0
A cikin Afirilun bana, Gidan Adana Kayan Tarihi
na kasar Burkina Faso tare da hadin gwiwar
Kungiyar Makaranta sun karrama marubuci
Dokta Bukar Usman da kambin girmamawa,
bisa la'akari da gudunmowarsa wajen bunkasa
Adabin Hausa da kuma jaddada zaman lafiya tsakanin al'ummar Hausa da
duniya baki daya.
Bayan ya dawo, ya rubuta wannan tsaraba ga
masu karatu, kamar haka: Ita dai Kungiyar Makaranta, kungiya ce mai zaman
kanta, wacce ba ta gwamnati ba kuma al'ummar
Hausawa mazauna kasar Burkina Faso ce ta kafa ta
a 2006, da nufin bunkasa al'adu, ilimi,
zamantakewa, tattalin arziki da kuma harshen
Hausa a kasar. Domin tabbatar da wannan kuduri nata, sai kungiyar ta
shirya gagarumin biki, wanda
ya hada da kalankuwa, baje kolin kayan gargajiya,
babban taron masana daga ko'ina a duniya da
kuma karrama wasu muhimman 'yan Afrika da
suka taimaka wajen bunkasa al'ummar Hausawa.
Ina daya daga cikin wadanda aka zaba, domin karramawa. Haka kuma, ba
yan ni kaina, an kuma
zabi Sanata (Injiniya) Rabi'u Musa Kwankwaso,
tsohon Gwamnan Jihar Kano. Sanata Kwankwaso da ni kaina, mun halarci
bikin a Babban Birnin Burkina Faso, Ouagadougou
(Wagadugu). Ma'anar sunan birnin nan shi ne
'Wurin da ake karrama da girmama mutane' - babu
shakka birnin ya ci sunansa, domin kuwa hakika
ana girmama baki da daraja su. An karrama ni da kambi tare da takardar
shaida mai taken 'Jakadan
Adabin Hausa.' Wannan taro na kasa-da-kasa, an yi masa lakabi
da "Gudunmowar Al'adun Hausa Wajen Wayar Da
Kan Al'ummar Afirka." Kasar Hausa ta yi fice wajen
saka da rini da kira da jimar fata da ginin tukwane
da sauran ayyukan fasaha da zayyana, wadanda
ake sayarwa har wajen kasar ta Hausa. Harshen Hausa na daya daga cikin
manyan harsunan
duniya. Adabin Hausa na ci gaba da bunkasa,
musamman ana samun rubuce-rubuce a fannoni
da dama na ci gaban al'umma, duk kuwa da cewa
akwai bukatar a rika amfani da na'urorin zamani
tare da tsarin dauri wajen taskance harshen da al'adunsa domin amfanin
gida da ma al'ummar
duniya baki daya. An nuna sha'awar sanin ainahin
sunayen da ake amfani da su a kasar Hausa, kafin
zuwan Musulunci, sannan kuma aka nuna takaici
da yadda yara kan gaza yin magana da harshen
iyayensu. A yayin bikin nunin kayan al'adun gargajiya na
Hausa, wanda Ministan Al'adu Da Shakatawa na
Burkina Faso, Mista Tahirou Barry ya bude, an baje
kolin kayayyaki daban-daban, har ma da abincin
gargajiya. Kayan sun hada da zayyane-zayyane da
aka yi na fata, duwatsu, tabarmi da mafutai, kayan aikin noma, kayan
girki da na cin abinci, korai,
sakakkun suturu da kuma tukwane iri daban-
daban da aka yi wa zayyana masu kyau. Haka
kuma akwai ingantattun magungunan gargajiya
da sake-saki, nama iri-iri da kayan sha na gargajiya
daban-daban. An sha kallo kuma an nishadantu da kade-kade
da wake-waken gargajiya na Hausa, ga wasanni,
musamman na kokowa da aka gudanar. Wasan
kokowa na daya daga cikin wasanni masu tashe a
kasar Burkina Faso. Tawagar karfafa kuma
gwanayen kokowa daga Jamhuriyyar Nijar ta halarci bikin. A yayin da
aka gudanar da tarukan
kara wa juna ilimi a ranakun 14-16 na watan Afrilu,
an ci gaba da baje kolin kayayyakin gargajiya,
wanda zai dore har zuwa tsakiyar Yunin bana. Zan iya tunawa, a
lokacin da nake makarantar
sakandare, a 1960, na samu labarin madaukakun
Daulolin Mossi Dagomba da ke yankin Tsakiyar
Afrika ta Yamma. A wannan zamani a yau, a
Burkina Faso, irin wadannan dauloli da suka
bunkasa, sun ci gaba da bunkasa har zuwa lokacin da Turawan mulkin
mallaka na Faransa suka
murkushe su a wajajen 1896. Wannan dalili ma na
daga cikin dalilan da suka sanya na yi kwadayin
ziyartar kasar, musamman domin in tantance
wadannan kayatattun labarun da suka shafi kasa
da al'ummomin Burkina Faso, kamar yadda aka gaya mana a can baya.
A sakamakon tsawon lokacin da na yi ina
nazarin tsarin al'umma, na fahimta da cewa duk mai
son ya fahimci tarihi da al'adun al'umma, zai iya
samun ilimi mai yawa daga almara da
tatsuniyoyinsu. Wannan ya sanya a lokacin da na
sauka a birnin Wagadugu, tun ma kafin in sauka a masaukina na otel,
sai na yi wa shagon sayar da
littattafai tsinke, domin in samu littafin da ya yi
bayani game da kasa da al'ummar Burkina Faso.
