0
Daga
Rabi'u Muhammad Abu Hidaya Masarautar Bande wadda ta kasance masarauta
mai dadadden tarihi cikin masarautun kasar Nijar ta
samu sabon sarki bayan rasuwar tsohon sarkin
garin,
sarkin dai mai suna Abubakar Yahaya Lushe ya
kasance shi ne sarki na bakwai a jerin sarakunan da suka mulki kasar
ya kuma matashi ne jami'i a
aikin Soja mai mukamin Kanal wanda ya bar aikin
sojan don maye gurbin mahaifinsa domin shi
mutum ne mai son ci gaban al'ummar kasarsa, ya
samu zama sarkin ne bayan da masu ruwa da tsaki
suka zabe shi a matsayin wanda zai gaji mahaifinsa da ya rasu kwanaki
kadan baya, wannan zabi da
aka yi masa dai ya faranta ran mafi yawa daga cikin
jama'ar garin Bande da na masarautar, inda
dukkansu su ka yi maraba da shi, domin sun
tabbatar da cewa sabon sarkin na su yana da halin
girma da dattako irin na mahaifinsa. A lokacin da sarkin yake jawabi
game da kudirin
da zai gabatar a masarautar da ya gada daga
mahaifinsa ya ce "zai fi mayar da hankali ne game
da abin ya shafi Ilimi a kasar da kuma harkar
kasuwanci tare da wasannin gargajiya wadanda ya
ce an yi musu nisa a sauran gurare. Ya kuma ce zai karfafa alaka da
sauran masarautun
da suke sauran kasashen da suke makotaka da
masarautarsa"
har ila yau da yake ci gaba da jawabi ya ce
masarautarsa tana maraba da duk wani da yake da
son ci gaban al'umma kuma zai yi hadin gwiwa da duk wanda da yake da
harkar kasuwanci, haka
kuma yace game da abin da ya shafi noma kiwo
gami da kiwon lafiya nan ma ba za a bar kasar
bande a baya ba, lallai a karkashin masarautarsa za
a samu ci gaba sosai, babban burin wannan sabon
sarki dai ya ce bai wuce ya samu hadin kan jama'ar kasarsa ba sannan
yana fatan a ce ya fi mahaifinsa
kokari.
A nasa jawabin wani malamin Makaranta kuma na
kusa da masarautar ya ce" lallai suna alfahari da
wannan sarki wanda suke ganinsa tamkar
mahaifinsa domin mahaifinsa ya zauna da kowa lafiya da ya kuma kaunaci
talakawansa tamkar a
'yayan cikinsa shi mutum ne mai son talakawan
kasarsa, kuma ya tabbatar da cewa wannan sarki
zai kawo ma kasar Bande gagarumin ci gaba.
A karshe mafi yawa daga cikin jama'ar kasar suna
ta tururuwa domin yin mubaya'a ga sabon sarkin na su Abubakar Yahaya
Lushe har ila yau kuma
mutane da dama suna ta fatan ganin ranar da za a
yi bikin ba shi sandar mulki domin su nuna masa
soyayya da kauna.

