0
Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya
+2348065025820
abuhidya3@gmail.com

GABATARWA
Wannan shi ne kundin kudiri na gamayyar tunanin kafar turakun siyasar
'yan kasuwa a jihar Kano wanda ya dunkule yadda za a gabatar da tsari
da manufofin kudirin wannan tafiya bisa aminci da yarda.

TARIHIN KASUWANCI A KANO DA ZUWAN 'YAN KASUWA LARABAWA DA WASUN SU.
Kafin bayyana waccan tsari da aka fada a sama yana da kyau a dan dubi
tarihin kasuwan a wannan babbar jiha ta Kano. A shekara ta 1453
miladiyya, a zamanin Sarkin Kano Yakubu dan Abdullahi Barja, Sarkin
Kano na goma sha shida(16)a mulkin kanawa, wadansu Larabawa mutanen
kasar Gadamus masu fatauci, suka zo daga Turabulus(Libya), suka sauka
a birnin Kano, su ne Larabawan da suka fara zuwa Kano. Da saukar
wadannan fataken Larabawa, suka je wurin sarkin Kano Malam Yakubu, a
jujin 'Yan Labu, a lokacin ba a gina gidan sarautar Kano na yanzu ba,
Shamakin Kano Korau, yana shigar da su gaban sarki, suka ce da Sarki a
cikin harshen Larabci su fatake ne, suna so su zauna a Kano, domin su
yi ciniki.

A wannan Lokaci kuwa, limamin Kano Muhammadu Hashimu, shi ne yake
fassara wa Sarkin Kano abin da wadannan Larabawa suke fada cikin
harshen Hausa. Daga nan Sarkin Kano Yakubu ya yi farin ciki kwarai da
gaske da wadannan larabawa, sannan yace da Shamakin Kano, ya kai su
sararin nan na yamma da Unguwar Garke wato Dandali, su yi gidaje su
zauna a can. Saboda wadannan Larabawa suna da jar fata, sai mutane
suka sa musu suna Turawa. Ya yin da wadannan Fatake Larabawa suka yi
gidaje a wannan wuri suka zazzauna, sai Kanawa suka sa wa wannan
unguwa suna Dandalin Turawa, dalilin sunan Dandalin Turawa ta yanzu ke
nan, tun shekarar 553.

A waccan zamani, sarkin Kano yana da shekara daya a kan gadon sarautar
Kano. A zamaninsa Kano ta karu da arziki mai yawa da kuma garuruwa
ko'ina, a kowane gari, akwai makarantu na Al'kur'ani Mai Girma Har Ila
yau, kuma a kowane gari, akwai karofi da Mabugai da Masaku da Makera
da Dukawa, (Wato wurin Dukanci) da majema,(Wato wurin yin jima) da
kuma masassakan turmi da akusa, ko'ina sun yawaita a kasar Kano.
Tun daga waccan zamani Larabawa suka ci gaba da zuwa Kano, kamar
Yamalawa(Mutanen Yaman) da Larabawan Tunis, amma kowane da nau'in
kasuwancinsa. Su Larabawan Libiya duk kayan da suke sayarwa kayan
alatu ne(Suturu da kayan kamshi da kayan zaki).
Da wahala a ce ga lokacin asalin samuwar Kasuwanci a Kano. A zamanin
da, mutanen da ke Kano ba su san wata harka ta Kasuwanci ba, sai dai
sun fi mayar da hankali a kan aikin gona da aikin lambu. Amma an sani
cewa sana'o'inmu na Hausa wato sana'o'in gargajiya kamar su rini da
jima da kira da saka da sauransu, su suka haifar da ainihin samuwar
kasuwanci, domin kuwa a wancan zamanin mutum zai yi abu ya sayar don
amfanin jama'ar kasarsa, ko da yake lokacin da ba a fara amfani da
kudi a Kano ba, ana yin amfani da wata hanya ta ba ni gishiri in baka
manda (cinikin furfure ) don cinikayya.

Daga baya ne lokacin da fatake Larabawa ko Asbinawa da Agalawa suka zo
Kano, Kasuwanci ya fara Kankama. Haka kuma lokacin fataucin Kasar
Hausa, wato lokacin da abubuwan zirga-zirga na zamani ba su iso kano
ba, za mu iya cewa Kasuwanci ya samu kwarai a Kano, dangane da tawayen
da fatake suka yi wa kasar Katsina, suka dawo kasar Kano da sha'anin
Kasuwanci, kamar yadda aka fada a cikin littafi mai suna (Kano Civil
War and the Britshi Over Rule 1882-1940) na Muhammad F.A wannan ya
kawo mu har lokacin zuwan Turawa, wato lokacin da suka zo mana da
farin kudi a shekarar 1930, har aka fara amfani da shi a harkar
cinikayya ta Kano. Wannan ya sa kasuwanci ya dada samuwa kwarai a
Kano, ta hanyar bude ido da abin da Turawa suka zo da shi a sha'anin
kasuwanci, wanda ya kai jama'ar Kano suka san mene ne kasuwancin ma
kansa, har su tafiyar da sha'anin kasuwanci kansa, ba tare da wasu
Turawa sun ja musu gaba ba. Samuwar wannan kasuwanci a Kano ya fito
da Kano a idanun duniya baki daya, wanda har ta kai ga yi mata kirari
kamar haka, "Kano tumbin Giwa, ko da me ka zo an fika".