Tabbas kuwa na ga littattafai da yawa da za su yi
mani amfani, amma abin takaici, babu ko daya da
aka rubuta da Ingilishi. Na yi kokarin tambayar inda zan samu littattafan
da nake nema, amma ban dace ba. Don haka sai na
maida hankali ga intanet, inda na samu bayanai irin
na kunne-ya-girmi-kaka. Na fahimta da cewa a
kasar, manyan yarukan da ake amfani da su, su ne
Moore da Djula da kuma Faransanci. Burkina Faso na da kabilu 63,
cikinsu har da Fulani da Yarabawa
da Ibo, tare da shugabanninsu. Burkina Faso, wadda ke nufin 'kasar mutane
masu gaskiya' tana da tarihi mai tsawo. Tarihinta ya
faro ne tun 1896, lokacin da Faransa ta yi tunga a
yankin a matsayin mallakinta. A 1904, Faransa ta
mallaki kasar Upper Senegal da Yankin Nijar a
Afrika ta Yamma, inda birnin Bamako ya kasance hedikwata. Daga bisani
aka canja wa yankin suna
zuwa French Upper Volta mai hedikwata a
Wagadugu, a 1919. A shekarar 1932 aka rushe
wannan tsari, aka karkasa kasashen zuwa Ivory
Coast da Sudan da Nijar. An sake maida ta tsarin
baya a 1947, inda aka dawo da yankin Upper Volta, aka mayar mata da
iyakokinta. An ba ta
mulkin kanta a 1958, sannan aka ba ta 'yancin kai
da sunan Jamhuriyyar Upper Volta a 1960. Kamar dai yadda ta faru
a Najeriya, sojoji sun
tsoma hannunsu a mulkin Jamhuriyyar Upper Volta
a 1966, inda gwamnatin ta soja ta kare a 1976.
Sabuwar gwamnatin farar hula da ta gaji ta soja, an
tunkude ta ita ma a 1980, inda sojan suka ci gaba
da mulki zuwa 1983. Thomas Sankara da Blaise Campaore ne suka ci gaba
da mulki a kakin soja
kuma wannan gwamnatin ce ma ta canja wa kasar
suna zuwa Burkina Faso a 1984. Bayan an yi wa
Thomas Sankara kisan gilla a 1987, kasar ta samu
natsuwar mulki a karkashin Shugaban Kasa Blaise
Campaore na tsawon shekara 27. An matsa masa lamba, dole ya sauka daga
mulki a 2014. Tsohon sunan kasar na Upper Volta, an samo shi
ne daga Koramar Volta, wacce ta hade har zuwa
Kogin Atilantika, wanda ya ratsa har zuwa kasar
Ghana a yanzu. Wani Baturen Fotugal ne ya rada
mata sunan "Volta" domin ya yi la'akari da yadda ta
yi ta kwana-kwana. Koramar tana da manyan bakuna uku, Farar Volta, Jar
Volta da kuma Bakar
Volta, wanda haka ke nuna launin kasar wuraren.
Launin kasar Wagadugu ja ce kuma Jar Volta na
Arewa Maso Yammacin Wagadugu. Burkina Faso a yanzu haka tana da yawan
mutane miliyan 20, inda Wagadugu ne Fadar
Gwamnati, wanda ke kunshe da yawan mutane
kimanin miliyan 2. Birnin Kasuwancin kasar,
sunansa Bobo-Dioulasso, yawan al'ummarsa na
kasa da miliyan daya ne kuma an yi kidayar jama'a ta karshe a 1982.
Mossi ita ce kabila mai mafi yawan mutane a
kasar kuma suna da karin harshe kala biyu,
Kompela da Tenkodogo. Mutanensu sun yi suna
wajen hakuri da juriya, don haka Turawan Faransa
suka rika daukar mazansu aikin soja, kuma aka
rika ba su aikin gina hanyoyin jirgin kasa da na mota. Haka ma
matansu, ba su da son jiki, suna da
kokarin neman abinci. Ba su jin nauyi, domin za ka
gan su suna tuka babur da motocin haya a babban
birnin kasar. Suna yin noma, ban ruwa a fadamu,
aikin buga bulo ko yin aikin siminti. An taba
haramta auren mace fiye da daya a zamanin mulkin Sankara amma daga
baya gwamnatin da ta gaje shi
ta dawo da shi. Wannan ya sanya mutane da suke
daraja al'ada suka rika auren mata da yawa. Duk
macen da mijinta ya mutu, ba ta fita daga gidan
aurenta, sai dai kawai ta zabi namiji daya daga
dangin mijinta, ta sake aure. Noma, shi ne babbar sana'ar mutanen kasar.
Suna noma jar dawa da gyada, haka ma suna noma
acca. Kamar Masar da Sudan, su ma Burkina Faso
suna noma auduga mai yawa da suke sayarwa
kasashen waje. Suna da ma'aidinan zinari da azurfa
da sauransu, wadanda kasashen Australia da Afrika ta Kudu da Faransa
da Japan da Ghana da
sauransu ke amfana sosai ta hanyar hako su. Kasar
tana dogaro da agajin kasashen waje ta bangaren
tattalin arziki. Otel din Laico, wanda kuma ake kira
da Hotel Libya shi ne kusan otel mafi inganci a
Wagadugu. Marigayi Muamar Gaddafi ne ya gina shi kuma yana daya daga
cikin abin alherin da 'yan
kasar ke tuna marigayin shi da shi. Wasu daga ciki
wuraren bude ido a Wagadugu sun hada har da
'Zauren Shahidai' wanda yake kan hanyar Muamar
Gaddafi. An gina shi ne domin tunawa da mutanen
da aka rasa a hautsinin da ya faru a 2014. Masu masaukina a kasar
Burkina Faso, sun
kasance tsatson Hausawa. Kakanninsu sun yo hijira
ne daga Najeriya, musamman daga Kano,
Sakkwato, Katsina, Kebbi da sauran biranen Arewa.