On 11/23/17, Rabiu Muhammad Abu Hidaya <abuhidya3@gmail.com> wrote:
> ALMARA KO GASKE?
>
> Daga
> Rabi'u Muhammad Abu Hidaya
>
>
> Al'ada ta ce duk karshen mako na kan kai ziyara garinmu, domin gaishe
> da iyaye, 'yan'uwa da
> abokan arziki.
> A garin akwai wata kasuwa da
> ta ke ci duk ranar juma'a, kasancewata mutum ne mai son shan fura, don
> haka duk ranar kasuwar garin na kan shiga kasuwar domin sayan fura,
> akwai wata budurwar bafulatana, mai suna Hajjo, Hajjo tana da kirki
> kwarai don haka ne ma, babu furar wadda da nake sha kaf
> kasuwar sai ta ta, mun saba da Hajjo matukar sabo, domin idan na je
> gurinta sam ba ta iya sakewa
> saboda tsananin jin kunya.
> So! shu'umi ya kan shiga zuciya ba tare da ya yi sallama ba. A kwana a
> tashi sai na fara jin son Hajjo mai fura ya shiga zuciyata, domin har
> ta kai idan na dawo kano bana iya sakewa in yi ayyukana yadda ya
> kamata, haka zan ta fatan karshen mako ya yi na je garin, ban samu
> nutsuwa ba sai da na bayyanawa Hajjo abin da yake raina, na ci sa'a
> domin a karon farko Hajjo ta amince da ni a matsayin saurayinta.
> Watarana ina kasuwa a cikin rumfar da Hajjo take sayar da fura muna
> hira ina shan furar da ta dama min, sai nake
> tambayarta Hajjo ya kamata a ce nasan gidanku
> domin in zo mu yi maganar aure, shiru ta yi na 'yan
> mintoci gami da aje ludayin furar da ke hannunta tare da sunkuyar da
> kai kasa na dan wani lokaci, kana daga bisani sai ta ja wani dogon
> numfashi! Gami da kallon wata yarinya da ke zaune a gefenta bisa wani
> dutse tana sayar da mandako. Ko ba ki son in zo gidan ku ne? A'a kawai
> dai ina wani dan tunani ne. Wai don Allah da gaske ka ke
> kana so na?
> (Dariya) ina sonki mana Hajjo. Amma me ya sa kika
> min wannan tambayar?
> Ai gani na yi kai dan birni
> ne, me za ka yi da 'yar kauye iri na?Dariya na sake yi sannan na ce
> mata kar ki damu Hajjo
> ko ma ya ki ke ina sonki a haka kuma aurenki zan yi.
> A karshe Hajjo ta kwatanta mini
> rugar su, ranar Asabar ranar ce mu ka yi da Hajjo zan je rugar su.
> Da misalin hudu da rabi na
> yammacin ranar Asabar na shiga rugar su Hajjo, ban sha wata wahala ba
> wajen neman gidansu ba, domin rugar ta su ba ta da girma sosai. Hajjo
> tana gani na ta yi ta murna kamar ta rungume ni don tsananin jin dadi,
> kusan duka mutanen gidan su Hajjo sai da suka zo muka gaisa tare da
> nuna farin cikinsu da gani na.
> Fura da nono mai kyau Hajjo ta kawo min, na kuma ji dadin furar
> gaskiya kauye akwai dadi musamman rugagen fulani ba ruwansu ga yanayi
> mai dadi ga kuma nono mai kyau ka sha iya shanka ba ka da damuwa.
> Abu ka ga garinmu kauye ko?
> Hajjo kenan, ai garin nan naku ina ganin bayan mun yi aure a nan za mu
> zauna saboda ya min kyau.
> Cikin jin dadi Hajjo ta rufe fuska da hannayenta tana murmushi alamun
> jin kunya, kana ta ce haba dai ashe za ka iya zaman kauye?
> Bayan na hadiye wani gayan fura tare lashe baki kai da ka gan ni kasan
> ina jin dadin furar da nake sha, sai na bata amsa na ce ban da abin ki
> Hajjo ai ko shugaban kasa zai so zama a nan ko don shan fura da nonon
> da ke rugar nan.
> Wannan karon dariya Hajjo ta yi har da kyakyatawa kana ta ce" gaskiya
> Abu furar nan ta kama ka da kyau har da santi haka.
> A ranar mun yi hira sosai kuma hira mai dadi da ita, sannan a karshe
> mu ka yi bankwana tare da alkawarin kwanaki kadan masu zuwa zan sake
> dawowa.
>
> KARO NA BIYU A RUGAR SU HAJJO
> Daga ina ka ke?
> Wa kake nema?
> Yanzu ba mu da Hajjo a wannan gidan, Hajjonmu yau kimanin shekarunta
> bakwai da rasuwa. Abin da aka shaida min kenan
> bayan na koma rugar su Hajjo a karo na biyu.
> Ikon Allah sai kallo, abin da ya fi bani mamaki shi ne duk mutanen
> gidan su Hajjo babu wanda ya nuna ya ta6a ganina balle
> mai kamata, na yi musu bayanin kamanin Hajjo sun tabbatar min ita ce
> hasalima sun kawo min
> hotunanta inda ni ma na tabbatar musu cewa ita din ce.
> Cikin tsananin mamaki da kaduwa haka na baro rugar su Hajjo duk jiki
> na ya yi sanyi.
> Tun daga wannan ranar idanuna ba su sake tozali
> da Hajjo ba balle mai kamarta. Kuma har yanzu zuciyata na cike da
> matsananciyar kaunarta...
>

Post a Comment

Dear readers, after reading the Content please ask for advice and to provide constructive feedback Please Write Relevant Comment with Polite Language.Your comments inspired me to continue blogging. Your opinion much more valuable to me. Thank you.

