar farko da Allah (S.W.T) ya
fara saukarwa cewa ya yi: "Maza suna da rabo daga abin da iyaye biyu da
makusanta dangi suka bari, kuma mata suna da
rabo daga abin da ya karanta daga gare shi ko
kuwa ya yi yawa, a rabo yankakke."(4: 7).
Wannan ayar ta nuna muna cewa mace tana da
hakki gadon iyayenta da mijinta da 'ya'yanta da kuma 'yan uwan
haihuwarta, idan ba su haihu ba.
Bayan wannan kuma Musulunci ya ceto rayuwar
mace, ya ba ta damar rayuwa cikin al'umma tamkar
namiji, domin ya hana a bizne ta da rai. Inda Allah
(S.W.T) ke cewa:
"Kuma idan aka yi wa dayansu albishir da ('ya) mace sai fuskarsa ta yi
murtuk yana cike da
tsananin bakin ciki. Ya buya daga (idon) mutane
saboda mummunan abin da aka yi masa albishir da
shi. Shin zai riki ne a wulakance ko kuma zai binne
shi ne a cikin kasa, Na'am abin da suka hukunta
kam ya munana."(Nahl 58:59). Bagu da kari kuma addinin Musulunci ya ba mace
damar neman ilmi kamar yadda ya ba namiji. Akwai
hadisin Manzo (S.A.W) da ke cewa:
"Neman ilmi wajibi ne a kan kowane musulmi da
musulma. (Bukhari).
Mace ita ce kashin bayan al'umma, idan ta gyaru to al'ummar ta gyaru,
idan kuma ta lalace to al'ummar
za ta lalace."(Hadisi Nisa'i).
Haka kuma, Annabi (S.A.W) ya ce,
"Idan ka ilmantar da mace daya tamkar ka ilmantar
da al'umma ne ga baki daya". (Bukhari)
A nan mun ga Musulunci ya karfafa ilmin mata fiye da na maza domin
ganin cewa mace ita ke kula da
tarbiyar yaro, idan ba ta samu ilmi ba, ba za ta iya
tarbiyartar da 'ya'yanta ba balle su girma su gina
al'umma ta gari.
MATA A WANNAN ZAMANI
Da yake mun ga yadda ake kallon mata a wasu nahiyoyi tun a zamanin
jahiliyya da sauran lokuttan
da suka shige da kuma ceton da Musulunci ya yi wa
mata. Sai kuma mu leka yadda ake kallon su cikin
wannan zamani, musamman daga karni na sha-
tara zuwa na ashirin da daya. Daga abin da wannan
binciken ya samo dangane da matsalolin mata da yadda ake kallon su, a
iya cewa har yau da sauran
rina a kaba. Har yanzu al'adar nan ta daukar mata a
matsayin 'yan baya ga dangi tana nan sake cikin
zukatan al`umma duk kuwa da juyin da Musulunci
ya kawo da kuma canjin zamani. Domin ko a
kasashen Turai masu ikirarin ci gaba da wayewar kai, inda kuma ake ta
hayaniya kan 'yancin mata
har yanzu matsayin mace na mai rauni akan
kowane sha'ani, yana nan. Mata suna fuskantar
matsaloli da dama ta bangaren ilmi da siyasa da
fasaha da aure da aikin gwamnati da sauran su, a
ko'ina cikin duniya. Alal misali idan muka dauki bangaren ilmi wanda
shi ne mabudin arziki na
duniya da lahira, ta hanyarsa ne mutum ke fita
duhun jahilci, ya san addini da sauran al'amurran
rayuwar duniya. Da ilmi ne mutum ke iya samun
babban matsayi a cikin aikin gwamnati. Haka kuma
da ilmi mace za ta san kanta, har ta sami damar bada gudummawa a cikin
al'umma. Amma a mafi
yawan kasashe, musamman masu tasowa, mata ne
a baya, wajen samun ilmi. Misali a wata kididdigar
yawan jama'a da aka gabatar, an gano cewa a
kasashe Sin da Bangaladash yawan mazan da ke
da ilmi ya ribanya na mata sau uku. A Afirka kuwa matan da ke da ilmi
kalilan ne, kuma mafi yawanci
ilmin nasu ba mai zurfi ne ba33, Umar (1990).
A wata kididdiga ta "UNESCO" a shekarar 2000
yawan matan da ke cikin jahilci sai kara hauhawa
yake yi. Mangwat da Abama (1999) sun nuna cewa
a shekarar 1958 yawan mata marasa ilmi ya kai kashi hamsin da takwas
bisa dari, sai kuma kara
hauhawa da ya yi ta yadda a shekarar 1985 inda
yawan mata marasa ilmi ya kai miliyan 133. Har wa
yau wata kididdiga ta "UNESCO" ta karshen karni na
ashirin ta nuna cewa daga cikin yaran da suka
shiga makaranta a Nijeriya, kashi talatin da uku ne mata, sauran duk
maza ne. Saboda matan ko da
sun shiga akan janye su daga baya, saboda wasu
dalilai da masana da manazarta suka sha
bayyanawa.
A Arewacin Nijeriya ma tun kafin da bayan zuwan
turawan mulkin mallaka an maida mata baya a fagen ilmi. Domin ko da
Turawa suka ci Sakkwato
da yaki suka kwace mulki da karfi sun sami mata
masu ilmi da yawa wadanda suka gaji su Nana
Asma'u da 'yanuwanta da kuma takwarorinta,
wadanda suka yi ilmin addinin musulunci, suka
kuma yi rubuce-rubuce cikin harsunan Larabci, Fulfulde da kuma Hausa
don fadakar da al'umma,
ciki har da rubutatatun wakoki. Amma sai Turawa
suka yi biris da sha'anin ilmin mata har sai bayan
lokaci mai tsawo, a farkon karni na 20 da suka
bude makarantar maza a Kano ba su bude ta mata
irinta ba sai a shekarar 1933. Haka kuma Mulkin mallaka ya raunanar da
makarantun allo da ya iske.
Wannan ba karamin ci baya ya janyo wa Arewa ba
domi mata su ne asasin gyaran al'umma da son ci
gaba da samun ilmin addini kamar yadda aka
dauko a karni na 19. Da an yi hakan da alam aka
ba su ilmin zamani a lokacin da ya dace su same shi da Arewa ba ta
tsinci kanta a sahun 'yan baya ga
dangi ba a fagen ilmi da ci gaban al'umma. Daga
baya da aka sami makarantu don mata kuwa sai
aka yi rashin sa'a da cewa mutane na dari-dari da
ilmin boko, saboda addini da akidun wadanda
suka kawo shi. Dangane da wanna ga abin da Babba (1986) ke cewa :
iyaye na hana yaransu
mata karatu, domin kada su rasa miji. Saboda
al'umma, musamman ta Hausawa sun dauki cewa
boko ke sa yarinya ta hinjire wa mijin, saboda za ta
dauki kanta tana da wani matsayi cikin al'umma
tun da tana da ilmi, alhali kuwa a zahiri ba haka abin yake ba. Domin
mata da suka yi ilmi, su ne za a
same su masu tsabta da sanin ya kamata. Ga sanin
addini da kuma iya biyayya ga miji, ta hanyar kula
da shi da 'ya'yansa da kuma kayansa.
Haka kuma Congleton (1988) a cikin wata hira da
aka yi da shi, ya yi bayanin cewa, mutanen Arewacin Nijeria sun fi ba
wa tarbiyar da yaro ke
samu a gida muhimmanci a kan wadda za a ba shi a
makaranta. Har suna ganin cewa ana gurbata wa
yaransu, musamman mata tarbiya idan suka bar su
suka yi zurfi a cikin makaranta. Wanda kuma a dalili
haka maza ba su cika son su auri mata masu ilmi sosai ba. Babban
dalili kuwa bai wuce na akidar
nan ta cewa mace ta bi miji sau da kafa, ko da kuwa
yin haka din zai jawo mata cikas a rayuwarta. Suna
ganin cewa mace mai ilmi ta san hakkinta a kan miji
da kuma san hakkin miji a kan ta, ba za ta yarda a
tauye ta ba a cikin gida kamar dabba, ba kulawa ba wani abin yi.
Azare (2000) cewa ya yi babban dalili da ke sa ana
hana ko janye mata daga makaranta, shi ne rashin
isasshen kudin da za a dauki dawainiyar karatun
duka 'yaya, maza da mata ga baki daya, kuma
gudun lalacewar tarbiyarsu, wadda al'adar al'ummarsu ta tanadar musu.
Amma kuma sai abin
ya zan "an ki cin biri, an ci dila", domin sai a hana su
makaranta amma a tura su wajen kwadago ko
tallace-tallace, inda suke shiga cikin hadurra kala-
kala, kamar yin cikin shege ko kamuwa da cutar
kanjamau . Idan muka dubi matsalar ta fuskar siyasa kuma za
mu ga cewa a wannan fagen maza ne suka yi
kaka-gida, domin a yawanci kasashen duniya ba a
ba mata damar da ta kamance su a sha'anin siyasa
ballantana a ce su kai ga taka rawar gani a cikin
sha'anin mulki, Ashford (1995:17) ta yi bayanin cewa ana dai babatun
dimokuradiyya ne a baki
kawai, amma ayyanawar ba haka take ba. Da kyar
ne mace take kai ga shiga takarar mukamin siyasa.
Idan kuma ta samu shiga din, za ta fuskanci
tarnakin al'ada, wanda ke iya hana al'umma ta zabe
ta. Saboda idan aka dubi siyasar duniya a yau, mata irin su Margaret
Thacher ta Ingila, da Indira Ghandi
ta Indiya, da Komaratonga ta Sirilanka, da Benezir