Sun ce sun sauka a Upper Volta ne a matsayin 'yan
kasuwa, masaka, masunta, tun kafin zuwan Turawan Mulkin Mallaka na
Faransa. Sun ce su ne
ma tun farko suka fara kai sana'ar rini da sakar
tufafi a kasar. Har zuwa yau kuwa, irin suturunsu
ne ake alfahari da su a kasar. Akwai al'ummar Hausawa da dama a biranen
kasar Burkina Faso, suna zaune ne a
unguwanninsu da ake wa lakabi ba Zango, sunan
da aka samo a sanadiyyar kasuwancin da ya
gudana shekaru masu yawa da suka shude, inda
'yan kasuwa kan keta sahara daga wannan kasa zuwa waccan a kan rakuma.
Wuraren da suke yada
zango ne ake lakaba wa sunan unguwar ta
Hausawa. A birnin Wagadugu, an canza wa Zango
na ainahi matsuguni har sau biyu, domin kuwa
ayyukan raya birnin ya shafe shi. Zango na farko
yana kusa da tashar jirgin kasa, shi kuwa Zango na biyu, inda nan
Hausawan suka zauna tsawon
shekara 85, yana cikin kawyar birnin, nisan
kilomita biyu daga Fadar Masarautar Moogo Naaba,
Sarkin Gargajiyar Mossi; wanda suke da
kyakkyawar mu'amala da shi. A 2001, Gwamnatin
Blaise Campaore ce ta canza wa Zangon wuri zuwa inda yake yanzu, kusa
da Fadar Shugaban Kasa. Kalilan daga cikin Hausawa da suka yi
karatun
Boko, sun rike manyan mukamai a Ma'aikatun
Gwamnatin Burkina Faso da sauran wurare har ma
da wajen kasar. Daga bisani ne suka farga da
muhimmancin ilimin zamani, inda suka kafa
Kungiyar Makaranta, wacce ke taimakawa wajen fadakar da al'ummarsu,
muhimmancin da ke tattare
da ilimin na zamani. Akwai abubuwa da yawa da mutum zai nazarta
kuma ya karu a kasar Burkina Faso, duk kuwa da
cewa karamar kasa ce da ba ta da yawan
albarkatun kasa kamar wasu. Suna tafiyar da
al'amuransu a kan tsari, ga su da bin doka da oda. Moogo Naaba
(Sarkin Duniya), shi ne lakanin
Sarkin Gargajiya na Mossi da ke Wagadugu. Ana ba
shi girma da daraja sosai. Kasancewar fadarsa na a
babban birnin kasar, yana da martaba ta
musamman, duk kuwa da cewa shi ne na hudu a
tsarin martabar sarakuna a Daular Mossi ta Burkina Faso. Tarihi
ya nuna cewa Daular Mossi a Burkina Faso
ta samo asali ne tun a Karni na 7. Kamar yadda
tarihin ya tabbatar, Sarkin Gambaga na kabilar
Dagomba a Arewacin Ghana, diya mace kawai ya
haifa. Bayan ta yi aure, wata rana sai ta fita kilisa a
doki, ta shiga daji kuma ta yi makuwa. Wani maharbi dan kasar Mali ya
tsince ta kuma suka yi
aure, suka haifi da namiji. Kasancewar a kan doki
aka samu mahaifiyar jaririn, sai aka rada masa suna
Ouedraogo (sunan namijin doki ke nan a Daular
Mossi). Shi Ouedraogo ne ya zama Sarki na farko a
Daular Mossi kuma shi ne ya kafa Masarautar
Tenkodogo. Sarkin Mossi na yanzu a Wagadugu,
Naaba Booggo, shekararsa 34 ke nan a kan
karaga. Shi ne sarki na 147 a jerin sarakunan
daular. Masarautar tana daraja al'ada sosai, musamman akwai wata
al'ada da har yanzu take
wanzuwa. Kamar yadda sauran sarakunan kasar
suka rika yi, duk Jumu'a, Naaba Booggo kan shiga
sulke, ya hau doki da nufin tafiya yaki da wasu
al'umma da ke Mali. Haka za a yi ta lallashinsa, ana
ba shi hakuri, sannan ya sauko. Wannan shauki na yaki ya zama jiki a
masarautar, duk Jumu'a. Mai martaba Naaba Booggo ya amshi
bakuncin
mu mahalarta wannan muhimmin taro. Kafin mu
kai ga ganawa da shi, sai da aka yi ta kai-komo
wajen bin ka'idoji daban-daban amma duk da
haka kwalliya ta biya kudin sabulu. Mutanen
Burkina sun yi suna wajen hakuri, don haka sun dauka bakinsu ma haka
ne. Sarkin na zaune a bisa
karaga, tsakiyar butumbutumin zakoki biyu,
hakoransu a bude, gwanin ban tsoro. Da yarensu
ya yi mana jawabi, tafinta ya rika fassara mana. Ya
yi mana jawabi ne game da rainon yara, inda ya
nuna cewa zamani ya canja, don haka akwai bukatar dattawa su maida
hankali wajen kyautata
rainon yara, domin su tashi da da'a da biyayya, a
matsayin 'yan kasa nagari. Na fahimta da cewa, irin
wannan sakon ne yake isarwa ga dukkan tawagar
da ta ziyarci fadar tasa. Domin kare martabar al'adun Masarautar Mossi,
an haramta wa kowane mutum daukar hoton wani
abu a fadar masarautar ba tare da izini ba. Sarkin
dai ya karrama mu, inda ya amince muka dauki
hoto da shi a wajen fadar. Akwai wani azancin
magana da aka rubuta baro-baro a wata hasumiyar masarautar da harsuna
uku na Moore
da Djula da Fulatanci, kamar haka: "Duk inda ka ga
dattijo, da wuya a aikata ba daidai ba a wurin." Naaba Booggo,
dan kwallo ne. Babu mamaki,
watakila shi ya sanya ma aka gina babban filin
wasa na kasa kusa da fadar masarautarsa. Na samu
bayanin cewa, shahararren dan kwallon nan na
kasar Kamaru, Samuel Eto ne ya gina shingayen
karfe da suka kewaye kofar fadar sarkin saboda nuna gamsuwa da yadda
sarkin ke sha'awar
wasan kwallon kafa. Mun karu da wasu karin azancin magana a fadar
Sarkin Hausawa a Zango. Kakakin Fadar ya ambata
cewa: "Abu ne mai sauki ka ga makiyayi yana
sarrafa garken shanu da sanda guda, a yayin da
abu ne mai matukar wahala ka mulki jama'a kamar
haka." Wannan yana yi mana ishara da yadda mulki ke da wahala.