AN YI NADIN SABON SARKI A MASARAUTAR BANDE

Daga
Rabi'u Muhammad Abu Hidaya Masarautar Bande wadda ta kasance masarauta
mai dadadden tarihi cikin masarautun kasar Nijar ta
samu sabon sarki bayan rasuwar tsohon sarkin
garin,
sarkin dai mai suna Abubakar Yahaya Lushe ya
kasance shi ne sarki na bakwai a jerin sarakunan da suka mulki kasar
ya kuma matashi ne jami'i a
aikin Soja mai mukamin Kanal wanda ya bar aikin
sojan don maye gurbin mahaifinsa domin shi
mutum ne mai son ci gaban al'ummar kasarsa, ya
samu zama sarkin ne bayan da masu ruwa da tsaki
suka zabe shi a matsayin wanda zai gaji mahaifinsa da ya rasu kwanaki
kadan baya, wannan zabi da
aka yi masa dai ya faranta ran mafi yawa daga cikin
jama'ar garin Bande da na masarautar, inda
dukkansu su ka yi maraba da shi, domin sun
tabbatar da cewa sabon sarkin na su yana da halin
girma da dattako irin na mahaifinsa. A lokacin da sarkin yake jawabi
game da kudirin
da zai gabatar a masarautar da ya gada daga
mahaifinsa ya ce "zai fi mayar da hankali ne game
da abin ya shafi Ilimi a kasar da kuma harkar
kasuwanci tare da wasannin gargajiya wadanda ya
ce an yi musu nisa a sauran gurare. Ya kuma ce zai karfafa alaka da
sauran masarautun
da suke sauran kasashen da suke makotaka da
masarautarsa"
har ila yau da yake ci gaba da jawabi ya ce
masarautarsa tana maraba da duk wani da yake da
son ci gaban al'umma kuma zai yi hadin gwiwa da duk wanda da yake da
harkar kasuwanci, haka
kuma yace game da abin da ya shafi noma kiwo
gami da kiwon lafiya nan ma ba za a bar kasar
bande a baya ba, lallai a karkashin masarautarsa za
a samu ci gaba sosai, babban burin wannan sabon
sarki dai ya ce bai wuce ya samu hadin kan jama'ar kasarsa ba sannan
yana fatan a ce ya fi mahaifinsa
kokari.
A nasa jawabin wani malamin Makaranta kuma na
kusa da masarautar ya ce" lallai suna alfahari da
wannan sarki wanda suke ganinsa tamkar
mahaifinsa domin mahaifinsa ya zauna da kowa lafiya da ya kuma kaunaci
talakawansa tamkar a
'yayan cikinsa shi mutum ne mai son talakawan
kasarsa, kuma ya tabbatar da cewa wannan sarki
zai kawo ma kasar Bande gagarumin ci gaba.
A karshe mafi yawa daga cikin jama'ar kasar suna
ta tururuwa domin yin mubaya'a ga sabon sarkin na su Abubakar Yahaya
Lushe har ila yau kuma
mutane da dama suna ta fatan ganin ranar da za a
yi bikin ba shi sandar mulki domin su nuna masa
soyayya da kauna.