TASIRIN 'YAN KASUWA A NIJERIYA
Idan mun lura za mu ga ne cewa yan kasuwa suna da tasiri kwarai da
gaske a jihohin Nijeriya da kasa baki daya, musamman jihar Kano wadda
ake yi wa kirari da cibiyar kasuwancin afrika. Kuma manyan yan kasuwar
da suke baiwa kasa kayan masarufi da al'muran yau da kullum daga Kano
suke, dukkan wani kasuwanci a yau baya samun karbuwa matukar babu shi
a jihar Kano, duba da bayanan da suka gabata a baya za mu yarda da
cewa Kano ta zama tumbin giwa komai ka nema akwai a ciki.
'Yan kasuwa masu sha'awar kasuwa daga sassa daban-daban na duniya a
kullum shiga jihar Kano suke don tallata hajarsu, a saboda haka muna
iya cewa kano ta 'yan kasuwa ce.

YUNKURIN 'YAN KASUWA WAJEN KAFA MULKIN DIMOKARADIYA A NIJERIYA.
A yau idan ka raba mutanen Nijeriya kaso goma to kaso shida duka 'yan
kasuwa ne, ragowar kashin ne za a rabawa ma'aikatan gwamnati da sauran
sassa. Bisa kididdiga ko bincike da mu ka yi mun samu nasarar gano a
duk unguwa a Nijeriya cikin kowane gida matukar mutanen cikin sun
haura biyar sai ka samu dan kasuwa a ciki, kama daga masu sana'ar
sayar da Kosai, kitso, mai, Kanti, Shayi, shagunan kayan gyara da na
masarufi da suturu da sauransu.
Har ila yau wadannan mutane su ne suke tururuwa lokacin gudanar da har
zabe don zabar shugabanni 'yan boko wadanda za su jagorance su don
kawo musu ci gaba a har kasuwancinsu da bunkasarsa amma a wasu lokaci
harkar su ba ta cimma ruwa, wani sa'in ma sai a biyo su da neman su
biya haraji bayan ba su samu ribar zaben da suka yi ba, haka kuma
lokacin zabe wadannan yan siyasa za su sake wanke rigunansu su shigo
cikin al'ummar da ta zabe su wadanda mafi akasarinsu 'yan kasuwa ne su
ce a kara zabarsu karo na gaba, haka dai za su kara komawa bisa
matsayinsu ba tare da kawo wani babban ci gaba ba a harkar kasuwancin,
wanda kuma shi ne yake rike da kasar ma baki daya.

KAFA TSARIN SHUGABANCIN 'YAN KASUWA NA JIHA DA KANANAN HUKUMOMI.
A saboda wadancan dalilai na rashin samun tagomashin ribar romon
dimokaradiya da 'yan kasuwa ba sa yi ya sanya suka ga dacewar su kafa
gwamnatin da za su ji koken junansu da na sauran al'umma don ci gaban
kasuwanci da masana'antu a jiha da kasa baki daya.

Ga Yadda tsarin zai kasance
idan har kowani mai karamin sana'a zai iya aje wani abu daga cikin
abin da yake samu don bunkasar kasuwancinsa da goyon bayan wannan
tafiya, misali a ce ko wani mai sana'a a jihar kano zai a je Naira
dari(100) a wata don bayarwa a yankin da yake a matakin karamar hukuma
zuwa jiha to za a samu adadin abin ake so na kafa gwamnati da sauran
hidindimun da za su sanya kowa ya fahimci cewa "Daminar bana ta dara
ta bara"
don haka a wannan tsari za a kafa ofishi da zai kula da adadin 'yan
kasuwar da suke a kowacce karamar hukuma kuma za a yi wa kowa rijista
wacce za ta game duka yan kasuwar jihar Kano a inuwa daya yadda ko
wani tsunsu zai yi kukan gidansu.
Ta yadda za a zama tsintsiya madaurinki daya.

MATAKIN DA ZA A SANAR DA TSARIN
1-Za a yi amfani da kafafen yada labarai don sanar da wannan yunkuri.
2- Za a radawa tsarin suna yadda amonsa zai mamaye jiha da kasa baki daya.
3- Za a kafa tsarin shugabanci tun daga jiha har kananan hukumomi.
4-A karkashin wannan tsari za a fitar da shugabanin ta za su yi
takarar kujerun da ake bukata don biyan bukatar al'ummar kasa.