Bhuto a Pakistan da wasu kalilan kadai ne
wadanda suka taba samun nasarar zama
zababbun shugabanin kasashe, wanda yake idan
aka kwatanta su da maza da suka taba shugabanci ba su kai ko kashi
biyar bisa dari ba. Haka kuma a
mafi yawan kasashe masu tasowa, musamman irin
su Mexico da Brazil da yawancin na nahiyar Afrika,
kujerin da ake ba mata a majilisar dokokin kasa ba
su taka kara sun karya ba. Har ma a kasashen da
suka ci gaba idan aka kwatanta maza da ke rike da mukamin siyasa da na
mata, za a sami bambanci
mai yawan gaske. A Arewanci Najeriya abin ma ya
fi muni, domin al'umma sun dauki cewa mata
karuwai kawai ke yin siyasa.
A lokacin da muka dubi matsalar shugabanci sai a
ga cewa a cikin matan da suka yi ilmi, kalilan ne ke samun yin aikin
gwamnati. Wadanda kuma suka
sami aikin, sukan fuskanci matsaloli ta fuskoki da
yawa. A kasashen duniya da yawa, har da
wadanda suka ci gaba, a kan nuna wa mata
bambanci ta fuskar matsayi ko makami da awoyin
aiki. Haka kuma akan nuna musu bambanci wajen biyan ladar aiki. A
kasar Amurka ga misali, Riley
(1997) ta yi bayanin akan tauye 'yancin mata ta
fuskar mayar da su saniyar ware a fagen siyasa. Ta
kai ga har shata wani tsari aka yi wanda yake
tabbatar da cewa matan da suke aikin gwamnati
ko na manyan kamfuna ba su rika manyan mukamai ba, wanda ya sa
bambanci tsakanin mata
da maza ya dade kafin a kawar da shi a kasar. Ta
kara da cewa ta kai ma ga albashin namiji ya fi na
mace yawa ko da kuwa aikinsu iri daya ne.
Wannan bambancin kuma ya kasance har a
kasashen Ingila da Kanada da kuma Siriya. Wannan akidar ba a can kadai
ta tsaya ba, ko a nahiyar
Afrika da kasar Nijeriya, har ma Arewa, mata sun
kasance a matsayin saniyar ware a fagen siyasa,
domin matan Arewa ba su fara ko jefa kuri`a ba sai
1976, ballantana su shiga takara a zabe su,
Dityavyar(1998;145). Matan da ke aiki ma ana yi musu kallon wasu
tsiraru ne, wadanda suka fi
karfin mazajensu a cikin al'umma. A wajen aikin
kuwa akwai mukaman da ake ganin cewa mata ba
su isa su rika su ba sai dai maza.
A fagen tattalin arziki mata na bakin kokarinsu,
domin kamar yadda Osunde and Imorayi (1999) suka bayyana, mata na yin
ayyuka da dama
wadanda ke taimaka wa wajen habaka arzikin
al'umma. Inda suka bada misalin cewa, mata na
noma, kiwo da kuma sana'oin hannu irin su saka,
har ma da fatauci, suna kuma yin ayyukan gayya.
Ita ma Riley (1997) ta yi bayani cewa A kasar Sin 'ya'ya mata ne ake
turawa gona ko wajen ga aiki,
domin su nemo wa iyaye da sauran 'yan uwansa
da suka hada da maza abin masarufi. Haka kuma
sanannen abu ne cewa a kasar Indiya mace ke
neman kudin biyan sadakin aurenta. A nahiyar
Afrika, har a arewacin Nijeriya mata na kokarin neman na kai. Inda
suke yin duk abubuwan da
aka ambata a sama, har ma da kari, domin sukan yi
`yan sana`oin hannu, suna dora wa 'yayansu
tallace-tallace, su kuma suna can suna yin wasu
sana'a wadanda suka hada har da kitso, dinki, da
sayar da abinci a wurare daban-daban. Mack (1992) ta yi bayanin har da
cinikin bayi matan
kasar Hausa suna yi a zamani da ake yin sa. Amma
abin mamaki shi ne duk da wannan gagarumar
gudumawar da mata ke bayarwa ta fannin tattalin
arziki, al'umma na ci gaba da yi musu kallon cima-
kwance wadanda komi sai an nemo an ba su. A yanayin zamantakewa na yau
da kullum, mata su
ne kashin bayan zaman lafiya da mu'amala mai
kyau cikin al'umma. Domin su ne aka fi sani da
kokarin sada zumunta da hulda da makwabta da
tarbiyar yara da kuma yin 'yan sana'o'in hannu,
masu taimakawa wajen gudanar da rayuwa cikin sauki. Haka kuma tarihi
ya nuna mata suna da
tausayi da kokari wajen kula da marasa lafiya,
musamman a zamanin da ake yawan yake-yake.
Ko a nan kusa lokacin jihadin su Shehu Usman
Danfodiyo, Boyd (1989) ta yi bayani akan irin
gudumawar da su Nana Asma'u da sauran matan zamaninta suka bayar, ta
hanyar kula da wadanda
aka ji wa rauni da kuma bada abinci da daukar
kaya da kula da yara lokacin yaki. A wannan
zamani da ake ciki mata na gudanar da kusan duk
abin da maza ke yi a kowane bangare na rayuwa
idan dai an ba su dama. A harkar aure mata suna samun matsaloli a ko ina
ciki duniya. Sai dai bayanin da zan yi a nan shi ne a
kan matan arewacin Najeriya, inda har yanzu a kan
yi wa yarinya aure ba tare da an nemi yardar ta ba,
kuma a nemi ta zauna da mijin nan bisa ga ladabi
da biyayya ko da kuwa ba ta son sa. A wani bayani na Callway and
Greevey (1994:84) cewa suka yi:
"A kasar Hausa ana yi wa yarinya auren wuri, kuma
zaba mata mijin ake yi (ba tare da yardarta ba)
kuma dole ta zauna da shi, ta bi shi sau da kafa, ta
kuma zauna tare da kishiyoyi, ko tana so, ko ba ta
so". Wannan auren da ake yi musu, na wuri yakan jawo
musu matsaloli iri-iri, musamman idan suka yi
saurin daukar ciki idan an zo wurin haihuwa, mafi
yawa yaran da ba su yi kwarin haihuwa ba, sukan
sami matsalar yoyon fitsari. Inda kuma daga
karshen mazan ke juya musu baya, sai dai iyayensu su yi ta wahala da
su. Wannan kuma ba a kasar
Hausa kawai yake faruwa ba, yana faruwa a
yawanci kasashe masu tasowa. Misali a kasar
Somaliya, musamman sai da wata baturiya ta kafa
asibitin taimakon irin wadannan mata da ke samun
matsalar yankan gishiri, kuma al'umma ta juya musu baya48.
MATA DA ADABIN BAKA
Shahararrun masana da yawa wadanda suka yi
rubuce-rubuce a tarihi da al'adun kasar Hausa,
kamar Clapperton da Lander (1829), da Jeroma
(1970,1972,1973), da Joseph (1973), da Palmer (1978) da Mark (1985) da
Boyd (1989) da Hill
(1972), da sauransu, duk sun yi bayanin cewa
kafin zuwan baki a kasar Hausa, matan Hausawa
sun kasance masu taka muhimmiyar rawa wajen
ciyar da kasar da al'ummarsu gaba. Irin wannan
rawa tasu ta shafi bangaren tattalin arziki da siyasa, tarbiya da
fasaha da kuma ciyar da harshen Hausa
gaba, ta hanyar tatsuniyoyi da labarai da kacici-
kacici da karin magana da salon magana da badda-
bami da sauran su. Wadannan suna cikin
abubuwan da Fafunwa (1982) ya kira makarantun
farko na 'yan Afirika kafin su sami ilmin karatu da rubutu. Amma kuma
idan aka tashi bayani game da
irin wannan ci gaba sai ya zan gudummuwar maza
kadai ke fice.
Haka dai al'amarin mata ya kasance rayuwarsu na
cikin tawaya da rashin walwala wanda ba kome ya
hassada masu shi ba sai al'adu, wadanda ke ci da yawun addinai da
siyasa domin biyan bukatun
wani jinsin da ba mace ba. Wadanna al'adun sun yi
tasiri sosai cikin al'ummomi musamman a nahiyar
Afirika yadda har su ma matan an dasa wannan
akida ta namiji dutse, mace sakaina, har ya zan ba
su iya kalubalantar matsalolin da ke tattare da su, Remi(2003). Sai a
'yan shekarun baya –bayan nan
da aka sami mata kalilian masu matsawa, suka
tunkari wannan matsalar ta danniyar jinsin mata, ta
hanyoyi daban –daban.
MATA DA RUBUTACCEN ADABIN HAUSA
Daga abin da muka ga a sama mun fahimci abubuwa da dama. Da farko dai
matsalar nazari da
sharhi game da mata ba ta wuce irin mizanin da aka
dora batun ba, ko a adinance ko siyasance ko
kuma tafuskar ilmi da zamantakewa. Na biyu kuwa
shi ne duk da cewa an yarda mata na taka rawa a
gnuwar rayuwa ta kowace irin fuska, da alama akwai wadansu katangai da
ake jefawa a gabansu
domin kada su kai ga gaci.Na uku ga alama, yadda
ake kallon mata a kowane fage da irin rawar da
suke takawa da matsalolin da suke fuskanta su ne
suka yi katutu ko da a fagen nazarin ayyukan
adabin Hausawa. An fadi haka ne ganin cewa mata kamar
takwarorinsu maza su ma sun samu ilmin karatu da