Taron kara wa juna sani da kuma bikin,
kasancewarsu na kasa-da-kasa, an gayyaci
mahalarta daga kasashen Benin, Kamaro, Afrika Ta
Tsakiya, Chadi, Ghana, Nijar, Najeriya, Togo da
kuma Sudan kuma dukkan wadannan kasashe,
akwai al'ummar Hausawa da yawa. Taron ya samu halartar baki sosai, sai
son barka, domin kuwa
sarakunan gargajiya har uku suka zo daga kasar
Togo kadai. Ba domin matsalolin sufuri da ke
addabar nahiyar Afrika ba, da an samu mahalarta
taron fiye da kima. Amma duk da haka, taron ya
samu yabo daga mahalarta, a yayin da kasashen Togo da Senegal suka
dauki alkawarin shirya irinsa
a nan gaba. Tafiya ta jirgin sama daga Abuja zuwa
Wagadugu akwai wahala. An ba ni shawarar in
shiga jirgi zuwa Kairo (Masar), ko kuma in bi ta
wasu kasashen ma da ba na Afrika ba domin zuwa
Wagadugu. Hanya mafi gajarta, ita ce ta Lome
(Togo) ko Abdijan (Kwaddabuwa) kuma sai mutum ya kwana biyu a hanya.
Matafiya daga
Najeriya da suka biyo ta hanyar mota, sai da suka yi
kwana uku, sun yada zango a Maradi da Yamai
(Jamhuriyyar Nijar), sannan suka isa Wagadugu a
rana ta ukun saboda jidalin bincike-binciken
jami'an tsaro a iyakokin kasashen. Kodayake duk da wannan
jidalin, tafiya ta mota
na tattare da nishadi, domin kuwa mutum zai karu
sosai da sababbin abubuwa a hanya, na mutane iri-
iri da kuma wurare. Ta fannin gane-gane a hanya
kuwa, masu tafiya ta jirgi ma sun karu, domin kuwa
mutum zai samu damar ganin falalen kasa, da itatuwa nan da can da
hanyoyin kasa marasa
kwalta da kuma gidaje warwatse, nan da can. Lallai
akwai yalwar kasa, wacce ya kamata a aikata ta,
domin ceto ta daga balbalcewa. Na yi hira da wasu abokan tafiyata, wadanda
suka bayyana abubuwan burgewa game da
Najeriya. A jirgin da na shiga zuwa Abdijan zuwa
Wagadugu, wani tsohon malamin Kwalejin Fourah
Bay, Saliyo ya bayyana takaicinsa game da Najeriya.
Ya bayyana yadda Allah Ya albarkaci Najeriya da albarkatun kasa amma
saboda halin ko-in-kula na
al'ummar kasar, an kasa amfana. Domin kawo
gyara, ya ce 'Najeriya na bukatar shugaba mai
nuna karfa-karfa, amma ba mai zuciyar kisa ba.' Haka kuma mun
tattauna kan al'amuran da suka
shafi 'yancin dan Adam, musamman sakamakon
yadda wasu mutum biyu suka rika cacar baki da
juna. Daya daga cikinsu ma Bature ne. Wani mutum
ne da ke zaune a bayan Baturen, yake ta magana a
waya da karfi, shi ne Baturen ya kasa daurewa, ya shiga damuwa sosai,
ya yi korafi. Shi kuma mai
waya sai ya harzuka, ya maida masa martani mai
kaushi, sai suka fara fada. Kafin ka ce kwabo, sai
fadan ya girma har da zage-zagen juna, kowa na
nuna cewa shi ke da gaskiya. Baturen ya roki
ma'aikacin jirgin da ya sanya baki amma hakan ba ta samu ba. Haka suka
ci gaba da cacar bakinsu,
har suna cewa za su dambace, da zarar sun sauka
daga jirgin. Duk dai a cikin jirgin nan, wasu fasinjoji biyu,
daya dattijo, daya kuma budurwa ce, su ma sun yi
nasu wasan kwaikwayon. Dattijon ne yake ta buga
kwamfutarsa (laptop) abinsa, sai ita kuma matar ta
yi korafin cewa gwiwar hannunsa na tunkurinta.
Shi kuma mutumin ya yi biris da ita. Haka abin ya ci gaba, ba a samu
maslaha ba sai da matar ta canja
wurin zama. Babu shakka akwai darussa daga abubuwan
nan da suka faru. Wani babban darasi daya a nan
shi ne, a lokacin da mutum ke neman kare
hakkinsa, yana da kyau ya yi la'akari da hakkin
sauran mutane. Idan na kalli wadannan al'amura
da suka faru a jirgi kuma na duba dalilin da ya sanya aka gayyace ni
zuwa Burkina Faso domin a
karrama ni, sai na fahimta da cewa a rayuwa muna
bukatar mu kasance masu fahimtar juna, mu daraja
ra'ayin juna a mu'amala, mu daraja al'adu da
ra'ayoyin juna kuma mu yi iyaka kokarinmu wajen
wanzar da zaman lafiya a tsakanin al'umma. Dokta Bukar Usman,
marubuci ne kuma
tsohon Babban-Sakatare a Fadar Shugaban

Post a Comment

Dear readers, after reading the Content please ask for advice and to provide constructive feedback Please Write Relevant Comment with Polite Language.Your comments inspired me to continue blogging. Your opinion much more valuable to me. Thank you.