KARSHE
Ana fata wannan tsari ya zama kawo ci gaban da zai mayar da kasar
Nijeriya sama da kasashen da ake ganin sun taso tare amma sun fita ci
gaba.


On 11/23/17, Rabiu Muhammad Abu Hidaya <abuhidya3@gmail.com> wrote:
> Daga
> Rabi'u Muhammad Abu Hidaya Masarautar Bande wadda ta kasance masarauta
> mai dadadden tarihi cikin masarautun kasar Nijar ta
> samu sabon sarki bayan rasuwar tsohon sarkin
> garin,
> sarkin dai mai suna Abubakar Yahaya Lushe ya
> kasance shi ne sarki na bakwai a jerin sarakunan da suka mulki kasar
> ya kuma matashi ne jami'i a
> aikin Soja mai mukamin Kanal wanda ya bar aikin
> sojan don maye gurbin mahaifinsa domin shi
> mutum ne mai son ci gaban al'ummar kasarsa, ya
> samu zama sarkin ne bayan da masu ruwa da tsaki
> suka zabe shi a matsayin wanda zai gaji mahaifinsa da ya rasu kwanaki
> kadan baya, wannan zabi da
> aka yi masa dai ya faranta ran mafi yawa daga cikin
> jama'ar garin Bande da na masarautar, inda
> dukkansu su ka yi maraba da shi, domin sun
> tabbatar da cewa sabon sarkin na su yana da halin
> girma da dattako irin na mahaifinsa. A lokacin da sarkin yake jawabi
> game da kudirin
> da zai gabatar a masarautar da ya gada daga
> mahaifinsa ya ce "zai fi mayar da hankali ne game
> da abin ya shafi Ilimi a kasar da kuma harkar
> kasuwanci tare da wasannin gargajiya wadanda ya
> ce an yi musu nisa a sauran gurare. Ya kuma ce zai karfafa alaka da
> sauran masarautun
> da suke sauran kasashen da suke makotaka da
> masarautarsa"
> har ila yau da yake ci gaba da jawabi ya ce
> masarautarsa tana maraba da duk wani da yake da
> son ci gaban al'umma kuma zai yi hadin gwiwa da duk wanda da yake da
> harkar kasuwanci, haka
> kuma yace game da abin da ya shafi noma kiwo
> gami da kiwon lafiya nan ma ba za a bar kasar
> bande a baya ba, lallai a karkashin masarautarsa za
> a samu ci gaba sosai, babban burin wannan sabon
> sarki dai ya ce bai wuce ya samu hadin kan jama'ar kasarsa ba sannan
> yana fatan a ce ya fi mahaifinsa
> kokari.
> A nasa jawabin wani malamin Makaranta kuma na
> kusa da masarautar ya ce" lallai suna alfahari da
> wannan sarki wanda suke ganinsa tamkar
> mahaifinsa domin mahaifinsa ya zauna da kowa lafiya da ya kuma kaunaci
> talakawansa tamkar a
> 'yayan cikinsa shi mutum ne mai son talakawan
> kasarsa, kuma ya tabbatar da cewa wannan sarki
> zai kawo ma kasar Bande gagarumin ci gaba.
> A karshe mafi yawa daga cikin jama'ar kasar suna
> ta tururuwa domin yin mubaya'a ga sabon sarkin na su Abubakar Yahaya
> Lushe har ila yau kuma
> mutane da dama suna ta fatan ganin ranar da za a
> yi bikin ba shi sandar mulki domin su nuna masa
> soyayya da kauna.
>
> On 11/23/17, Rabiu Muhammad Abu Hidaya <abuhidya3@gmail.com> wrote:
>> ALMARA KO GASKE?
>>
>> Daga
>> Rabi'u Muhammad Abu Hidaya
>>
>>
>> Al'ada ta ce duk karshen mako na kan kai ziyara garinmu, domin gaishe
>> da iyaye, 'yan'uwa da
>> abokan arziki.
>> A garin akwai wata kasuwa da
>> ta ke ci duk ranar juma'a, kasancewata mutum ne mai son shan fura, don
>> haka duk ranar kasuwar garin na kan shiga kasuwar domin sayan fura,
>> akwai wata budurwar bafulatana, mai suna Hajjo, Hajjo tana da kirki
>> kwarai don haka ne ma, babu furar wadda da nake sha kaf
>> kasuwar sai ta ta, mun saba da Hajjo matukar sabo, domin idan na je
>> gurinta sam ba ta iya sakewa
>> saboda tsananin jin kunya.
>> So! shu'umi ya kan shiga zuciya ba tare da ya yi sallama ba. A kwana a
>> tashi sai na fara jin son Hajjo mai fura ya shiga zuciyata, domin har
>> ta kai idan na dawo kano bana iya sakewa in yi ayyukana yadda ya