rubutu bayan zuwan addinin Musulunci. Amma
duk da cewa Musulunci ya wajabta neman ilmi,
musamman na addini a kan kowane musulmi,
namiji ko mace, tarihi ya nuna cewa a kasar Hausa al'umma ta yi watsi
da sha'anin ilmin mata, wanda
shi ne ya haifar da barin mata cikin jahilci. Wannan
ya sa mata suka kasance tamkar dabbobi cikin
duhun jahilci. Abin da al'umma ta tanadar musu shi
ne aikin zaman gida. Da yake kuma rubutaccen
adabi ba ya samuwa sai da karatu da rubutu, dole rawar mata a wannan
fage ta takaita.
Rawa ba ta canza ba sosai, sai lokacin jihadin su
Shehu Danfodiyo da magoya bayansa, a karni na
19, Inda Shehu ya lura da wannan matsalar ya
kuma tashi tsaye domin kawar da ita. Ga abin da
Shehu ke cewa game da matan kasar Hausa a wancan lokaci:
Maza sun dauki matansu tamkar wasu rubabbun
kayan gida, wadanda aka gama amfani da su, sai
yar a shara. Kash wannan hali ya saba wa ka'ida.
Yaya za su bar su cikin duhun kai, bayan ga shi
kuwa suna ba dalibansu sani a waje." Shehu ya ci gaba da cewa fadar
nan ta Hausawa
mai cewa "aljannar mace tana karkashin kafafun
mijinta", ba ta da wani tasiri sai idan mace ta bauta
wa Allah yadda ya kamata. Bauta wa Allah ba ta
inganta sai da ilmin addinin Musulunci.
Wannan ne ya malamai da magidanta da 'yan uwan Shehu da kuma `ya`yansu
duk sun karbi kiran da
ya yi. Nan da nan sai makarantu suka budu a
gidajen mutanen da sassa a can cikin gidaje wurin
mata. Mafi yawan matan malamai suka zama
malamai su kansu. Alal misali matan Shehu da
'yanyansa da sarakunansa, kamar su Hadiza, Asma'u, 'yayan Shehu da
A'ishatu matar Aliyu Jedo,
da Maryam da Fatima, matan Sarkin Musulmi Bello
da Maryam 'Yar Shehu duk sun bude azuzuwan
karatun allo a cikin gidajen mazansu. Idan an
manta da rawar da wadannan suka taka to da kyar
ne za mu manta da rawar da Nana Asma'u ta taka. Dubi Boyd (1989),
wadda ta kawo bayanin `yan
taru, wadanda suka samo asali daga shirin ba mata
ilmi na Nana Asma'u. Haka kuma duk wadannan
mata sun yi rubuce-rubuce da suka hada har da
wakoki. A kan abubuwan da suka shafi rayuwar
al'umma dangane da addinin musulunci, Boyd (1989) ta yi bayanin cewa
Nana Asma'u kadai ta
rubuta wakoki da dama, amma kuma duk
wadannan ayyukan da mata suka yi, saboda su
mata ne, sai wannan ya kasance musu tarnaki
wajen yin fice da kuma samun shiga cikin
mashahuran marubuta. Ko Nana Asma'u idan ba domin bincike-binciken
Boyd da wasu ba da har
yanzu mutane da dama ba san irin gudumawar da
ta bayar ba. Domin ita Boyd ce ta yi kokarin binciko
wadannan ayyukan ta kuma buga cikin littattafai
da mujallu daban-daban. Amma kuma har yanzu
mutane kalilan ne a cikin wannan al`umma suka san ayyukanta. Wannan
dabi'ar ta rashin ba aiki
mata muhimmaci ba wai a ciki al'ummar Hausawa
kadai take ba, har ma da sauran al'ummomin
duniya. Misali kasar Ingila, tun a shekarar 1866
wata marubuciya mai suna Anne Evans ta yi rubutu
a kan matsalar mata, ta ce 'mace ba ta da zabi… sai dai ta dogara ga
duk abin da ta samu ko ya same
ta. Ta kuma tsaya iya dan matsayinta". Babban abin
takaici a nan shi ne ita wannan mata sai da ta lika
wa kanta sunan namiji wato "George Elliant' kafin
rubutunta ya sami karbuwa ga al'umma. Haka
kuma idan muka koma ga tarihi, za mu ga cewa daga cikin shahararrun
marubuta da suka yi suna a
duniya, wadanda aka yi ta nazarce-nazarce a kan
ayyukansu, da kyar ne idan za a sami mace. Misali
mun ga an yayata su Plato da Aristottle da
Shakesphere da Milton da Chaucer da Samuel
Johnson da T.S. Elliot da sauran su. Amma ba a damu da shahararrun
marubuta mata ba irin su
Austen da Broute, Woolf da Hurston da sauran su a
duniyar Turai da Amurka, ba domin komi ba sai
don suna mata.
Idan har hakan ya kasance dangane da su Nana
Asma'u da dangoginta a zamanin masu jihadi, ba abin mamaki ba ne idan
ba a ba mabiyansu wani
muhimmanci ba, duk kuwa da cewa an samar da
mata mashahurai da suka tashe a wannan fage.
Faga cikin irin wadannann an ci gaba da samun
mata da suka ci gaba da yin rubuce-rubuce cikin
Hausa da sauran harsunan Arewacin Nijeriya,musamman a fannin rubutattun wakoki
domin su ne suka fi saukin hardacewa ga matan da
ke daukar karatu da kuma dadin saurare ga
sauran jama'a. Amma saboda matsalar wariyar jinsi
da tarnakin al'adu wanda ya tauye mata ga samun
shawarwari daga kwararru game da rubuce- rubucen da kuma gudun
korafe-korafe a cikin
al'umma, sai aka kara samun dakushe aikace-
aikacen mata na rubutaccen adabin Hausa. Idan
kuma aka dubi bangaren maza ba haka abin yake
ba.
A halin yanzu ambaton Akilu Aliyu da Aliyu Namangi ko Abubakar Imam ko
Yusufu Kantu ko
Alkali Haliru Wurno ko Bello Kagara da dimbin
mazan da suka yi rubuce-rubucen cikin adabin
Hausa a shekarun baya, sai ka taras an san su. To
amma matan fa? Kodayake akwai su ba a ba su
damar fitowa su yayata kansu ba, ba a kuma taimaka aka yayata su ba.
Ko 'yan wadanda suka yi
fice, ba da yawun bakin maza suka yi shi ba. Domin
mata ne 'yan uwansu, suka yi kokarin da suka fito
da su. Wato mata irin su Baturiya Beverly Mark da ta
yi kokarin buga littafin "Alkalami a Hannun
Mata" (1983),wanda yake dauke da rubutattun wakoki na wasu mata a
Kano, wato Hajiya Hauwa
Gwaram da Hajiya 'Yar Shehu. Sai kuma Gambo U.
Babba, wadda ta rubuta kundin digirin farko a
Jami'ar Ahmadu Bello Zariya, a kan wata malama
marubuciya a1986, wato Hajiya Hasana Sufi, sauran
matan da aka ji sunansu kuwa, su ne suka yi kokarin rubuta labaransu,
suka kuma buga abin su
da kan su. Wato irin Hafsat Abdulwaheed (1980)
da Yaya Hasana Umar (1980) da kuma marubutan
zamani, wato irin su Bilkisu Funtuwa da Balaraba
Ramat da Zuwaira Isah da sauran su. Inda kila za a
ga wannan aiki ya kankama shi ne littafin Ibrahim Yaro Yahaya
(1988),wato Hausa a Rubuce, shi ma
rubuce-rubucen maza ya fi yawa, kila saboda
rubuce-rubucen mazan ne ya fi yawa, ga abin da
yake cewa game da wannan batu:
Mata su ma ba a bar su a baya ba wajen ciyar da ilmi
gaba ta yin rubuce-rubuce da ajami ko boko, a buga a littattafai.
Harsashin da nana Asma'u 'yar
Shehu da Maryama 'yar Shehu suka aza a kan ilmin
mata ya samu kafuwa sosai, har ma ana ta dora gini
a kansa tun daga wancan karni har zuwa wannan
zamani namu, domin ana samun mata a ko'ina a
kasar Hausa suna neman ilmi a makarantun allo da na Islamiyya da ilmin
zamani ma. Wasu daga
cikinsu in an yi musu aure, suna gudanar da
azuzuwan koyarwa a gidajen mazajensu.
Akwai mata da dama irin wadanda Yahaya (1988)
ya ambata, wadanda suka nemi ilmi har suka zama
malamai, kuma marubuta cikin ajami da boko. Haka kuma rubuce-rubucen
nasu sun tabo fannoni da
dama, sai dai saboda kasancewar mafi yawansa
matan aure ne ko kuma 'yan matan da ke
karkashin kulawar iyayensu ba su da damar zuwa
wasu wurare don nuna fasaharsu, kamar yadda
maza ke samun yi, ya sa ba a san da zaman mafi yawansu ba, wannan
matsalar ta fi shafuwar
marubuta wakoki, kila shi ya sa mazan suka fi
tashe fiye da matan. Lallai akwai marubuta mata
kamar yadda aka sha fada, amma ga nawa tunanin
ba wai fadar cewa akwai matan ne kawai da ke
rubuce-rubucen ajami ke da muhimmanci ba, a'a, a ga ayyukan nasu a
zahiri. Wannan shi ne kashin
bayan wannan tunani, a nemo matan marubuta
wakoki da kagaggun labarai da kuma wasan
kwaikwayo, domin kafa hujja ta fasalce-fasalcen
ayyukan adabi na mata a kasar Hausa. Ta haka ne
za a ga irin rawar da suka ko suke ko za su bayarwa a raya kasa da al'umma.