BULAGURON MARUBUCI BUKAR USMAN ZUWA BURKINA FASO

A cikin Afirilun bana, Gidan Adana Kayan Tarihi
na kasar Burkina Faso tare da hadin gwiwar
Kungiyar Makaranta sun karrama marubuci
Dokta Bukar Usman da kambin girmamawa,
bisa la'akari da gudunmowarsa wajen bunkasa
Adabin Hausa da kuma jaddada zaman lafiya tsakanin al'ummar Hausa da
duniya baki daya.
Bayan ya dawo, ya rubuta wannan tsaraba ga
masu karatu, kamar haka: Ita dai Kungiyar Makaranta, kungiya ce mai zaman
kanta, wacce ba ta gwamnati ba kuma al'ummar
Hausawa mazauna kasar Burkina Faso ce ta kafa ta
a 2006, da nufin bunkasa al'adu, ilimi,
zamantakewa, tattalin arziki da kuma harshen
Hausa a kasar. Domin tabbatar da wannan kuduri nata, sai kungiyar ta
shirya gagarumin biki, wanda
ya hada da kalankuwa, baje kolin kayan gargajiya,
babban taron masana daga ko'ina a duniya da
kuma karrama wasu muhimman 'yan Afrika da
suka taimaka wajen bunkasa al'ummar Hausawa.
Ina daya daga cikin wadanda aka zaba, domin karramawa. Haka kuma, ba
yan ni kaina, an kuma
zabi Sanata (Injiniya) Rabi'u Musa Kwankwaso,
tsohon Gwamnan Jihar Kano. Sanata Kwankwaso da ni kaina, mun halarci
bikin a Babban Birnin Burkina Faso, Ouagadougou
(Wagadugu). Ma'anar sunan birnin nan shi ne
'Wurin da ake karrama da girmama mutane' - babu
shakka birnin ya ci sunansa, domin kuwa hakika
ana girmama baki da daraja su. An karrama ni da kambi tare da takardar
shaida mai taken 'Jakadan
Adabin Hausa.' Wannan taro na kasa-da-kasa, an yi masa lakabi
da "Gudunmowar Al'adun Hausa Wajen Wayar Da
Kan Al'ummar Afirka." Kasar Hausa ta yi fice wajen
saka da rini da kira da jimar fata da ginin tukwane
da sauran ayyukan fasaha da zayyana, wadanda
ake sayarwa har wajen kasar ta Hausa. Harshen Hausa na daya daga cikin
manyan harsunan
duniya. Adabin Hausa na ci gaba da bunkasa,
musamman ana samun rubuce-rubuce a fannoni
da dama na ci gaban al'umma, duk kuwa da cewa
akwai bukatar a rika amfani da na'urorin zamani
tare da tsarin dauri wajen taskance harshen da al'adunsa domin amfanin
gida da ma al'ummar
duniya baki daya. An nuna sha'awar sanin ainahin
sunayen da ake amfani da su a kasar Hausa, kafin
zuwan Musulunci, sannan kuma aka nuna takaici
da yadda yara kan gaza yin magana da harshen
iyayensu. A yayin bikin nunin kayan al'adun gargajiya na
Hausa, wanda Ministan Al'adu Da Shakatawa na
Burkina Faso, Mista Tahirou Barry ya bude, an baje
kolin kayayyaki daban-daban, har ma da abincin
gargajiya. Kayan sun hada da zayyane-zayyane da
aka yi na fata, duwatsu, tabarmi da mafutai, kayan aikin noma, kayan
girki da na cin abinci, korai,
sakakkun suturu da kuma tukwane iri daban-
daban da aka yi wa zayyana masu kyau. Haka
kuma akwai ingantattun magungunan gargajiya
da sake-saki, nama iri-iri da kayan sha na gargajiya
daban-daban. An sha kallo kuma an nishadantu da kade-kade
da wake-waken gargajiya na Hausa, ga wasanni,
musamman na kokowa da aka gudanar. Wasan
kokowa na daya daga cikin wasanni masu tashe a
kasar Burkina Faso. Tawagar karfafa kuma
gwanayen kokowa daga Jamhuriyyar Nijar ta halarci bikin. A yayin da
aka gudanar da tarukan
kara wa juna ilimi a ranakun 14-16 na watan Afrilu,
an ci gaba da baje kolin kayayyakin gargajiya,
wanda zai dore har zuwa tsakiyar Yunin bana. Zan iya tunawa, a
lokacin da nake makarantar
sakandare, a 1960, na samu labarin madaukakun
Daulolin Mossi Dagomba da ke yankin Tsakiyar
Afrika ta Yamma. A wannan zamani a yau, a
Burkina Faso, irin wadannan dauloli da suka
bunkasa, sun ci gaba da bunkasa har zuwa lokacin da Turawan mulkin
mallaka na Faransa suka
murkushe su a wajajen 1896. Wannan dalili ma na
daga cikin dalilan da suka sanya na yi kwadayin
ziyartar kasar, musamman domin in tantance
wadannan kayatattun labarun da suka shafi kasa
da al'ummomin Burkina Faso, kamar yadda aka gaya mana a can baya.
A sakamakon tsawon lokacin da na yi ina
nazarin tsarin al'umma, na fahimta da cewa duk mai
son ya fahimci tarihi da al'adun al'umma, zai iya
samun ilimi mai yawa daga almara da
tatsuniyoyinsu. Wannan ya sanya a lokacin da na
sauka a birnin Wagadugu, tun ma kafin in sauka a masaukina na otel,
sai na yi wa shagon sayar da
littattafai tsinke, domin in samu littafin da ya yi
bayani game da kasa da al'ummar Burkina Faso.