>> kamata, haka zan ta fatan karshen mako ya yi na je garin, ban samu
>> nutsuwa ba sai da na bayyanawa Hajjo abin da yake raina, na ci sa'a
>> domin a karon farko Hajjo ta amince da ni a matsayin saurayinta.
>> Watarana ina kasuwa a cikin rumfar da Hajjo take sayar da fura muna
>> hira ina shan furar da ta dama min, sai nake
>> tambayarta Hajjo ya kamata a ce nasan gidanku
>> domin in zo mu yi maganar aure, shiru ta yi na 'yan
>> mintoci gami da aje ludayin furar da ke hannunta tare da sunkuyar da
>> kai kasa na dan wani lokaci, kana daga bisani sai ta ja wani dogon
>> numfashi! Gami da kallon wata yarinya da ke zaune a gefenta bisa wani
>> dutse tana sayar da mandako. Ko ba ki son in zo gidan ku ne? A'a kawai
>> dai ina wani dan tunani ne. Wai don Allah da gaske ka ke
>> kana so na?
>> (Dariya) ina sonki mana Hajjo. Amma me ya sa kika
>> min wannan tambayar?
>> Ai gani na yi kai dan birni
>> ne, me za ka yi da 'yar kauye iri na?Dariya na sake yi sannan na ce
>> mata kar ki damu Hajjo
>> ko ma ya ki ke ina sonki a haka kuma aurenki zan yi.
>> A karshe Hajjo ta kwatanta mini
>> rugar su, ranar Asabar ranar ce mu ka yi da Hajjo zan je rugar su.
>> Da misalin hudu da rabi na
>> yammacin ranar Asabar na shiga rugar su Hajjo, ban sha wata wahala ba
>> wajen neman gidansu ba, domin rugar ta su ba ta da girma sosai. Hajjo
>> tana gani na ta yi ta murna kamar ta rungume ni don tsananin jin dadi,
>> kusan duka mutanen gidan su Hajjo sai da suka zo muka gaisa tare da
>> nuna farin cikinsu da gani na.
>> Fura da nono mai kyau Hajjo ta kawo min, na kuma ji dadin furar
>> gaskiya kauye akwai dadi musamman rugagen fulani ba ruwansu ga yanayi
>> mai dadi ga kuma nono mai kyau ka sha iya shanka ba ka da damuwa.
>> Abu ka ga garinmu kauye ko?
>> Hajjo kenan, ai garin nan naku ina ganin bayan mun yi aure a nan za mu
>> zauna saboda ya min kyau.
>> Cikin jin dadi Hajjo ta rufe fuska da hannayenta tana murmushi alamun
>> jin kunya, kana ta ce haba dai ashe za ka iya zaman kauye?
>> Bayan na hadiye wani gayan fura tare lashe baki kai da ka gan ni kasan
>> ina jin dadin furar da nake sha, sai na bata amsa na ce ban da abin ki
>> Hajjo ai ko shugaban kasa zai so zama a nan ko don shan fura da nonon
>> da ke rugar nan.
>> Wannan karon dariya Hajjo ta yi har da kyakyatawa kana ta ce" gaskiya
>> Abu furar nan ta kama ka da kyau har da santi haka.
>> A ranar mun yi hira sosai kuma hira mai dadi da ita, sannan a karshe
>> mu ka yi bankwana tare da alkawarin kwanaki kadan masu zuwa zan sake
>> dawowa.
>>
>> KARO NA BIYU A RUGAR SU HAJJO
>> Daga ina ka ke?
>> Wa kake nema?
>> Yanzu ba mu da Hajjo a wannan gidan, Hajjonmu yau kimanin shekarunta
>> bakwai da rasuwa. Abin da aka shaida min kenan
>> bayan na koma rugar su Hajjo a karo na biyu.
>> Ikon Allah sai kallo, abin da ya fi bani mamaki shi ne duk mutanen
>> gidan su Hajjo babu wanda ya nuna ya ta6a ganina balle
>> mai kamata, na yi musu bayanin kamanin Hajjo sun tabbatar min ita ce
>> hasalima sun kawo min
>> hotunanta inda ni ma na tabbatar musu cewa ita din ce.
>> Cikin tsananin mamaki da kaduwa haka na baro rugar su Hajjo duk jiki
>> na ya yi sanyi.
>> Tun daga wannan ranar idanuna ba su sake tozali
>> da Hajjo ba balle mai kamarta. Kuma har yanzu zuciyata na cike da
>> matsananciyar kaunarta...
>>
>

Post a Comment

Dear readers, after reading the Content please ask for advice and to provide constructive feedback Please Write Relevant Comment with Polite Language.Your comments inspired me to continue blogging. Your opinion much more valuable to me. Thank you.