SABANI GAME DA WASU KA'IDOJIN RUBUTUN HAUSA.

DAGA Nasir G Ahmad, ZUWA GA FARFESA
MALUMFASHI:
Kamar yadda aka ba da shawara, za mu so jin
ra'ayin Malam, da ma sauran malamai kan sabanin da ke akwai a halin
yanzu game da wani bangare
na ka'idojin rubutun Hausa, musamman 'yar
mallaka da zagagen aikatau na lokaci mai ci.
Yayin da mu daliban Hausa muka kankame abin da
ke rubuce cikin littafai dangane da wadannan
ka'idoji muke hadewa mu rubuta: GIDANMU, GUDUMMAWARMU, AYYUKANMU;
akwai ra'ayi na
biyu (Darikar Malam Sheme) da ke cewa raba 'yar
mallakar da kalmar abin da aka mallaka za a yi,
wato a rubuta, GIDAN MU, GUDUMMAWAR MU,
AYYUKAN MU.
Haka nan akwai masu raba zagagen aikatau na lokaci mai ci, wato suna
rubuta TA NA, MU NA, KA
NA, KI KE, YA KE, SU KE, ds., maimakon hade su da
mu muke yi.
*Ina jin zafin wannan sabani da ke akwai, domin
zai raba hankalin matasan marubuta, su rasa
wanne za su dauka, ko kuma abin ya zama "Hamiyya," wato ya zamo mutum
na zabar ra'ayi
kaza ne, saboda shi wane ke bi, don haka shi ne
dai dai.
*Mene ne mafita game da wannan sabani?
*** *** ***
Malumfashi Ibrahim: "Salamu alykum. Ina jin kamar an amsa tambayar
ma kafin ni na shigo. Aminu Garba Ingawa ya ce;
mafita a nan Malam ita ce: shehunan Malaman da
muke da su su yi zama na musamman don samar
mana mafita kan wannan matsalar. Hauwa Lawan
Maiturare kuma ta ce, shawarar Aminu ita ce abin bi, domin kuwa
ba'arin malamai tun daga
sakandare zuwa jami'o'i har yau suna koyarda
had'e mallaka ne, memakon raba su, amma idan
aka shirya zama aka buga masa stamfi sai ya zama
kar'ba'b'be bai d'aya, memakon wannan nabin
d'arik'ar wane, wance na bin ta wance. Ni na kara da cewa harkar
dabbaka ka'idojin
rubutu a kowane harshe na duniya a fagen nazarin
kimiyyar harshe yake shimfide, ba adabi ko al'ada
ko wani abu makamancinsa ba, duk kuwa da cewa
masana kimiyyar harshen ba sa aiwatar da komi sai
sun yi la'akari da adabi da al'adu da addini da sauran ire-iren su
wajen kai ga matsaya.
Ba wani abu ya sa haka ba, sai ganin cewa dukkan
ka'idojin suna tafiya da ginuwar nahawun harshe;
shi ya sa za ka ji ana maganar DOGUWA da
GAJERIYAR MALLAKA, da kuma TSIGALAU da
WAKILIN SUNA ko ZAGIN AIKATAU ko AZUZUWAN AIKATAU da LOKUTTAN HAUSA da
wasu da dama
irin su.
Wannan ne ya sa ko a fagen tsara rubutu da
ka'idojinsa ake tattaruwa da mutane mabambanta
domin a samar da matsaya. Duk wata matsala da a
yanzu ake fama da ita ta rarrabuwa da dagewa a kan wani abin da ake
gani shi ne daidai, to an bar
tsayayyar ka'ida ne an shigo da son rai ko wani
abu makamancin haka.
Alal misali, a duniyar rubutun Hausa yanzu za ka ga
ana samun takaddama kan: Ba da za a rubuta ko
Bada. Akan zo ne za a ce ko A kan zo. Bayar da ne daidai ko Bayarda.
Namu, naku, nasu ne gaskiya
ko na mu, na ku, na su. Wane ne daidai ko Wanene.
Mene ne ko kuwa Menene ko Minene, Allah ne ko
kuwa allah Allah ya ce ko kuwa Allah Ya ce.
Akwai misalai da yawan gaske da ake ta fama da
su tsakanin masana da manazarta da dalibai. A nawa tunanin ba abin da
ya jawo haka face rashin
bin diddigin yadda lamurra suke a nazarce, da
kuma rashin ilmin Rubutun Ka'idojin Rubutu da
yawancinmu ba mu da shi, sa'annan uwa-uba
rashin takarkarewa wajen koyar da wadannan
ka'idoji a makarantun Firamare da Sakandare da Kwalejoji da Jami'o'inmu.
Ba a ba wannan darasi muhimmanci ba, shi ya sa
muke wa harkar ka'idojin rubutu labarin cin
kanzon kurege. Abin da na sani shi ne, a yanzu
mutum daya ko biyu ko uku ko ma fiye ba su da
ikon canza ka'idojin da aka amince da su tsakanin masana da goyon bayan hukuma.
Muna da dama mu ki amincewa da dukkan abin da
aka taru aka amince kan sa, a matsayin 'yan tsiraru,
amma a kullum tarbacen taron masana ake aiki da
shi ba na 'yan tsirarun ba.
Saboda haka a halin yanzu MALLAKA a rubutun HAUSA a hade take, kamar
yadda malam Nasir G
Ahmad ya nuna: GIDANMU, GUDUMMAWARMU,
AYYUKANMU ake rubutawa a gajera, alhali a
doguwa GIDAN NAMU, GUDUMMAWAR TAMU,
AYYUKAN NAMU. Haka kuma TANA, MUNA, KANA,
KIKE, YAKE, SUKE, da sauransu ake rubutawa, maimakon rabawa da wasu ke yi.
Wannan ita ce tsayayya, amsassa kuma karbabbar
ka'ida. Sai in nan gaba an sake yin wani taro an
canza wadannan ka'idoji, sa'annan za mu iya
amincewa da sabon alkawari."
*** *** *** Ibrahim Sheme: "RA'AYIN "TSIRARU" KAN RABA MALLAKA.
Oh, ikon Allah! Malam ya ce: "Abin da na sani shi ne,
a yanzu mutum daya ko biyu ko uku ko ma fiye ba
su da ikon canza ka'idojin da aka amince da su
tsakanin masana da goyon bayan hukuma. Muna
da dama mu ki amincewa da dukkan abin da aka taru aka amince kan sa, a
matsayin 'yan tsiraru,
amma a kullum tarbacen taron masana ake aiki da
shi ba na 'yan tsirarun ba."
Amma na yi mamakin yadda Farfesa ya gina
kafewar sa a kan AL'ADA, wato kunne ya girmi
kaka. Ban da nuna mana cewa "haka ake yi" ko "haka mu ka gani," babu
wata kwakkwarar hujja
da ya kawo mana mai nuna dalilin da ya sa za mu
hade mallaka.
Malam bai kawo mana sabon abu ba; ai da ma mun
san cewa an ce "haka ake yi." Abin da mu ke so shi
ne: me ya sa? Don me za a yi hakan? Bisa wace hujja?
Ni, da yawa an san ni da cewa ina daga cikin tsiraru
(ko ma jagoran su) masu yekuwar lallai sai an raba
mallaka. Kuma tuni na kawo kwararan hujjoji na a
wannan dandalin na DM (koda yake na ga babu
wanda ya tuno da su, ciki kuwa har da shi Mal. Nasir).
Ni ina ganin maganar da Farfesa ya yi ta farko kafin
ya yanke hukuncin sa cikin garaje ita ce ya kamata
ya zauna a kai, wato inda ya ce:
"Ina jin kamar an amsa tambayar ma kafin ni na
shigo. Aminu Garba Ingawa ya ce; mafita a nan Malam ita ce: shehunan
Malaman da muke da su su
yi zama na musamman don samar mana mafita kan
wannan matsalar. Hauwa Lawan Maiturare kuma ta
ce, shawarar Aminu ita ce abin bi, domin kuwa
ba'arin malamai tun daga sakandare zuwa jami'o'i
har yau suna koyarda had'e mallaka ne, memakon raba su, amma idan aka
shirya zama aka buga
masa stamfi sai ya zama kar'ba'b'be bai d'aya
memakon wannan nabin d'arik'ar wane wance na
bin ta wance."
Wannan na nuna cewa har yanzu ba a yanke
hukunci kan batun nan na mallaka ba. Ba mallaka kurum ba, har ma wasu
kalmomin masu tarin
yawa. Farfesa Malumfashi ya yanke nasa a nan, ba