Tabbas kuwa na ga littattafai da yawa da za su yi
mani amfani, amma abin takaici, babu ko daya da
aka rubuta da Ingilishi. Na yi kokarin tambayar inda zan samu littattafan
da nake nema, amma ban dace ba. Don haka sai na
maida hankali ga intanet, inda na samu bayanai irin
na kunne-ya-girmi-kaka. Na fahimta da cewa a
kasar, manyan yarukan da ake amfani da su, su ne
Moore da Djula da kuma Faransanci. Burkina Faso na da kabilu 63,
cikinsu har da Fulani da Yarabawa
da Ibo, tare da shugabanninsu. Burkina Faso, wadda ke nufin 'kasar mutane
masu gaskiya' tana da tarihi mai tsawo. Tarihinta ya
faro ne tun 1896, lokacin da Faransa ta yi tunga a
yankin a matsayin mallakinta. A 1904, Faransa ta
mallaki kasar Upper Senegal da Yankin Nijar a
Afrika ta Yamma, inda birnin Bamako ya kasance hedikwata. Daga bisani
aka canja wa yankin suna
zuwa French Upper Volta mai hedikwata a
Wagadugu, a 1919. A shekarar 1932 aka rushe
wannan tsari, aka karkasa kasashen zuwa Ivory
Coast da Sudan da Nijar. An sake maida ta tsarin
baya a 1947, inda aka dawo da yankin Upper Volta, aka mayar mata da
iyakokinta. An ba ta
mulkin kanta a 1958, sannan aka ba ta 'yancin kai
da sunan Jamhuriyyar Upper Volta a 1960. Kamar dai yadda ta faru
a Najeriya, sojoji sun
tsoma hannunsu a mulkin Jamhuriyyar Upper Volta
a 1966, inda gwamnatin ta soja ta kare a 1976.
Sabuwar gwamnatin farar hula da ta gaji ta soja, an
tunkude ta ita ma a 1980, inda sojan suka ci gaba
da mulki zuwa 1983. Thomas Sankara da Blaise Campaore ne suka ci gaba
da mulki a kakin soja
kuma wannan gwamnatin ce ma ta canja wa kasar
suna zuwa Burkina Faso a 1984. Bayan an yi wa
Thomas Sankara kisan gilla a 1987, kasar ta samu
natsuwar mulki a karkashin Shugaban Kasa Blaise
Campaore na tsawon shekara 27. An matsa masa lamba, dole ya sauka daga
mulki a 2014. Tsohon sunan kasar na Upper Volta, an samo shi
ne daga Koramar Volta, wacce ta hade har zuwa
Kogin Atilantika, wanda ya ratsa har zuwa kasar
Ghana a yanzu. Wani Baturen Fotugal ne ya rada
mata sunan "Volta" domin ya yi la'akari da yadda ta
yi ta kwana-kwana. Koramar tana da manyan bakuna uku, Farar Volta, Jar
Volta da kuma Bakar
Volta, wanda haka ke nuna launin kasar wuraren.
Launin kasar Wagadugu ja ce kuma Jar Volta na
Arewa Maso Yammacin Wagadugu. Burkina Faso a yanzu haka tana da yawan
mutane miliyan 20, inda Wagadugu ne Fadar
Gwamnati, wanda ke kunshe da yawan mutane
kimanin miliyan 2. Birnin Kasuwancin kasar,
sunansa Bobo-Dioulasso, yawan al'ummarsa na
kasa da miliyan daya ne kuma an yi kidayar jama'a ta karshe a 1982.
Mossi ita ce kabila mai mafi yawan mutane a
kasar kuma suna da karin harshe kala biyu,
Kompela da Tenkodogo. Mutanensu sun yi suna
wajen hakuri da juriya, don haka Turawan Faransa
suka rika daukar mazansu aikin soja, kuma aka
rika ba su aikin gina hanyoyin jirgin kasa da na mota. Haka ma
matansu, ba su da son jiki, suna da
kokarin neman abinci. Ba su jin nauyi, domin za ka
gan su suna tuka babur da motocin haya a babban
birnin kasar. Suna yin noma, ban ruwa a fadamu,
aikin buga bulo ko yin aikin siminti. An taba
haramta auren mace fiye da daya a zamanin mulkin Sankara amma daga
baya gwamnatin da ta gaje shi
ta dawo da shi. Wannan ya sanya mutane da suke
daraja al'ada suka rika auren mata da yawa. Duk
macen da mijinta ya mutu, ba ta fita daga gidan
aurenta, sai dai kawai ta zabi namiji daya daga
dangin mijinta, ta sake aure. Noma, shi ne babbar sana'ar mutanen kasar.
Suna noma jar dawa da gyada, haka ma suna noma
acca. Kamar Masar da Sudan, su ma Burkina Faso
suna noma auduga mai yawa da suke sayarwa
kasashen waje. Suna da ma'aidinan zinari da azurfa
da sauransu, wadanda kasashen Australia da Afrika ta Kudu da Faransa
da Japan da Ghana da
sauransu ke amfana sosai ta hanyar hako su. Kasar
tana dogaro da agajin kasashen waje ta bangaren
tattalin arziki. Otel din Laico, wanda kuma ake kira
da Hotel Libya shi ne kusan otel mafi inganci a
Wagadugu. Marigayi Muamar Gaddafi ne ya gina shi kuma yana daya daga
cikin abin alherin da 'yan
kasar ke tuna marigayin shi da shi. Wasu daga ciki
wuraren bude ido a Wagadugu sun hada har da
'Zauren Shahidai' wanda yake kan hanyar Muamar
Gaddafi. An gina shi ne domin tunawa da mutanen
da aka rasa a hautsinin da ya faru a 2014. Masu masaukina a kasar
Burkina Faso, sun
kasance tsatson Hausawa. Kakanninsu sun yo hijira
ne daga Najeriya, musamman daga Kano,
Sakkwato, Katsina, Kebbi da sauran biranen Arewa.