YUNKURIN 'YAN KASUWA WAJEN KAFA MULKIN DIMOKARADIYA A NIJERIYA.

Daga Rabiu Muhammad Abu Hidaya
+2348065025820
abuhidya3@gmail.com

GABATARWA
Wannan shi ne kundin kudiri na gamayyar tunanin kafar turakun siyasar
'yan kasuwa a jihar Kano wanda ya dunkule yadda za a gabatar da tsari
da manufofin kudirin wannan tafiya bisa aminci da yarda.

TARIHIN KASUWANCI A KANO DA ZUWAN 'YAN KASUWA LARABAWA DA WASUN SU.
Kafin bayyana waccan tsari da aka fada a sama yana da kyau a dan dubi
tarihin kasuwan a wannan babbar jiha ta Kano. A shekara ta 1453
miladiyya, a zamanin Sarkin Kano Yakubu dan Abdullahi Barja, Sarkin
Kano na goma sha shida(16)a mulkin kanawa, wadansu Larabawa mutanen
kasar Gadamus masu fatauci, suka zo daga Turabulus(Libya), suka sauka
a birnin Kano, su ne Larabawan da suka fara zuwa Kano. Da saukar
wadannan fataken Larabawa, suka je wurin sarkin Kano Malam Yakubu, a
jujin 'Yan Labu, a lokacin ba a gina gidan sarautar Kano na yanzu ba,
Shamakin Kano Korau, yana shigar da su gaban sarki, suka ce da Sarki a
cikin harshen Larabci su fatake ne, suna so su zauna a Kano, domin su
yi ciniki.

A wannan Lokaci kuwa, limamin Kano Muhammadu Hashimu, shi ne yake
fassara wa Sarkin Kano abin da wadannan Larabawa suke fada cikin
harshen Hausa. Daga nan Sarkin Kano Yakubu ya yi farin ciki kwarai da
gaske da wadannan larabawa, sannan yace da Shamakin Kano, ya kai su
sararin nan na yamma da Unguwar Garke wato Dandali, su yi gidaje su
zauna a can. Saboda wadannan Larabawa suna da jar fata, sai mutane
suka sa musu suna Turawa. Ya yin da wadannan Fatake Larabawa suka yi
gidaje a wannan wuri suka zazzauna, sai Kanawa suka sa wa wannan
unguwa suna Dandalin Turawa, dalilin sunan Dandalin Turawa ta yanzu ke
nan, tun shekarar 553.

A waccan zamani, sarkin Kano yana da shekara daya a kan gadon sarautar
Kano. A zamaninsa Kano ta karu da arziki mai yawa da kuma garuruwa
ko'ina, a kowane gari, akwai makarantu na Al'kur'ani Mai Girma Har Ila
yau, kuma a kowane gari, akwai karofi da Mabugai da Masaku da Makera
da Dukawa, (Wato wurin Dukanci) da majema,(Wato wurin yin jima) da
kuma masassakan turmi da akusa, ko'ina sun yawaita a kasar Kano.
Tun daga waccan zamani Larabawa suka ci gaba da zuwa Kano, kamar
Yamalawa(Mutanen Yaman) da Larabawan Tunis, amma kowane da nau'in
kasuwancinsa. Su Larabawan Libiya duk kayan da suke sayarwa kayan
alatu ne(Suturu da kayan kamshi da kayan zaki).
Da wahala a ce ga lokacin asalin samuwar Kasuwanci a Kano. A zamanin
da, mutanen da ke Kano ba su san wata harka ta Kasuwanci ba, sai dai
sun fi mayar da hankali a kan aikin gona da aikin lambu. Amma an sani
cewa sana'o'inmu na Hausa wato sana'o'in gargajiya kamar su rini da
jima da kira da saka da sauransu, su suka haifar da ainihin samuwar
kasuwanci, domin kuwa a wancan zamanin mutum zai yi abu ya sayar don
amfanin jama'ar kasarsa, ko da yake lokacin da ba a fara amfani da
kudi a Kano ba, ana yin amfani da wata hanya ta ba ni gishiri in baka
manda (cinikin furfure ) don cinikayya.