tare da ya kawo mana wata madogara da za mu
zauna a kai ba.
Sannan batun nan ba fa na "son rai" ba ne ko
"rashin ilmi" kamar yadda Malam ya nuna. Batu ne na nazari da bincike
inda ake kafa hujja. Ni kam ba
ni da PhD ko farfesanci, to amma ba shakka zan ja
da ko waye da zai ce ba ni da ilmi ko ba ni da sani
kan nahawu. Na karanta shi matukar karantawa, a
cikin aji (ni dalibin Farfesa Sani Zaria ne), na mallaki
littattafan nahawu, na fahimci dukkan inda duk wani masani mai cewa a
hade mallaka ya dosa.
Tuni na kasance daya daga cikin marubutan Hausa
da su ka san harshen Hausa da yadda ake rubuta
shi. Wannan ba cika baki ba ne, dahir ne.
A da can, ina bin waccan darikar ta masu cewa a
hade kalma. Littattafai na na farko-farko, irin su "Kifin Rijiya"
(1991) da bugun farko na
"'Yartsana" (2003) da duk wasu rubuce-rubuce da
na yi lokacin ina aikin jaridar Hausa (Nasiha, Rana,
Gaskiya Ta Fi Kwabo) a bisa waccan darikar na yi
su, to amma tuni kai na ya waye, na gane cewa
masana sun dulmiyar da mu cikin wannan dokar ba tare da sun ba mu dalilin su ba.
Daga nan na zama "tsiraru" ko "dan tawaye" - har
na ke jagorantar su. A cikin farin sani na sauya
sheka, ba wai duhun sani ba.
Na so a ce Malam Malumfashi ya kawo mana hujja,
misali: ga dalilin da ya sa ake hadewa, ba wai kawai a ce taron masana
ne su ka ce a yi hakan ba. Ai
mun san me su ka ce tun tuni.
Da masanan su ka taru, me su ka gindaya a
matsayin hujja? Idan an shanya mana hujjar su a
faifai, to sai mu dube ta mu gani: karbabbiya ce ko
a'a? Dalili shi ne: ilmi kogi ne. Malam ya fi ni sanin hakan.
Ina so ni da Farfesa mu zauna in jera masa hujjoji
na daki-daki (idan na kai minzalin zama da farfesa).
Na tabbatar a matsayin sa na mutum wanda ya
dade da kin karbar abu ba tare da ya ga hujja ba,
zai amince da nawa uzirin, kuma ya dawo cikin mu "tsiraru".
*** *** ***
Nasir G Ahmad:
"Allah ya ja mana da Malam (Sheme)! Ina sha'awar
irin wannan dagewa taka, amma fa ni ba zan bi
wannan sabuwar darika ba. Ga Farfesa ka fuskantar da bayananka. Duk da
haka ga ra'ayin
almajirinku:
Ka yi watsi da ijma'i, wato haduwar ra'ayin
manazarta kan hade gajerar mallaka, wannan
ra'ayinka ne. Amma ijma'i ya fi karfin a ce ba abin
dogaro ba ne. A musulunce ma, shi ne mataki na uku wajen samar da
hukunce-hukuncen shari'a.
Wanda ya bijire wa ijma'i, ya zama mu'utazili ke nan,
wato dan tawaye, kamar yadda ka ce ka yi wa
ra'ayin manazartan Hausa.
Kamar dai yadda na taba fada, zan yi amfani da
abin da nake da madogara kansa a hannuna ne. Wanda aka yi
wallafe-wallafe kansa, ake kuma kan
yi. Aka amince da amfani da shi, da koyar da shi a
dukkan matakan ilimi.
Kamar yadda kuma na taba fada, ni da nake
malamin makaranta mai koyar da dalibai Hausa da
ka'idojin rubuta ta, da wace hujja zan dogara in na ce zan sauya
alkibla rana tsaka, na nemi koyar da
dalibaina ka'idojin rubutun Hausa na sabuwar
darikar Shemiyya, alhali ga abin da ke cikin littafan
manhaja da aka umarce ni na yi amfani da su? Ba
ma ta fuskar aiki ba, ni a karan kaina, ba zan iya ba
da hujjojin da Malam ke rike da su a matsayin madogarata ba, domin ni
kaina ba su gamshe ni ba
(ta yiwu saboda karamin sanina).
Kamar yadda kuma na taba fada, ya kamata Malam
(Sheme) ya fito da wata wallafa ta littafi, ko a
matsayin makala ga irin taron masana Hausa da
akan yi, inda zai fito da wannan sabon ra'ayi nasa ga 'yan uwansa
manyan masana don tattaunawa.
Idan aka amince, aka yi ittifakin yin amfani da su,
mu dalibai ba abin da ke kanmu sai run gumar su
da fara dabbaka su a rubuce-rubucenmu. In ba
haka ba, to muna nan bisa darikar 'yan mazan jiya,
babu gudu babu ja da baya." *** *** ***
Malumfashi Ibrahim:
"Alhamdu lillah, na karanta jawabin Ibrahim
Sheme, amma kamar ya yi mani mummunar
fahimta, 'son rai' da 'rashin ilmin' da na yi magana
ba da shi nake ba, da dukkanmu nake da ke da matsala da ka'idojin
rubutun Hausa. Ba wai shi
kadai ba ne ke cikin 'tsirarun' da na yi magana, ni
ma ina ciki. Kuma na sha korafi game da haka a
wuraren tarurrukan ilimi da kara wa juna sani.
Na dade ban yarda a raba /ba da/, misali /na ba da
kudi/ ni fi yarda da a hade su, domin a tawa fahimtar /bada/
cikakkiyar kalma ce, amma in
muka raba, / ba/ na matsayinta daban da /da/ ke
nan, wato dukkansu za su iya zama da gindinsu su
bada ma'ana.
Na kuma kafa hujja da abu guda, idan muka koma
ga ita kalmar /ba/ za a ga ta samo asali ne daga / bayar/, wato misali
/na bayar da/. A bisa ka'idar
nahawu, duk inda aka yanke wani abu daga wata
kalma, abin da ke bin wannan kalmar hade shi ake
da wanda ya biyo masa, ya koma kalma guda mai
ma'ana guda. Ke nan /bayar da/ idan ka ka debe /
yar/ zai zama /ba/, ita kuma /da/ da ke biye sai ta koma ta
saje da /ba/ ya zama / bada/. Wannan shi aka koya
mana a nahawun, amma daga baya masu nazarin
nahawu suka ce, ai nan ba kalmomi yau da kullum
ba ne, kalmomin fannu ne na aikatau, kuma tun
azal bayar/ da /ba/ kalmomi biyu masu zaman kansu , wato kana iya cewa
/bayar da/ ko kuma /
ba da/, domin ita/bayar/ da /ba/ duk abu daya ne
a kalmomin fannun aikatau, aji ne kurum ya
bambanta su, ba wai gutsire / yar/ aka yi ba, ke
nan dole a bar su a rabe. Har yau a rubuce-
rubucena raba su nake yi, sai in na tuna da cewa ai an yi ittifaki,
kan rabawa sai na
gyara na koma ga wanda aka amince da shi. Ko a
aji, nakan bayyana wa dalibai rashin amincewa ta
da wasu ka'idoji da yawa, amma in mun gama
tattaunawa, tambayar da aka yi man ita ce, 'to
malam wane za mu dauka mu yi aiki da shi,' ni kuma a kullum nakan ce,
wanda aka amince da shi,
ko da kuwa bisa kuskure ne.
Saboda me? Idan aka bar harshe yana gudana bisa
son rai ko rashin sanin tushen abu, yana iya jawo
rugujewar abin da aka riga aka gina, ta yadda za a
zo a kare ba wan ba kanen. Sheme da duk wani mai irin wannan ra'ayi nasa ba
za mu taba samun galaba ba sai an kuma yin wani
taro na bitar ka'idojin, mun je wurin an kwafsa da
mu, ba mun bayar da hujjojinmu, an karba, an
buga, an watsa ga sauran al'umma, ana kuma
karantar da su don na baya su sami abin karaswa. Ba yadda za ka yi
jayayya da abin da taron
daidaitawa ya zo da su, yin haka barna zai jawo ga
harshen."

