0

     DAGA
               AHMAD S. BELLO 
        (08033551751)
                 SASHEN HAUSA
KWALEJIN ILIMI TA TARAYYA DA KE ZARIYA





TAKARDAR DA AKA GABATAR A WAJEN TARON MASOYA AMINU ALAN WAQA WANDA AKA YI A XAKIN TARO NA MAKARANTAR ADO   GWARAM DA KE KAN TITIN GIDAN NAMUN DAJI, KANO. 
                                         RANAR LAHADI, 08/10/2017.

1.0 GABATARWA
Wannan takarda za ta yi magana ne a bisa tasirin da waqa kan yi a cikin al'ummar Hausawa: Tsokaci daga wasu waqoqin Aminu Ala. Ko da yake ainihin batun da aka ba ni, an taqaita taken batun ne a kan tasirin waqa a cikin al'umma kawai. To, a nan sai na yi wa kaina tambaya, to, wace al'ummar ake so a nuna yadda waqa ta yi tasiri a kanta? Sannin kowa ne al'ummomin duniya suna da yawa, haka nan suke da yawa a Afirka, balle uwa uba Nijeriya. Nijeriyar ma ta arewaci al'ummominta suna da yawa, don haka wacce al'umma ake so mu xaura aikin nan a kai yanzu? Amsar ita al'ummar Hausawa. Don haka, na yi karambanin  qari a kan wannan batu da cewa, Tasirin Waqa a Cikin Al'ummar Hausawa: Tsokaci Daga Wasu Waqoqin Aminu Ala. Tun da taron nan an tsara shi domin karrama Aminu Ala da masoyansa, to, an taqaita tsokaci a bisa waqoqin nasa kawai a matsayin kadaddarta, domin ita ma takarda mai qaunar Aminu Ala ce, kuma tana mai nuna so da qauna tare da karramawa a gare shi a yau, tare da mu masoyan nasa baki xaya. Bigiren wannan takarda ya taqaita ne a bisa waqoqin da aka rubuta a cikin littafin Muhammad Lawal Barista, mai suna Waqoqin Aminu Ladan Abubakar Alan Waqa Littafi na Xaya. Don haka, me ake nufi da tasiri? Qamusun Hausa na Jami'ar Bayero (2007) ya ce tasiri yana nufin muhimmanci ko dangantaka ko qarfi. A nan za mu duba wane irin dangantaka waqoqoqin Aminu Ala suke da shi a cikin al'ummar Hausawa? Ina mai fata Allah Subhanahu wata'ala ya saka wa waxanda suka halarci wannan taro da alhairi, tare da waxanda suka yi qoqarin tabbatar da shi.Amin.
2.0 MA'ANAR WAQA
Kamar yadda Xangambo (2007) ya ce ya kamata mu tuna cewa akwai waqoqi iri biyu: rubutacciyar waqa da waqar baka wato waqar makaxa. Shin me ce ce waqa? Sau da yawa mutane sukan yi wannan tambaya muhawara ta harqe. Ko da yake ba nufin wannan takarda ba ne a kawo wannan mahawara, a nan, waqa wani saqo ne da aka gina shi kan tsararriyar qa'ida ta baiti, xango, rerawa, kari (bahari) amsa-amo (qafiya) da sauran qa'idojn da suka shafi daidaita kalmomi, zavensu da amfani da su, cikin sigogin da ba lalle ne haka suke a maganar baka ba. Gusau (2003) ya nuna cewar waqa tana zuwa ne a sigar gunduwowin zantuka waxanda ake kira baitoci ko xiyoyi. Kuma ake rerawa da wani irin sautin murya ta musamman.
Shi ma Yahaya (1984:2-3) ya ce: "waqa maganar hikima ce da ake rerawa ba faxa kurum ba wadda ke da wani saqo da ke qunshe cikin wasu kalmomi zavavvu, tsararru kuma zaunannu.
Idan muka kalli ma'anar da waxannan masana suka bayar a bisa waqa za a ga sun yi tarayya a bisa tsarawa da hikima da rerawa da saqo da zavavvun kalmomi tare da zamansu ko direwa. Wannan yana nuna mana cewa waqa daban take da zancen baka na yau da gobe, kuma tana xauke da wani saqo da take son isar wa ga al'ummar da aka tsara wa ga al'ummar tata kuma dominta.