Sun ce sun sauka a Upper Volta ne a matsayin 'yan
kasuwa, masaka, masunta, tun kafin zuwan Turawan Mulkin Mallaka na
Faransa. Sun ce su ne
ma tun farko suka fara kai sana'ar rini da sakar
tufafi a kasar. Har zuwa yau kuwa, irin suturunsu
ne ake alfahari da su a kasar. Akwai al'ummar Hausawa da dama a biranen
kasar Burkina Faso, suna zaune ne a
unguwanninsu da ake wa lakabi ba Zango, sunan
da aka samo a sanadiyyar kasuwancin da ya
gudana shekaru masu yawa da suka shude, inda
'yan kasuwa kan keta sahara daga wannan kasa zuwa waccan a kan rakuma.
Wuraren da suke yada
zango ne ake lakaba wa sunan unguwar ta
Hausawa. A birnin Wagadugu, an canza wa Zango
na ainahi matsuguni har sau biyu, domin kuwa
ayyukan raya birnin ya shafe shi. Zango na farko
yana kusa da tashar jirgin kasa, shi kuwa Zango na biyu, inda nan
Hausawan suka zauna tsawon
shekara 85, yana cikin kawyar birnin, nisan
kilomita biyu daga Fadar Masarautar Moogo Naaba,
Sarkin Gargajiyar Mossi; wanda suke da
kyakkyawar mu'amala da shi. A 2001, Gwamnatin
Blaise Campaore ce ta canza wa Zangon wuri zuwa inda yake yanzu, kusa
da Fadar Shugaban Kasa. Kalilan daga cikin Hausawa da suka yi
karatun
Boko, sun rike manyan mukamai a Ma'aikatun
Gwamnatin Burkina Faso da sauran wurare har ma
da wajen kasar. Daga bisani ne suka farga da
muhimmancin ilimin zamani, inda suka kafa
Kungiyar Makaranta, wacce ke taimakawa wajen fadakar da al'ummarsu,
muhimmancin da ke tattare
da ilimin na zamani. Akwai abubuwa da yawa da mutum zai nazarta
kuma ya karu a kasar Burkina Faso, duk kuwa da
cewa karamar kasa ce da ba ta da yawan
albarkatun kasa kamar wasu. Suna tafiyar da
al'amuransu a kan tsari, ga su da bin doka da oda. Moogo Naaba
(Sarkin Duniya), shi ne lakanin
Sarkin Gargajiya na Mossi da ke Wagadugu. Ana ba
shi girma da daraja sosai. Kasancewar fadarsa na a
babban birnin kasar, yana da martaba ta
musamman, duk kuwa da cewa shi ne na hudu a
tsarin martabar sarakuna a Daular Mossi ta Burkina Faso. Tarihi
ya nuna cewa Daular Mossi a Burkina Faso
ta samo asali ne tun a Karni na 7. Kamar yadda
tarihin ya tabbatar, Sarkin Gambaga na kabilar
Dagomba a Arewacin Ghana, diya mace kawai ya
haifa. Bayan ta yi aure, wata rana sai ta fita kilisa a
doki, ta shiga daji kuma ta yi makuwa. Wani maharbi dan kasar Mali ya
tsince ta kuma suka yi
aure, suka haifi da namiji. Kasancewar a kan doki
aka samu mahaifiyar jaririn, sai aka rada masa suna
Ouedraogo (sunan namijin doki ke nan a Daular
Mossi). Shi Ouedraogo ne ya zama Sarki na farko a
Daular Mossi kuma shi ne ya kafa Masarautar
Tenkodogo. Sarkin Mossi na yanzu a Wagadugu,
Naaba Booggo, shekararsa 34 ke nan a kan
karaga. Shi ne sarki na 147 a jerin sarakunan
daular. Masarautar tana daraja al'ada sosai, musamman akwai wata
al'ada da har yanzu take
wanzuwa. Kamar yadda sauran sarakunan kasar
suka rika yi, duk Jumu'a, Naaba Booggo kan shiga
sulke, ya hau doki da nufin tafiya yaki da wasu
al'umma da ke Mali. Haka za a yi ta lallashinsa, ana
ba shi hakuri, sannan ya sauko. Wannan shauki na yaki ya zama jiki a
masarautar, duk Jumu'a. Mai martaba Naaba Booggo ya amshi
bakuncin
mu mahalarta wannan muhimmin taro. Kafin mu
kai ga ganawa da shi, sai da aka yi ta kai-komo
wajen bin ka'idoji daban-daban amma duk da
haka kwalliya ta biya kudin sabulu. Mutanen
Burkina sun yi suna wajen hakuri, don haka sun dauka bakinsu ma haka
ne. Sarkin na zaune a bisa
karaga, tsakiyar butumbutumin zakoki biyu,
hakoransu a bude, gwanin ban tsoro. Da yarensu
ya yi mana jawabi, tafinta ya rika fassara mana. Ya
yi mana jawabi ne game da rainon yara, inda ya
nuna cewa zamani ya canja, don haka akwai bukatar dattawa su maida
hankali wajen kyautata
rainon yara, domin su tashi da da'a da biyayya, a
matsayin 'yan kasa nagari. Na fahimta da cewa, irin
wannan sakon ne yake isarwa ga dukkan tawagar
da ta ziyarci fadar tasa. Domin kare martabar al'adun Masarautar Mossi,
an haramta wa kowane mutum daukar hoton wani
abu a fadar masarautar ba tare da izini ba. Sarkin
dai ya karrama mu, inda ya amince muka dauki
hoto da shi a wajen fadar. Akwai wani azancin
magana da aka rubuta baro-baro a wata hasumiyar masarautar da harsuna
uku na Moore
da Djula da Fulatanci, kamar haka: "Duk inda ka ga
dattijo, da wuya a aikata ba daidai ba a wurin." Naaba Booggo,
dan kwallo ne. Babu mamaki,
watakila shi ya sanya ma aka gina babban filin
wasa na kasa kusa da fadar masarautarsa. Na samu
bayanin cewa, shahararren dan kwallon nan na
kasar Kamaru, Samuel Eto ne ya gina shingayen
karfe da suka kewaye kofar fadar sarkin saboda nuna gamsuwa da yadda
sarkin ke sha'awar
wasan kwallon kafa. Mun karu da wasu karin azancin magana a fadar
Sarkin Hausawa a Zango. Kakakin Fadar ya ambata
cewa: "Abu ne mai sauki ka ga makiyayi yana
sarrafa garken shanu da sanda guda, a yayin da
abu ne mai matukar wahala ka mulki jama'a kamar
haka." Wannan yana yi mana ishara da yadda mulki ke da wahala.