YUNKURIN 'YAN KASUWA WAJEN KAFA MULKIN DIMOKARADIYA A NIJERIYA.

Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya
+2348065025820
abuhidya3@gmail.com

GABATARWA
Wannan shi ne kundin kudiri na gamayyar tunanin kafar turakun siyasar
'yan kasuwa a jihar Kano wanda ya dunkule yadda za a gabatar da tsari
da manufofin kudirin wannan tafiya bisa aminci da yarda.

TARIHIN KASUWANCI A KANO DA ZUWAN 'YAN KASUWA LARABAWA DA WASUN SU.
Kafin bayyana waccan tsari da aka fada a sama yana da kyau a dan dubi
tarihin kasuwan a wannan babbar jiha ta Kano. A shekara ta 1453
miladiyya, a zamanin Sarkin Kano Yakubu dan Abdullahi Barja, Sarkin
Kano na goma sha shida(16)a mulkin kanawa, wadansu Larabawa mutanen
kasar Gadamus masu fatauci, suka zo daga Turabulus(Libya), suka sauka
a birnin Kano, su ne Larabawan da suka fara zuwa Kano. Da saukar
wadannan fataken Larabawa, suka je wurin sarkin Kano Malam Yakubu, a
jujin 'Yan Labu, a lokacin ba a gina gidan sarautar Kano na yanzu ba,
Shamakin Kano Korau, yana shigar da su gaban sarki, suka ce da Sarki a
cikin harshen Larabci su fatake ne, suna so su zauna a Kano, domin su
yi ciniki.

A wannan Lokaci kuwa, limamin Kano Muhammadu Hashimu, shi ne yake
fassara wa Sarkin Kano abin da wadannan Larabawa suke fada cikin
harshen Hausa. Daga nan Sarkin Kano Yakubu ya yi farin ciki kwarai da
gaske da wadannan larabawa, sannan yace da Shamakin Kano, ya kai su
sararin nan na yamma da Unguwar Garke wato Dandali, su yi gidaje su
zauna a can. Saboda wadannan Larabawa suna da jar fata, sai mutane
suka sa musu suna Turawa. Ya yin da wadannan Fatake Larabawa suka yi
gidaje a wannan wuri suka zazzauna, sai Kanawa suka sa wa wannan
unguwa suna Dandalin Turawa, dalilin sunan Dandalin Turawa ta yanzu ke
nan, tun shekarar 553.

A waccan zamani, sarkin Kano yana da shekara daya a kan gadon sarautar
Kano. A zamaninsa Kano ta karu da arziki mai yawa da kuma garuruwa
ko'ina, a kowane gari, akwai makarantu na Al'kur'ani Mai Girma Har Ila
yau, kuma a kowane gari, akwai karofi da Mabugai da Masaku da Makera
da Dukawa, (Wato wurin Dukanci) da majema,(Wato wurin yin jima) da
kuma masassakan turmi da akusa, ko'ina sun yawaita a kasar Kano.
Tun daga waccan zamani Larabawa suka ci gaba da zuwa Kano, kamar
Yamalawa(Mutanen Yaman) da Larabawan Tunis, amma kowane da nau'in
kasuwancinsa. Su Larabawan Libiya duk kayan da suke sayarwa kayan
alatu ne(Suturu da kayan kamshi da kayan zaki).
Da wahala a ce ga lokacin asalin samuwar Kasuwanci a Kano. A zamanin
da, mutanen da ke Kano ba su san wata harka ta Kasuwanci ba, sai dai
sun fi mayar da hankali a kan aikin gona da aikin lambu. Amma an sani
cewa sana'o'inmu na Hausa wato sana'o'in gargajiya kamar su rini da
jima da kira da saka da sauransu, su suka haifar da ainihin samuwar
kasuwanci, domin kuwa a wancan zamanin mutum zai yi abu ya sayar don
amfanin jama'ar kasarsa, ko da yake lokacin da ba a fara amfani da
kudi a Kano ba, ana yin amfani da wata hanya ta ba ni gishiri in baka
manda (cinikin furfure ) don cinikayya.

Daga baya ne lokacin da fatake Larabawa ko Asbinawa da Agalawa suka zo
Kano, Kasuwanci ya fara Kankama. Haka kuma lokacin fataucin Kasar
Hausa, wato lokacin da abubuwan zirga-zirga na zamani ba su iso kano
ba, za mu iya cewa Kasuwanci ya samu kwarai a Kano, dangane da tawayen
da fatake suka yi wa kasar Katsina, suka dawo kasar Kano da sha'anin
Kasuwanci, kamar yadda aka fada a cikin littafi mai suna (Kano Civil
War and the Britshi Over Rule 1882-1940) na Muhammad F.A wannan ya
kawo mu har lokacin zuwan Turawa, wato lokacin da suka zo mana da
farin kudi a shekarar 1930, har aka fara amfani da shi a harkar
cinikayya ta Kano. Wannan ya sa kasuwanci ya dada samuwa kwarai a
Kano, ta hanyar bude ido da abin da Turawa suka zo da shi a sha'anin
kasuwanci, wanda ya kai jama'ar Kano suka san mene ne kasuwancin ma
kansa, har su tafiyar da sha'anin kasuwanci kansa, ba tare da wasu
Turawa sun ja musu gaba ba. Samuwar wannan kasuwanci a Kano ya fito
da Kano a idanun duniya baki daya, wanda har ta kai ga yi mata kirari
kamar haka, "Kano tumbin Giwa, ko da me ka zo an fika".

TASIRIN 'YAN KASUWA A NIJERIYA
Idan mun lura za mu ga ne cewa yan kasuwa suna da tasiri kwarai da
gaske a jihohin Nijeriya da kasa baki daya, musamman jihar Kano wadda
ake yi wa kirari da cibiyar kasuwancin afrika. Kuma manyan yan kasuwar
da suke baiwa kasa kayan masarufi da al'muran yau da kullum daga Kano
suke, dukkan wani kasuwanci a yau baya samun karbuwa matukar babu shi
a jihar Kano, duba da bayanan da suka gabata a baya za mu yarda da
cewa Kano ta zama tumbin giwa komai ka nema akwai a ciki.
'Yan kasuwa masu sha'awar kasuwa daga sassa daban-daban na duniya a
kullum shiga jihar Kano suke don tallata hajarsu, a saboda haka muna
iya cewa kano ta 'yan kasuwa ce.

YUNKURIN 'YAN KASUWA WAJEN KAFA MULKIN DIMOKARADIYA A NIJERIYA.
A yau idan ka raba mutanen Nijeriya kaso goma to kaso shida duka 'yan
kasuwa ne, ragowar kashin ne za a rabawa ma'aikatan gwamnati da sauran
sassa. Bisa kididdiga ko bincike da mu ka yi mun samu nasarar gano a
duk unguwa a Nijeriya cikin kowane gida matukar mutanen cikin sun
haura biyar sai ka samu dan kasuwa a ciki, kama daga masu sana'ar
sayar da Kosai, kitso, mai, Kanti, Shayi, shagunan kayan gyara da na
masarufi da suturu da sauransu.
Har ila yau wadannan mutane su ne suke tururuwa lokacin gudanar da har
zabe don zabar shugabanni 'yan boko wadanda za su jagorance su don
kawo musu ci gaba a har kasuwancinsu da bunkasarsa amma a wasu lokaci
harkar su ba ta cimma ruwa, wani sa'in ma sai a biyo su da neman su
biya haraji bayan ba su samu ribar zaben da suka yi ba, haka kuma
lokacin zabe wadannan yan siyasa za su sake wanke rigunansu su shigo
cikin al'ummar da ta zabe su wadanda mafi akasarinsu 'yan kasuwa ne su
ce a kara zabarsu karo na gaba, haka dai za su kara komawa bisa
matsayinsu ba tare da kawo wani babban ci gaba ba a harkar kasuwancin,
wanda kuma shi ne yake rike da kasar ma baki daya.

KAFA TSARIN SHUGABANCIN 'YAN KASUWA NA JIHA DA KANANAN HUKUMOMI.
A saboda wadancan dalilai na rashin samun tagomashin ribar romon
dimokaradiya da 'yan kasuwa ba sa yi ya sanya suka ga dacewar su kafa
gwamnatin da za su ji koken junansu da na sauran al'umma don ci gaban
kasuwanci da masana'antu a jiha da kasa baki daya.

Ga Yadda tsarin zai kasance
idan har kowani mai karamin sana'a zai iya aje wani abu daga cikin
abin da yake samu don bunkasar kasuwancinsa da goyon bayan wannan
tafiya, misali a ce ko wani mai sana'a a jihar kano zai a je Naira
dari(100) a wata don bayarwa a yankin da yake a matakin karamar hukuma
zuwa jiha to za a samu adadin abin ake so na kafa gwamnati da sauran
hidindimun da za su sanya kowa ya fahimci cewa "Daminar bana ta dara
ta bara"
don haka a wannan tsari za a kafa ofishi da zai kula da adadin 'yan
kasuwar da suke a kowacce karamar hukuma kuma za a yi wa kowa rijista
wacce za ta game duka yan kasuwar jihar Kano a inuwa daya yadda ko
wani tsunsu zai yi kukan gidansu.
Ta yadda za a zama tsintsiya madaurinki daya.