3.0 HAUSA, HAUSAWA DA QASARTA
Qasar Hausa tana da girma qwarai da gaske, tana da yanayi (hali da ake ciki) kamar na damina da kaka da bazara da sanyi. A nan yana da muhimmanci a san ko ina ne qasar Hausa, ina ne iyakokinta, su wane ne makwabtanta. Wannan shi zai taimaka mana wajen qara fahimtar yadda yanayin qasar Hausa take da kuma yadda yanayinta yake kasancewa a cikin shekara. (Adamu, 1997), ya ba da iyakokin qasar Hausa ta amfani da taswirar qwallon duniya, aka yi amfani da layuka da aka zana domin qara saukaka gano wurare a bisa qwallon duniya kamar haka:
"….za a sami qasar Hausa a tsakanin layi na goma sha biyar (150N) zuwa na goma sha takwas (180N) na arewa da ikwaita; kuma tana tsakanin layi na takwas (80E) da na goma sha biyu (120E) a gabas da layin Greenwic"
Masu nazari a fannin lammuran qasa (Geography) sun ce, wannan hanya ita ce mafi karvuwa wajen fayyace kowane muhalli da ainihin mazauninsa a bisa doron qasa. An kasa kwallon duniya zuwa gida-gida ta amfani da wasu layuka guda biyu, wato layin longtitude wanda ya faro daga arewa zuwa kudu a kan qwallon duniya; sai kuma layin latitude wanda ya faro tun daga gabas zuwa yamma a kan kwallon duniya.
Adamu, (2011) ya bayyana inda ake kira qasar Hausa a wata maqala da ya gabatar sai aka fassara kamar yadda yake cewa a Turance:
Qasar Hausa ta faro ne tun daga Abzin a tsaunuka Air a shiyyar arewa (a qasar Nijar ta yau) zuwa wasu kilomitoci kudu da kufena da Turunku a Zazzau (a qasar Nijeriya ta yau) daga sashen kudu ke nan; ta kuma soma daga tsakanin kwarin Neja a shiyar yamma har zuwa iyakokin Nijeriya da Nijar a gabas
Wannan bayani na Adamu (2011), ya ba mu haske a kan farfajiyar da qasar Hausa take a doron qasa, domin ya kawo mana mahallin da ita kanta qasar Hausar take, ta yadda idan mutum ya xauki littafin taswirar kwallon duniya (atlas) zai iya hasashen ko ina ne qasar Hausa. Adamu (1997) ya qara da cewa:
Kasar Hausa a yau tana cikin Afirka ta Yamma a arewacin Nijeriya. Kuma a kwance ta tavo har cikin qasar Nijar wajen su Maraxi da wasu 'yan garuruwa, haka kuma daga gabas ta yi iyaka da wani yanki na Jamhuriyar Binin a gabar da kogin kwara, daga wajen kudu kuma ta yi iyaka da qabilun Gwari da kuma qabilun kudancin Zariya da na kudancin Bauci.
To idan muka kalli waxannan bayanai da suka gabata kallo irin na fahimta, muna iya kammalawa da cewa, yanzu kam mun fitar da muhalli ko farfajiya da ake kira qasar Hausa a fannin tarihi da fannin kimiyyar lamuran qasa (geography). Idan kuwa muka haxa waxannan bayani, za mu ga haqiqannin inda ita wannan qasa ta Hausa take a cikin farfajiyar Afirka.
A duk bayanan da muka gabatar, kowane xaya daga cikin su ya ba da muhallin da farfajiyar qasar Hausa take, ma'ana babu inda wani daga cikinsu ya yi takun saka da wani a wurin fayyace ta. Duk sun ba da bayani waxanda suka yi canjaras da juna. 
Masana ilimin labarin qasa, sun bayyana qasar Hausa da cewa wuri ne da ke da shimfixaxxiyar qasa a mafi yawanta, ana kuma samun wasu wurare masu tudu da kwari, akwai manyan duwatsu da tsaunuka. Daga arewacin qasar inda ake kira Sahara (Sahel), nan ne ake samun itatuwa marasa inuwa sosai. Sai kuma daga kudanci, wurin da ya fi yawan itatuwa masu duhu, wato sashen sabana (savannah).
Gusau, (2003) yana mai faxaxa wannan batu da cewa a arewacin qasar akwai wurare masu dausayi a sanadiyyar kusanci da tafkuna ko rafuka ko kuma xaya daga cikin gulaben da suka samu a sanadiyyar rarrabuwar igiyoyin manyan koguna da suka ratsa qasar wato; kogin Haxeja wanda ya faro daga Kano, ya yi gabas har zuwa tafkin Chadi. Akwai kuma kogin Rima wanda ya faro daga Zamfara ya gangara arewa zuwa Nijar sannan ya karkato kudu ya yi yamma da Sakkwato ya haxe da kogin Kwara. Shi kuwa kogin Kwara ya yi iyaka ne da qasar Hausa daga sashen yamma.