Taron kara wa juna sani da kuma bikin,
kasancewarsu na kasa-da-kasa, an gayyaci
mahalarta daga kasashen Benin, Kamaro, Afrika Ta
Tsakiya, Chadi, Ghana, Nijar, Najeriya, Togo da
kuma Sudan kuma dukkan wadannan kasashe,
akwai al'ummar Hausawa da yawa. Taron ya samu halartar baki sosai, sai
son barka, domin kuwa
sarakunan gargajiya har uku suka zo daga kasar
Togo kadai. Ba domin matsalolin sufuri da ke
addabar nahiyar Afrika ba, da an samu mahalarta
taron fiye da kima. Amma duk da haka, taron ya
samu yabo daga mahalarta, a yayin da kasashen Togo da Senegal suka
dauki alkawarin shirya irinsa
a nan gaba. Tafiya ta jirgin sama daga Abuja zuwa
Wagadugu akwai wahala. An ba ni shawarar in
shiga jirgi zuwa Kairo (Masar), ko kuma in bi ta
wasu kasashen ma da ba na Afrika ba domin zuwa
Wagadugu. Hanya mafi gajarta, ita ce ta Lome
(Togo) ko Abdijan (Kwaddabuwa) kuma sai mutum ya kwana biyu a hanya.
Matafiya daga
Najeriya da suka biyo ta hanyar mota, sai da suka yi
kwana uku, sun yada zango a Maradi da Yamai
(Jamhuriyyar Nijar), sannan suka isa Wagadugu a
rana ta ukun saboda jidalin bincike-binciken
jami'an tsaro a iyakokin kasashen. Kodayake duk da wannan
jidalin, tafiya ta mota
na tattare da nishadi, domin kuwa mutum zai karu
sosai da sababbin abubuwa a hanya, na mutane iri-
iri da kuma wurare. Ta fannin gane-gane a hanya
kuwa, masu tafiya ta jirgi ma sun karu, domin kuwa
mutum zai samu damar ganin falalen kasa, da itatuwa nan da can da
hanyoyin kasa marasa
kwalta da kuma gidaje warwatse, nan da can. Lallai
akwai yalwar kasa, wacce ya kamata a aikata ta,
domin ceto ta daga balbalcewa. Na yi hira da wasu abokan tafiyata, wadanda
suka bayyana abubuwan burgewa game da
Najeriya. A jirgin da na shiga zuwa Abdijan zuwa
Wagadugu, wani tsohon malamin Kwalejin Fourah
Bay, Saliyo ya bayyana takaicinsa game da Najeriya.
Ya bayyana yadda Allah Ya albarkaci Najeriya da albarkatun kasa amma
saboda halin ko-in-kula na
al'ummar kasar, an kasa amfana. Domin kawo
gyara, ya ce 'Najeriya na bukatar shugaba mai
nuna karfa-karfa, amma ba mai zuciyar kisa ba.' Haka kuma mun
tattauna kan al'amuran da suka
shafi 'yancin dan Adam, musamman sakamakon
yadda wasu mutum biyu suka rika cacar baki da
juna. Daya daga cikinsu ma Bature ne. Wani mutum
ne da ke zaune a bayan Baturen, yake ta magana a
waya da karfi, shi ne Baturen ya kasa daurewa, ya shiga damuwa sosai,
ya yi korafi. Shi kuma mai
waya sai ya harzuka, ya maida masa martani mai
kaushi, sai suka fara fada. Kafin ka ce kwabo, sai
fadan ya girma har da zage-zagen juna, kowa na
nuna cewa shi ke da gaskiya. Baturen ya roki
ma'aikacin jirgin da ya sanya baki amma hakan ba ta samu ba. Haka suka
ci gaba da cacar bakinsu,
har suna cewa za su dambace, da zarar sun sauka
daga jirgin. Duk dai a cikin jirgin nan, wasu fasinjoji biyu,
daya dattijo, daya kuma budurwa ce, su ma sun yi
nasu wasan kwaikwayon. Dattijon ne yake ta buga
kwamfutarsa (laptop) abinsa, sai ita kuma matar ta
yi korafin cewa gwiwar hannunsa na tunkurinta.
Shi kuma mutumin ya yi biris da ita. Haka abin ya ci gaba, ba a samu
maslaha ba sai da matar ta canja
wurin zama. Babu shakka akwai darussa daga abubuwan
nan da suka faru. Wani babban darasi daya a nan
shi ne, a lokacin da mutum ke neman kare
hakkinsa, yana da kyau ya yi la'akari da hakkin
sauran mutane. Idan na kalli wadannan al'amura
da suka faru a jirgi kuma na duba dalilin da ya sanya aka gayyace ni
zuwa Burkina Faso domin a
karrama ni, sai na fahimta da cewa a rayuwa muna
bukatar mu kasance masu fahimtar juna, mu daraja
ra'ayin juna a mu'amala, mu daraja al'adu da
ra'ayoyin juna kuma mu yi iyaka kokarinmu wajen
wanzar da zaman lafiya a tsakanin al'umma. Dokta Bukar Usman,
marubuci ne kuma
tsohon Babban-Sakatare a Fadar Shugaban

No comments:

Post a Comment