MATAKIN DA ZA A SANAR DA TSARIN
1-Za a yi amfani da kafafen yada labarai don sanar da wannan yunkuri.
2- Za a radawa tsarin suna yadda amonsa zai mamaye jiha da kasa baki daya.
3- Za a kafa tsarin shugabanci tun daga jiha har kananan hukumomi.
4-A karkashin wannan tsari za a fitar da shugabanin ta za su yi
takarar kujerun da ake bukata don biyan bukatar al'ummar kasa.

KARSHE
Ana fata wannan tsari ya zama kawo ci gaban da zai mayar da kasar
Nijeriya sama da kasashen da ake ganin sun taso tare amma sun fita ci
gaba.


On 11/23/17, Rabiu Muhammad Abu Hidaya <abuhidya3@gmail.com> wrote:
> Daga
> Rabi'u Muhammad Abu Hidaya Masarautar Bande wadda ta kasance masarauta
> mai dadadden tarihi cikin masarautun kasar Nijar ta
> samu sabon sarki bayan rasuwar tsohon sarkin
> garin,
> sarkin dai mai suna Abubakar Yahaya Lushe ya
> kasance shi ne sarki na bakwai a jerin sarakunan da suka mulki kasar
> ya kuma matashi ne jami'i a
> aikin Soja mai mukamin Kanal wanda ya bar aikin
> sojan don maye gurbin mahaifinsa domin shi
> mutum ne mai son ci gaban al'ummar kasarsa, ya
> samu zama sarkin ne bayan da masu ruwa da tsaki
> suka zabe shi a matsayin wanda zai gaji mahaifinsa da ya rasu kwanaki
> kadan baya, wannan zabi da
> aka yi masa dai ya faranta ran mafi yawa daga cikin
> jama'ar garin Bande da na masarautar, inda
> dukkansu su ka yi maraba da shi, domin sun
> tabbatar da cewa sabon sarkin na su yana da halin
> girma da dattako irin na mahaifinsa. A lokacin da sarkin yake jawabi
> game da kudirin
> da zai gabatar a masarautar da ya gada daga
> mahaifinsa ya ce "zai fi mayar da hankali ne game
> da abin ya shafi Ilimi a kasar da kuma harkar
> kasuwanci tare da wasannin gargajiya wadanda ya
> ce an yi musu nisa a sauran gurare. Ya kuma ce zai karfafa alaka da
> sauran masarautun
> da suke sauran kasashen da suke makotaka da
> masarautarsa"
> har ila yau da yake ci gaba da jawabi ya ce
> masarautarsa tana maraba da duk wani da yake da
> son ci gaban al'umma kuma zai yi hadin gwiwa da duk wanda da yake da
> harkar kasuwanci, haka
> kuma yace game da abin da ya shafi noma kiwo
> gami da kiwon lafiya nan ma ba za a bar kasar
> bande a baya ba, lallai a karkashin masarautarsa za
> a samu ci gaba sosai, babban burin wannan sabon
> sarki dai ya ce bai wuce ya samu hadin kan jama'ar kasarsa ba sannan
> yana fatan a ce ya fi mahaifinsa
> kokari.
> A nasa jawabin wani malamin Makaranta kuma na
> kusa da masarautar ya ce" lallai suna alfahari da
> wannan sarki wanda suke ganinsa tamkar
> mahaifinsa domin mahaifinsa ya zauna da kowa lafiya da ya kuma kaunaci
> talakawansa tamkar a
> 'yayan cikinsa shi mutum ne mai son talakawan
> kasarsa, kuma ya tabbatar da cewa wannan sarki
> zai kawo ma kasar Bande gagarumin ci gaba.
> A karshe mafi yawa daga cikin jama'ar kasar suna
> ta tururuwa domin yin mubaya'a ga sabon sarkin na su Abubakar Yahaya
> Lushe har ila yau kuma
> mutane da dama suna ta fatan ganin ranar da za a
> yi bikin ba shi sandar mulki domin su nuna masa
> soyayya da kauna.
>
> On 11/23/17, Rabiu Muhammad Abu Hidaya <abuhidya3@gmail.com> wrote:
>> ALMARA KO GASKE?
>>
>> Daga
>> Rabi'u Muhammad Abu Hidaya
>>
>>
>> Al'ada ta ce duk karshen mako na kan kai ziyara garinmu, domin gaishe
>> da iyaye, 'yan'uwa da
>> abokan arziki.
>> A garin akwai wata kasuwa da
>> ta ke ci duk ranar juma'a, kasancewata mutum ne mai son shan fura, don
>> haka duk ranar kasuwar garin na kan shiga kasuwar domin sayan fura,
>> akwai wata budurwar bafulatana, mai suna Hajjo, Hajjo tana da kirki
>> kwarai don haka ne ma, babu furar wadda da nake sha kaf
>> kasuwar sai ta ta, mun saba da Hajjo matukar sabo, domin idan na je
>> gurinta sam ba ta iya sakewa
>> saboda tsananin jin kunya.
>> So! shu'umi ya kan shiga zuciya ba tare da ya yi sallama ba. A kwana a
>> tashi sai na fara jin son Hajjo mai fura ya shiga zuciyata, domin har
>> ta kai idan na dawo kano bana iya sakewa in yi ayyukana yadda ya
>> kamata, haka zan ta fatan karshen mako ya yi na je garin, ban samu
>> nutsuwa ba sai da na bayyanawa Hajjo abin da yake raina, na ci sa'a
>> domin a karon farko Hajjo ta amince da ni a matsayin saurayinta.
>> Watarana ina kasuwa a cikin rumfar da Hajjo take sayar da fura muna
>> hira ina shan furar da ta dama min, sai nake
>> tambayarta Hajjo ya kamata a ce nasan gidanku
>> domin in zo mu yi maganar aure, shiru ta yi na 'yan
>> mintoci gami da aje ludayin furar da ke hannunta tare da sunkuyar da
>> kai kasa na dan wani lokaci, kana daga bisani sai ta ja wani dogon
>> numfashi! Gami da kallon wata yarinya da ke zaune a gefenta bisa wani
>> dutse tana sayar da mandako. Ko ba ki son in zo gidan ku ne? A'a kawai
>> dai ina wani dan tunani ne. Wai don Allah da gaske ka ke
>> kana so na?
>> (Dariya) ina sonki mana Hajjo. Amma me ya sa kika
>> min wannan tambayar?
>> Ai gani na yi kai dan birni
>> ne, me za ka yi da 'yar kauye iri na?Dariya na sake yi sannan na ce
>> mata kar ki damu Hajjo
>> ko ma ya ki ke ina sonki a haka kuma aurenki zan yi.
>> A karshe Hajjo ta kwatanta mini
>> rugar su, ranar Asabar ranar ce mu ka yi da Hajjo zan je rugar su.
>> Da misalin hudu da rabi na
>> yammacin ranar Asabar na shiga rugar su Hajjo, ban sha wata wahala ba
>> wajen neman gidansu ba, domin rugar ta su ba ta da girma sosai. Hajjo
>> tana gani na ta yi ta murna kamar ta rungume ni don tsananin jin dadi,
>> kusan duka mutanen gidan su Hajjo sai da suka zo muka gaisa tare da
>> nuna farin cikinsu da gani na.
>> Fura da nono mai kyau Hajjo ta kawo min, na kuma ji dadin furar
>> gaskiya kauye akwai dadi musamman rugagen fulani ba ruwansu ga yanayi
>> mai dadi ga kuma nono mai kyau ka sha iya shanka ba ka da damuwa.
>> Abu ka ga garinmu kauye ko?
>> Hajjo kenan, ai garin nan naku ina ganin bayan mun yi aure a nan za mu
>> zauna saboda ya min kyau.
>> Cikin jin dadi Hajjo ta rufe fuska da hannayenta tana murmushi alamun
>> jin kunya, kana ta ce haba dai ashe za ka iya zaman kauye?
>> Bayan na hadiye wani gayan fura tare lashe baki kai da ka gan ni kasan
>> ina jin dadin furar da nake sha, sai na bata amsa na ce ban da abin ki
>> Hajjo ai ko shugaban kasa zai so zama a nan ko don shan fura da nonon
>> da ke rugar nan.
>> Wannan karon dariya Hajjo ta yi har da kyakyatawa kana ta ce" gaskiya
>> Abu furar nan ta kama ka da kyau har da santi haka.
>> A ranar mun yi hira sosai kuma hira mai dadi da ita, sannan a karshe
>> mu ka yi bankwana tare da alkawarin kwanaki kadan masu zuwa zan sake
>> dawowa.
>>
>> KARO NA BIYU A RUGAR SU HAJJO
>> Daga ina ka ke?
>> Wa kake nema?
>> Yanzu ba mu da Hajjo a wannan gidan, Hajjonmu yau kimanin shekarunta
>> bakwai da rasuwa. Abin da aka shaida min kenan
>> bayan na koma rugar su Hajjo a karo na biyu.
>> Ikon Allah sai kallo, abin da ya fi bani mamaki shi ne duk mutanen
>> gidan su Hajjo babu wanda ya nuna ya ta6a ganina balle
>> mai kamata, na yi musu bayanin kamanin Hajjo sun tabbatar min ita ce
>> hasalima sun kawo min
>> hotunanta inda ni ma na tabbatar musu cewa ita din ce.
>> Cikin tsananin mamaki da kaduwa haka na baro rugar su Hajjo duk jiki
>> na ya yi sanyi.
>> Tun daga wannan ranar idanuna ba su sake tozali
>> da Hajjo ba balle mai kamarta. Kuma har yanzu zuciyata na cike da
>> matsananciyar kaunarta...
>>
>

