0
Daga
Rabi'u Muhammad (Abu Hidaya)

Hajiya Hafsat M.A Abdulwahid fitaccen marubuciya ce wadda sunanta ya
shahara a duniyar rubutu musamman na Hausa, ba za ka shiga tarihin
marubuta ba, ba tare da ka yi gamo da ayyukanta ba, ta fara rubutu tun
kafin marubuta su yawaita, kusan ma ana iya cewa ita ce ta fara bude
hanyar rubutu ga marubuta mata.An haifi Hajiya Hafsat Abdulwahid a
jihar Kano a ranar 5th May, (1952)Ta yi karatun firamare ɗinta a
'Shahuci Primary
School' da ke a Kano. Daga nan ta wuce sakandiren ƴan mata ta
Provincial Girls School wanda aka
sauya ma suna zuwa Shekara Girls Secondary
School.
Ta yi aure a shekarar alif ɗari tara da sittin da shida
(1966),ta auri Muhammad Ahmad Abdulwahid,
tana zaune a jihar Zamfara. Ta na da ƴaƴa, daga cikin ƴaƴanta akwai Kadariya
Ahmad fitacciyar ƴar jarida.
Marubuciya ce da ke rubutunta cikin harshen
Hausa.
Hajiya Hafsat ta fara rubutu ne tun tana
makarantar firamare, inda ta samu damar ƙarbar
l ambobin yabo daga British Council. A shekarar (1970) Hajiya. Hafsat
ta shiga gasar Rubutu
da kamfanin maɗaba'ar wallafa littatafai ta Northern
Nigerian Publishing Company (NNPC) ta gudunar,
inda ta shigar da labarinta mai suna 'SO ALJANNAR
DUNIYA'. Wanda ta rubuta shi tun tana aji biyar na
firamare. Labarin SO ALJANNAR DUNIYA ya samu tagomashin zuwa mataki a
na biyu a gasar.

Hajiya Hafsat Abdulwahid ita ce mace ta farko da
ta fara rubutu a harshen Hausa cikin mata
marubuta da ake da su a yankin Arewa.

Ta rubuta littatafai da dama fiye da talatin , inda ta
samu damar fitar da guda biyar daga ciki. Kadan daga cikinsu sun haɗa
da So Aljannar
Duniya, Ƴardubu Mai Tambotsai, Nasiha Ga
Ma'aurata, Namijin Maza Tauraron Annabawa, sai
littafinta na waƙe a cikin harshen Turanci mai taken
Ancient Dance.

Hajiya Hafsat mace ce jaruma kuma ƴar gwagwarmaya mai rajin kare
hakkin mata (woman
right activist).
Tana daga cikin matan da su ka taɓa fitowa takara r
muƙamin gwamna a yankin arewacin Nijeriya.
Haƙiƙa tana cikin Matan Arewa da su ka kafa tarihi a
cikin mata. Tauraruwa ce, a bar koyi ga matan Arewa.
Babban littafinta na Hausa a yanzu shi ne SABA DAN SABABI wanda ake
ganin yana iya maye gurbin littafin magana jari ce na marigayi
Abubakar Imam.
Hajiya Hafsat Abdulwahid mace ce mai sha'awar tafiye-tafiye don nazari
da rubutu game da rayuwar al'umma, tana da saukin kai tare da son
jama'a.

Post a Comment

Dear readers, after reading the Content please ask for advice and to provide constructive feedback Please Write Relevant Comment with Polite Language.Your comments inspired me to continue blogging. Your opinion much more valuable to me. Thank you.

TAKAITACCEN TARIHIN HAJIYA. HAFSAT M.A ABDULWAHID

Daga
Rabi'u Muhammad (Abu Hidaya)

Hajiya Hafsat M.A Abdulwahid fitaccen marubuciya ce wadda sunanta ya
shahara a duniyar rubutu musamman na Hausa, ba za ka shiga tarihin
marubuta ba, ba tare da ka yi gamo da ayyukanta ba, ta fara rubutu tun
kafin marubuta su yawaita, kusan ma ana iya cewa ita ce ta fara bude
hanyar rubutu ga marubuta mata.An haifi Hajiya Hafsat Abdulwahid a
jihar Kano a ranar 5th May, (1952)Ta yi karatun firamare ɗinta a
'Shahuci Primary
School' da ke a Kano. Daga nan ta wuce sakandiren ƴan mata ta
Provincial Girls School wanda aka
sauya ma suna zuwa Shekara Girls Secondary
School.
Ta yi aure a shekarar alif ɗari tara da sittin da shida
(1966),ta auri Muhammad Ahmad Abdulwahid,
tana zaune a jihar Zamfara. Ta na da ƴaƴa, daga cikin ƴaƴanta akwai Kadariya
Ahmad fitacciyar ƴar jarida.
Marubuciya ce da ke rubutunta cikin harshen
Hausa.
Hajiya Hafsat ta fara rubutu ne tun tana
makarantar firamare, inda ta samu damar ƙarbar
l ambobin yabo daga British Council. A shekarar (1970) Hajiya. Hafsat
ta shiga gasar Rubutu
da kamfanin maɗaba'ar wallafa littatafai ta Northern
Nigerian Publishing Company (NNPC) ta gudunar,
inda ta shigar da labarinta mai suna 'SO ALJANNAR
DUNIYA'. Wanda ta rubuta shi tun tana aji biyar na
firamare. Labarin SO ALJANNAR DUNIYA ya samu tagomashin zuwa mataki a
na biyu a gasar.

Hajiya Hafsat Abdulwahid ita ce mace ta farko da
ta fara rubutu a harshen Hausa cikin mata
marubuta da ake da su a yankin Arewa.

Ta rubuta littatafai da dama fiye da talatin , inda ta
samu damar fitar da guda biyar daga ciki. Kadan daga cikinsu sun haɗa
da So Aljannar
Duniya, Ƴardubu Mai Tambotsai, Nasiha Ga
Ma'aurata, Namijin Maza Tauraron Annabawa, sai
littafinta na waƙe a cikin harshen Turanci mai taken
Ancient Dance.

Hajiya Hafsat mace ce jaruma kuma ƴar gwagwarmaya mai rajin kare
hakkin mata (woman
right activist).
Tana daga cikin matan da su ka taɓa fitowa takara r
muƙamin gwamna a yankin arewacin Nijeriya.
Haƙiƙa tana cikin Matan Arewa da su ka kafa tarihi a
cikin mata. Tauraruwa ce, a bar koyi ga matan Arewa.
Babban littafinta na Hausa a yanzu shi ne SABA DAN SABABI wanda ake
ganin yana iya maye gurbin littafin magana jari ce na marigayi
Abubakar Imam.
Hajiya Hafsat Abdulwahid mace ce mai sha'awar tafiye-tafiye don nazari
da rubutu game da rayuwar al'umma, tana da saukin kai tare da son
jama'a.

No comments:

Post a Comment