Daga baya ne lokacin da fatake Larabawa ko Asbinawa da Agalawa suka zo
Kano, Kasuwanci ya fara Kankama. Haka kuma lokacin fataucin Kasar
Hausa, wato lokacin da abubuwan zirga-zirga na zamani ba su iso kano
ba, za mu iya cewa Kasuwanci ya samu kwarai a Kano, dangane da tawayen
da fatake suka yi wa kasar Katsina, suka dawo kasar Kano da sha'anin
Kasuwanci, kamar yadda aka fada a cikin littafi mai suna (Kano Civil
War and the Britshi Over Rule 1882-1940) na Muhammad F.A wannan ya
kawo mu har lokacin zuwan Turawa, wato lokacin da suka zo mana da
farin kudi a shekarar 1930, har aka fara amfani da shi a harkar
cinikayya ta Kano. Wannan ya sa kasuwanci ya dada samuwa kwarai a
Kano, ta hanyar bude ido da abin da Turawa suka zo da shi a sha'anin
kasuwanci, wanda ya kai jama'ar Kano suka san mene ne kasuwancin ma
kansa, har su tafiyar da sha'anin kasuwanci kansa, ba tare da wasu
Turawa sun ja musu gaba ba. Samuwar wannan kasuwanci a Kano ya fito
da Kano a idanun duniya baki daya, wanda har ta kai ga yi mata kirari
kamar haka, "Kano tumbin Giwa, ko da me ka zo an fika".

TASIRIN 'YAN KASUWA A NIJERIYA
Idan mun lura za mu ga ne cewa yan kasuwa suna da tasiri kwarai da
gaske a jihohin Nijeriya da kasa baki daya, musamman jihar Kano wadda
ake yi wa kirari da cibiyar kasuwancin afrika. Kuma manyan yan kasuwar
da suke baiwa kasa kayan masarufi da al'muran yau da kullum daga Kano
suke, dukkan wani kasuwanci a yau baya samun karbuwa matukar babu shi
a jihar Kano, duba da bayanan da suka gabata a baya za mu yarda da
cewa Kano ta zama tumbin giwa komai ka nema akwai a ciki.
'Yan kasuwa masu sha'awar kasuwa daga sassa daban-daban na duniya a
kullum shiga jihar Kano suke don tallata hajarsu, a saboda haka muna
iya cewa kano ta 'yan kasuwa ce.

YUNKURIN 'YAN KASUWA WAJEN KAFA MULKIN DIMOKARADIYA A NIJERIYA.
A yau idan ka raba mutanen Nijeriya kaso goma to kaso shida duka 'yan
kasuwa ne, ragowar kashin ne za a rabawa ma'aikatan gwamnati da sauran
sassa. Bisa kididdiga ko bincike da mu ka yi mun samu nasarar gano a
duk unguwa a Nijeriya cikin kowane gida matukar mutanen cikin sun
haura biyar sai ka samu dan kasuwa a ciki, kama daga masu sana'ar
sayar da Kosai, kitso, mai, Kanti, Shayi, shagunan kayan gyara da na
masarufi da suturu da sauransu.
Har ila yau wadannan mutane su ne suke tururuwa lokacin gudanar da har
zabe don zabar shugabanni 'yan boko wadanda za su jagorance su don
kawo musu ci gaba a har kasuwancinsu da bunkasarsa amma a wasu lokaci
harkar su ba ta cimma ruwa, wani sa'in ma sai a biyo su da neman su
biya haraji bayan ba su samu ribar zaben da suka yi ba, haka kuma
lokacin zabe wadannan yan siyasa za su sake wanke rigunansu su shigo
cikin al'ummar da ta zabe su wadanda mafi akasarinsu 'yan kasuwa ne su
ce a kara zabarsu karo na gaba, haka dai za su kara komawa bisa
matsayinsu ba tare da kawo wani babban ci gaba ba a harkar kasuwancin,
wanda kuma shi ne yake rike da kasar ma baki daya.

KAFA TSARIN SHUGABANCIN 'YAN KASUWA NA JIHA DA KANANAN HUKUMOMI.
A saboda wadancan dalilai na rashin samun tagomashin ribar romon
dimokaradiya da 'yan kasuwa ba sa yi ya sanya suka ga dacewar su kafa
gwamnatin da za su ji koken junansu da na sauran al'umma don ci gaban
kasuwanci da masana'antu a jiha da kasa baki daya.

Ga Yadda tsarin zai kasance
idan har kowani mai karamin sana'a zai iya aje wani abu daga cikin
abin da yake samu don bunkasar kasuwancinsa da goyon bayan wannan
tafiya, misali a ce ko wani mai sana'a a jihar kano zai a je Naira
dari(100) a wata don bayarwa a yankin da yake a matakin karamar hukuma
zuwa jiha to za a samu adadin abin ake so na kafa gwamnati da sauran
hidindimun da za su sanya kowa ya fahimci cewa "Daminar bana ta dara
ta bara"
don haka a wannan tsari za a kafa ofishi da zai kula da adadin 'yan
kasuwar da suke a kowacce karamar hukuma kuma za a yi wa kowa rijista
wacce za ta game duka yan kasuwar jihar Kano a inuwa daya yadda ko
wani tsunsu zai yi kukan gidansu.
Ta yadda za a zama tsintsiya madaurinki daya.