On 11/23/17, Rabiu Muhammad Abu Hidaya <abuhidya3@gmail.com> wrote:
> ALMARA KO GASKE?
>
> Daga
> Rabi'u Muhammad Abu Hidaya
>
>
> Al'ada ta ce duk karshen mako na kan kai ziyara garinmu, domin gaishe
> da iyaye, 'yan'uwa da
> abokan arziki.
> A garin akwai wata kasuwa da
> ta ke ci duk ranar juma'a, kasancewata mutum ne mai son shan fura, don
> haka duk ranar kasuwar garin na kan shiga kasuwar domin sayan fura,
> akwai wata budurwar bafulatana, mai suna Hajjo, Hajjo tana da kirki
> kwarai don haka ne ma, babu furar wadda da nake sha kaf
> kasuwar sai ta ta, mun saba da Hajjo matukar sabo, domin idan na je
> gurinta sam ba ta iya sakewa
> saboda tsananin jin kunya.
> So! shu'umi ya kan shiga zuciya ba tare da ya yi sallama ba. A kwana a
> tashi sai na fara jin son Hajjo mai fura ya shiga zuciyata, domin har
> ta kai idan na dawo kano bana iya sakewa in yi ayyukana yadda ya
> kamata, haka zan ta fatan karshen mako ya yi na je garin, ban samu
> nutsuwa ba sai da na bayyanawa Hajjo abin da yake raina, na ci sa'a
> domin a karon farko Hajjo ta amince da ni a matsayin saurayinta.
> Watarana ina kasuwa a cikin rumfar da Hajjo take sayar da fura muna
> hira ina shan furar da ta dama min, sai nake
> tambayarta Hajjo ya kamata a ce nasan gidanku
> domin in zo mu yi maganar aure, shiru ta yi na 'yan
> mintoci gami da aje ludayin furar da ke hannunta tare da sunkuyar da
> kai kasa na dan wani lokaci, kana daga bisani sai ta ja wani dogon
> numfashi! Gami da kallon wata yarinya da ke zaune a gefenta bisa wani
> dutse tana sayar da mandako. Ko ba ki son in zo gidan ku ne? A'a kawai
> dai ina wani dan tunani ne. Wai don Allah da gaske ka ke
> kana so na?
> (Dariya) ina sonki mana Hajjo. Amma me ya sa kika
> min wannan tambayar?
> Ai gani na yi kai dan birni
> ne, me za ka yi da 'yar kauye iri na?Dariya na sake yi sannan na ce
> mata kar ki damu Hajjo
> ko ma ya ki ke ina sonki a haka kuma aurenki zan yi.
> A karshe Hajjo ta kwatanta mini
> rugar su, ranar Asabar ranar ce mu ka yi da Hajjo zan je rugar su.
> Da misalin hudu da rabi na
> yammacin ranar Asabar na shiga rugar su Hajjo, ban sha wata wahala ba
> wajen neman gidansu ba, domin rugar ta su ba ta da girma sosai. Hajjo
> tana gani na ta yi ta murna kamar ta rungume ni don tsananin jin dadi,
> kusan duka mutanen gidan su Hajjo sai da suka zo muka gaisa tare da
> nuna farin cikinsu da gani na.
> Fura da nono mai kyau Hajjo ta kawo min, na kuma ji dadin furar
> gaskiya kauye akwai dadi musamman rugagen fulani ba ruwansu ga yanayi
> mai dadi ga kuma nono mai kyau ka sha iya shanka ba ka da damuwa.
> Abu ka ga garinmu kauye ko?
> Hajjo kenan, ai garin nan naku ina ganin bayan mun yi aure a nan za mu
> zauna saboda ya min kyau.
> Cikin jin dadi Hajjo ta rufe fuska da hannayenta tana murmushi alamun
> jin kunya, kana ta ce haba dai ashe za ka iya zaman kauye?
> Bayan na hadiye wani gayan fura tare lashe baki kai da ka gan ni kasan
> ina jin dadin furar da nake sha, sai na bata amsa na ce ban da abin ki
> Hajjo ai ko shugaban kasa zai so zama a nan ko don shan fura da nonon
> da ke rugar nan.
> Wannan karon dariya Hajjo ta yi har da kyakyatawa kana ta ce" gaskiya
> Abu furar nan ta kama ka da kyau har da santi haka.
> A ranar mun yi hira sosai kuma hira mai dadi da ita, sannan a karshe
> mu ka yi bankwana tare da alkawarin kwanaki kadan masu zuwa zan sake
> dawowa.
>
> KARO NA BIYU A RUGAR SU HAJJO
> Daga ina ka ke?
> Wa kake nema?
> Yanzu ba mu da Hajjo a wannan gidan, Hajjonmu yau kimanin shekarunta
> bakwai da rasuwa. Abin da aka shaida min kenan
> bayan na koma rugar su Hajjo a karo na biyu.
> Ikon Allah sai kallo, abin da ya fi bani mamaki shi ne duk mutanen
> gidan su Hajjo babu wanda ya nuna ya ta6a ganina balle
> mai kamata, na yi musu bayanin kamanin Hajjo sun tabbatar min ita ce
> hasalima sun kawo min
> hotunanta inda ni ma na tabbatar musu cewa ita din ce.
> Cikin tsananin mamaki da kaduwa haka na baro rugar su Hajjo duk jiki
> na ya yi sanyi.
> Tun daga wannan ranar idanuna ba su sake tozali
> da Hajjo ba balle mai kamarta. Kuma har yanzu zuciyata na cike da
> matsananciyar kaunarta...
>

No comments:

Post a Comment