AN YI NADIN SABON SARKI A MASARAUTAR BANDE

Daga
Rabi'u Muhammad Abu Hidaya Masarautar Bande wadda ta kasance masarauta
mai dadadden tarihi cikin masarautun kasar Nijar ta
samu sabon sarki bayan rasuwar tsohon sarkin
garin,
sarkin dai mai suna Abubakar Yahaya Lushe ya
kasance shi ne sarki na bakwai a jerin sarakunan da suka mulki kasar
ya kuma matashi ne jami'i a
aikin Soja mai mukamin Kanal wanda ya bar aikin
sojan don maye gurbin mahaifinsa domin shi
mutum ne mai son ci gaban al'ummar kasarsa, ya
samu zama sarkin ne bayan da masu ruwa da tsaki
suka zabe shi a matsayin wanda zai gaji mahaifinsa da ya rasu kwanaki
kadan baya, wannan zabi da
aka yi masa dai ya faranta ran mafi yawa daga cikin
jama'ar garin Bande da na masarautar, inda
dukkansu su ka yi maraba da shi, domin sun
tabbatar da cewa sabon sarkin na su yana da halin
girma da dattako irin na mahaifinsa. A lokacin da sarkin yake jawabi
game da kudirin
da zai gabatar a masarautar da ya gada daga
mahaifinsa ya ce "zai fi mayar da hankali ne game
da abin ya shafi Ilimi a kasar da kuma harkar
kasuwanci tare da wasannin gargajiya wadanda ya
ce an yi musu nisa a sauran gurare. Ya kuma ce zai karfafa alaka da
sauran masarautun
da suke sauran kasashen da suke makotaka da
masarautarsa"
har ila yau da yake ci gaba da jawabi ya ce
masarautarsa tana maraba da duk wani da yake da
son ci gaban al'umma kuma zai yi hadin gwiwa da duk wanda da yake da
harkar kasuwanci, haka
kuma yace game da abin da ya shafi noma kiwo
gami da kiwon lafiya nan ma ba za a bar kasar
bande a baya ba, lallai a karkashin masarautarsa za
a samu ci gaba sosai, babban burin wannan sabon
sarki dai ya ce bai wuce ya samu hadin kan jama'ar kasarsa ba sannan
yana fatan a ce ya fi mahaifinsa
kokari.
A nasa jawabin wani malamin Makaranta kuma na
kusa da masarautar ya ce" lallai suna alfahari da
wannan sarki wanda suke ganinsa tamkar
mahaifinsa domin mahaifinsa ya zauna da kowa lafiya da ya kuma kaunaci
talakawansa tamkar a
'yayan cikinsa shi mutum ne mai son talakawan
kasarsa, kuma ya tabbatar da cewa wannan sarki
zai kawo ma kasar Bande gagarumin ci gaba.
A karshe mafi yawa daga cikin jama'ar kasar suna
ta tururuwa domin yin mubaya'a ga sabon sarkin na su Abubakar Yahaya
Lushe har ila yau kuma
mutane da dama suna ta fatan ganin ranar da za a
yi bikin ba shi sandar mulki domin su nuna masa
soyayya da kauna.

On 11/23/17, Rabiu Muhammad Abu Hidaya <abuhidya3@gmail.com> wrote:
> ALMARA KO GASKE?
>
> Daga
> Rabi'u Muhammad Abu Hidaya
>
>
> Al'ada ta ce duk karshen mako na kan kai ziyara garinmu, domin gaishe
> da iyaye, 'yan'uwa da
> abokan arziki.
> A garin akwai wata kasuwa da
> ta ke ci duk ranar juma'a, kasancewata mutum ne mai son shan fura, don
> haka duk ranar kasuwar garin na kan shiga kasuwar domin sayan fura,
> akwai wata budurwar bafulatana, mai suna Hajjo, Hajjo tana da kirki
> kwarai don haka ne ma, babu furar wadda da nake sha kaf
> kasuwar sai ta ta, mun saba da Hajjo matukar sabo, domin idan na je
> gurinta sam ba ta iya sakewa
> saboda tsananin jin kunya.
> So! shu'umi ya kan shiga zuciya ba tare da ya yi sallama ba. A kwana a
> tashi sai na fara jin son Hajjo mai fura ya shiga zuciyata, domin har
> ta kai idan na dawo kano bana iya sakewa in yi ayyukana yadda ya
> kamata, haka zan ta fatan karshen mako ya yi na je garin, ban samu
> nutsuwa ba sai da na bayyanawa Hajjo abin da yake raina, na ci sa'a
> domin a karon farko Hajjo ta amince da ni a matsayin saurayinta.
> Watarana ina kasuwa a cikin rumfar da Hajjo take sayar da fura muna
> hira ina shan furar da ta dama min, sai nake
> tambayarta Hajjo ya kamata a ce nasan gidanku
> domin in zo mu yi maganar aure, shiru ta yi na 'yan
> mintoci gami da aje ludayin furar da ke hannunta tare da sunkuyar da
> kai kasa na dan wani lokaci, kana daga bisani sai ta ja wani dogon
> numfashi! Gami da kallon wata yarinya da ke zaune a gefenta bisa wani
> dutse tana sayar da mandako. Ko ba ki son in zo gidan ku ne? A'a kawai
> dai ina wani dan tunani ne. Wai don Allah da gaske ka ke
> kana so na?
> (Dariya) ina sonki mana Hajjo. Amma me ya sa kika
> min wannan tambayar?
> Ai gani na yi kai dan birni
> ne, me za ka yi da 'yar kauye iri na?Dariya na sake yi sannan na ce
> mata kar ki damu Hajjo
> ko ma ya ki ke ina sonki a haka kuma aurenki zan yi.
> A karshe Hajjo ta kwatanta mini
> rugar su, ranar Asabar ranar ce mu ka yi da Hajjo zan je rugar su.
> Da misalin hudu da rabi na
> yammacin ranar Asabar na shiga rugar su Hajjo, ban sha wata wahala ba
> wajen neman gidansu ba, domin rugar ta su ba ta da girma sosai. Hajjo
> tana gani na ta yi ta murna kamar ta rungume ni don tsananin jin dadi,
> kusan duka mutanen gidan su Hajjo sai da suka zo muka gaisa tare da
> nuna farin cikinsu da gani na.
> Fura da nono mai kyau Hajjo ta kawo min, na kuma ji dadin furar
> gaskiya kauye akwai dadi musamman rugagen fulani ba ruwansu ga yanayi
> mai dadi ga kuma nono mai kyau ka sha iya shanka ba ka da damuwa.
> Abu ka ga garinmu kauye ko?
> Hajjo kenan, ai garin nan naku ina ganin bayan mun yi aure a nan za mu
> zauna saboda ya min kyau.
> Cikin jin dadi Hajjo ta rufe fuska da hannayenta tana murmushi alamun
> jin kunya, kana ta ce haba dai ashe za ka iya zaman kauye?
> Bayan na hadiye wani gayan fura tare lashe baki kai da ka gan ni kasan
> ina jin dadin furar da nake sha, sai na bata amsa na ce ban da abin ki
> Hajjo ai ko shugaban kasa zai so zama a nan ko don shan fura da nonon
> da ke rugar nan.
> Wannan karon dariya Hajjo ta yi har da kyakyatawa kana ta ce" gaskiya
> Abu furar nan ta kama ka da kyau har da santi haka.
> A ranar mun yi hira sosai kuma hira mai dadi da ita, sannan a karshe
> mu ka yi bankwana tare da alkawarin kwanaki kadan masu zuwa zan sake
> dawowa.
>
> KARO NA BIYU A RUGAR SU HAJJO
> Daga ina ka ke?
> Wa kake nema?
> Yanzu ba mu da Hajjo a wannan gidan, Hajjonmu yau kimanin shekarunta
> bakwai da rasuwa. Abin da aka shaida min kenan
> bayan na koma rugar su Hajjo a karo na biyu.
> Ikon Allah sai kallo, abin da ya fi bani mamaki shi ne duk mutanen
> gidan su Hajjo babu wanda ya nuna ya ta6a ganina balle
> mai kamata, na yi musu bayanin kamanin Hajjo sun tabbatar min ita ce
> hasalima sun kawo min
> hotunanta inda ni ma na tabbatar musu cewa ita din ce.
> Cikin tsananin mamaki da kaduwa haka na baro rugar su Hajjo duk jiki
> na ya yi sanyi.
> Tun daga wannan ranar idanuna ba su sake tozali
> da Hajjo ba balle mai kamarta. Kuma har yanzu zuciyata na cike da
> matsananciyar kaunarta...
>