MATAKIN DA ZA A SANAR DA TSARIN
1-Za a yi amfani da kafafen yada labarai don sanar da wannan yunkuri.
2- Za a radawa tsarin suna yadda amonsa zai mamaye jiha da kasa baki daya.
3- Za a kafa tsarin shugabanci tun daga jiha har kananan hukumomi.
4-A karkashin wannan tsari za a fitar da shugabanin ta za su yi
takarar kujerun da ake bukata don biyan bukatar al'ummar kasa.

KARSHE
Ana fata wannan tsari ya zama kawo ci gaban da zai mayar da kasar
Nijeriya sama da kasashen da ake ganin sun taso tare amma sun fita ci
gaba.


On 11/23/17, Rabiu Muhammad Abu Hidaya <abuhidya3@gmail.com> wrote:
> Daga
> Rabi'u Muhammad Abu Hidaya Masarautar Bande wadda ta kasance masarauta
> mai dadadden tarihi cikin masarautun kasar Nijar ta
> samu sabon sarki bayan rasuwar tsohon sarkin
> garin,
> sarkin dai mai suna Abubakar Yahaya Lushe ya
> kasance shi ne sarki na bakwai a jerin sarakunan da suka mulki kasar
> ya kuma matashi ne jami'i a
> aikin Soja mai mukamin Kanal wanda ya bar aikin
> sojan don maye gurbin mahaifinsa domin shi
> mutum ne mai son ci gaban al'ummar kasarsa, ya
> samu zama sarkin ne bayan da masu ruwa da tsaki
> suka zabe shi a matsayin wanda zai gaji mahaifinsa da ya rasu kwanaki
> kadan baya, wannan zabi da
> aka yi masa dai ya faranta ran mafi yawa daga cikin
> jama'ar garin Bande da na masarautar, inda
> dukkansu su ka yi maraba da shi, domin sun
> tabbatar da cewa sabon sarkin na su yana da halin
> girma da dattako irin na mahaifinsa. A lokacin da sarkin yake jawabi
> game da kudirin
> da zai gabatar a masarautar da ya gada daga
> mahaifinsa ya ce "zai fi mayar da hankali ne game
> da abin ya shafi Ilimi a kasar da kuma harkar
> kasuwanci tare da wasannin gargajiya wadanda ya
> ce an yi musu nisa a sauran gurare. Ya kuma ce zai karfafa alaka da
> sauran masarautun
> da suke sauran kasashen da suke makotaka da
> masarautarsa"
> har ila yau da yake ci gaba da jawabi ya ce
> masarautarsa tana maraba da duk wani da yake da
> son ci gaban al'umma kuma zai yi hadin gwiwa da duk wanda da yake da
> harkar kasuwanci, haka
> kuma yace game da abin da ya shafi noma kiwo
> gami da kiwon lafiya nan ma ba za a bar kasar
> bande a baya ba, lallai a karkashin masarautarsa za
> a samu ci gaba sosai, babban burin wannan sabon
> sarki dai ya ce bai wuce ya samu hadin kan jama'ar kasarsa ba sannan
> yana fatan a ce ya fi mahaifinsa
> kokari.
> A nasa jawabin wani malamin Makaranta kuma na
> kusa da masarautar ya ce" lallai suna alfahari da
> wannan sarki wanda suke ganinsa tamkar
> mahaifinsa domin mahaifinsa ya zauna da kowa lafiya da ya kuma kaunaci
> talakawansa tamkar a
> 'yayan cikinsa shi mutum ne mai son talakawan
> kasarsa, kuma ya tabbatar da cewa wannan sarki
> zai kawo ma kasar Bande gagarumin ci gaba.
> A karshe mafi yawa daga cikin jama'ar kasar suna
> ta tururuwa domin yin mubaya'a ga sabon sarkin na su Abubakar Yahaya
> Lushe har ila yau kuma
> mutane da dama suna ta fatan ganin ranar da za a
> yi bikin ba shi sandar mulki domin su nuna masa
> soyayya da kauna.
>
> On 11/23/17, Rabiu Muhammad Abu Hidaya <abuhidya3@gmail.com> wrote:
>> ALMARA KO GASKE?
>>
>> Daga
>> Rabi'u Muhammad Abu Hidaya
>>
>>
>> Al'ada ta ce duk karshen mako na kan kai ziyara garinmu, domin gaishe
>> da iyaye, 'yan'uwa da
>> abokan arziki.
>> A garin akwai wata kasuwa da
>> ta ke ci duk ranar juma'a, kasancewata mutum ne mai son shan fura, don
>> haka duk ranar kasuwar garin na kan shiga kasuwar domin sayan fura,
>> akwai wata budurwar bafulatana, mai suna Hajjo, Hajjo tana da kirki
>> kwarai don haka ne ma, babu furar wadda da nake sha kaf
>> kasuwar sai ta ta, mun saba da Hajjo matukar sabo, domin idan na je
>> gurinta sam ba ta iya sakewa
>> saboda tsananin jin kunya.
>> So! shu'umi ya kan shiga zuciya ba tare da ya yi sallama ba. A kwana a
>> tashi sai na fara jin son Hajjo mai fura ya shiga zuciyata, domin har
>> ta kai idan na dawo kano bana iya sakewa in yi ayyukana yadda ya
>> kamata, haka zan ta fatan karshen mako ya yi na je garin, ban samu
>> nutsuwa ba sai da na bayyanawa Hajjo abin da yake raina, na ci sa'a
>> domin a karon farko Hajjo ta amince da ni a matsayin saurayinta.
>> Watarana ina kasuwa a cikin rumfar da Hajjo take sayar da fura muna
>> hira ina shan furar da ta dama min, sai nake
>> tambayarta Hajjo ya kamata a ce nasan gidanku
>> domin in zo mu yi maganar aure, shiru ta yi na 'yan
>> mintoci gami da aje ludayin furar da ke hannunta tare da sunkuyar da
>> kai kasa na dan wani lokaci, kana daga bisani sai ta ja wani dogon
>> numfashi! Gami da kallon wata yarinya da ke zaune a gefenta bisa wani
>> dutse tana sayar da mandako. Ko ba ki son in zo gidan ku ne? A'a kawai
>> dai ina wani dan tunani ne. Wai don Allah da gaske ka ke
>> kana so na?
>> (Dariya) ina sonki mana Hajjo. Amma me ya sa kika
>> min wannan tambayar?
>> Ai gani na yi kai dan birni
>> ne, me za ka yi da 'yar kauye iri na?Dariya na sake yi sannan na ce
>> mata kar ki damu Hajjo
>> ko ma ya ki ke ina sonki a haka kuma aurenki zan yi.
>> A karshe Hajjo ta kwatanta mini
>> rugar su, ranar Asabar ranar ce mu ka yi da Hajjo zan je rugar su.
>> Da misalin hudu da rabi na
>> yammacin ranar Asabar na shiga rugar su Hajjo, ban sha wata wahala ba
>> wajen neman gidansu ba, domin rugar ta su ba ta da girma sosai. Hajjo
>> tana gani na ta yi ta murna kamar ta rungume ni don tsananin jin dadi,
>> kusan duka mutanen gidan su Hajjo sai da suka zo muka gaisa tare da
>> nuna farin cikinsu da gani na.
>> Fura da nono mai kyau Hajjo ta kawo min, na kuma ji dadin furar
>> gaskiya kauye akwai dadi musamman rugagen fulani ba ruwansu ga yanayi
>> mai dadi ga kuma nono mai kyau ka sha iya shanka ba ka da damuwa.
>> Abu ka ga garinmu kauye ko?
>> Hajjo kenan, ai garin nan naku ina ganin bayan mun yi aure a nan za mu
>> zauna saboda ya min kyau.
>> Cikin jin dadi Hajjo ta rufe fuska da hannayenta tana murmushi alamun
>> jin kunya, kana ta ce haba dai ashe za ka iya zaman kauye?
>> Bayan na hadiye wani gayan fura tare lashe baki kai da ka gan ni kasan
>> ina jin dadin furar da nake sha, sai na bata amsa na ce ban da abin ki
>> Hajjo ai ko shugaban kasa zai so zama a nan ko don shan fura da nonon
>> da ke rugar nan.
>> Wannan karon dariya Hajjo ta yi har da kyakyatawa kana ta ce" gaskiya
>> Abu furar nan ta kama ka da kyau har da santi haka.
>> A ranar mun yi hira sosai kuma hira mai dadi da ita, sannan a karshe
>> mu ka yi bankwana tare da alkawarin kwanaki kadan masu zuwa zan sake
>> dawowa.
>>
>> KARO NA BIYU A RUGAR SU HAJJO
>> Daga ina ka ke?
>> Wa kake nema?
>> Yanzu ba mu da Hajjo a wannan gidan, Hajjonmu yau kimanin shekarunta
>> bakwai da rasuwa. Abin da aka shaida min kenan
>> bayan na koma rugar su Hajjo a karo na biyu.
>> Ikon Allah sai kallo, abin da ya fi bani mamaki shi ne duk mutanen
>> gidan su Hajjo babu wanda ya nuna ya ta6a ganina balle
>> mai kamata, na yi musu bayanin kamanin Hajjo sun tabbatar min ita ce
>> hasalima sun kawo min
>> hotunanta inda ni ma na tabbatar musu cewa ita din ce.
>> Cikin tsananin mamaki da kaduwa haka na baro rugar su Hajjo duk jiki
>> na ya yi sanyi.
>> Tun daga wannan ranar idanuna ba su sake tozali
>> da Hajjo ba balle mai kamarta. Kuma har yanzu zuciyata na cike da
>> matsananciyar kaunarta...
>>
>

No comments:

Post a Comment