Adamu, (1997) ya yi bayani a kan yanayin qasar Hausa na shekara-shekara a inda yake cewa:
Qasar Hausa, tana da yanayin shekara-shekara iri biyu ne, lokacin damina da na rani. A lokacin damina ne wato tsakanin watan Mayu-Satumba ake samun ruwan sama, yawan ruwan da ake samu kima ne amma duk da haka yakan biya buqata wajen aikin gona. Lokacin rani yana farawa daga Oktoba zuwa Afrilu, rani ya kasu biyu; lokacin xari ko hunturu da lokacin zafi wato bazara. Bazara lokaci ne da rana take yin tsananin zafi iska takan tsaya cik. Sai dai kuma wani lokaci guguwa takan tashi daga wani wuri zuwa wancan.
Qasar Hausa ta kasance mai yanayi iri biyu wato damina da rani saboda irin halin da qasar take da shi, wato a wani vagare qasar tana da manyan itatuwa masu duhu kamar yankin qasar Zariya, sannan wani vangaren qasar tana da gajerun itatuwa kamar irin yankin qasar Sakkwato. Kasancewar hakan shi ya sa qasar Hausa take da yanayin shekara iri biyu. Bugu da qari, qasar Hausa wuri ne da ke da ma'adinai daban-daban a qarqashin qasa, kamar su kanwa da qarfe (jan karfe da bakin karfe da azurfa da sauransu), akwai kuma yumbu (qasa) wadda ake tubali na gini da kuma ginin tukwane da dai sauransu da ita.

3.1 Asalin Hausawa
Asalin Hausawa kamar yadda Smith (1984) ya bayyana cewa a tsakanin shekarar 1050 zuwa 1100 ta miladiya, waxansu 'yan qabilar Buzaye (Berbers) sun ratso sahara suka yi auratayya da wasu al'ummu daban. Wai a sanadin wannan cuxanya ne aka sami Hausawa da harshen Hausa.
Kazalika Smith (1984), ya kawo nasa ra'ayin mai kusanci da na Smith, wato ya amince da cewa akwai sauyin wurin zama da ya auku daga gabas zuwa kasar Tukururu, wanda ya yi sanadin samuwar Hausawa. Ya qara da cewa wannan qaura ta faru a shekarar 1350 miladiya.
Bunza, (1990) ya bayyana cewa, a wani ra'in, Hausawa dai suna zaune shekaru masu yawa da suka wuce, wai amma yarensu ba shi da suna, wai sai da Larabawa masu cinikin bayi suka zo qasar suka fara da yare mai kama da Larabci, amma yadda aka sauya wasu kalmomi a furucinsu sun sava da na Larabci.
Idan aka yi la'akari da bayanin wannan masanin, Hausawa dai mutane ne da suke zaune a qasar Hausa tun farkon ta. Ibrahim, da wasu (1982) suna da ra'ayin cewa, "Daxewar harshen Hausa a duniya ya dogara ne ga daxewar Hausawa. Wato ke nan tun a lokacin da 'yan Adam suka karkasu zuwa jinsi-jinsi, to a wannan ne aka sami qabilar Hausawa masu magana da Hausa. Bugu da qari wasu na da ra'ayin cewa Bayajidda (Abu Yazid) ya zo Daura ya tarar da mutane har da magajiyarsu a Daura. Abin nufi a nan dai, Hausawa suna da kafaffiyar daula. To a nan tambaya ita ce, kafin zuwan Bayajida da wane harshe suke amfani? Haka kuma, mutum zai iya tambayar yadda zance ya gudana tsakanin tsohuwar da Bayajida ya sauka a gidanta, wanda ya roqi ruwa a wurinta domin ya ba dokinsa. Ta kuma gaya masa cewa ba ta da ruwa, ta kuma labarta masa labarin Sarki macijiya, sannan ya nemi ta ara masa guga ya samo ruwa. Amsa a nan idan wannan batu haka yake, to Bayajida ya samu Hausa da Hausawa a mazauninsu, wato ba shi ne asalin Hausawa ba. Ashe ba abin mamaki ba ne idan mun ce Bayajida ya koyi Hausa kafin ya iso Daura ko kuma bayan ya zo Daura. 
Shi kuma Smith, (1987), ya nuna rashin amincewarsa da bayanin dangane da asalin Hausawa musamman ma cewa wai shekara dubu da suka wuce babu Hausawa. Shi yana ganin cewa kasa rarrabewa aka yi tsakanin asalin Hausawa da kuma asalin daular Hausawa da aka kafa a dalilin rashin fahimtar juna. Kazalika Malamin bai amince da cewa Hausawa sun samo asali a sakamakon auratayya tsakanin Berber (Buzaye) da kuma Tukururu da suka same su a wurin ba. Don haka ra'ayinsa ya karkata ko ya fi danganta Hausawa da harsuna 'yan gidan Chadi, irin su Margi da Bolawa da Ngizim da Buduma da Kotoko da jukun da Angas da Sayawa da sauransu. Haka nan yana ganin cewa Hausa ta raba hanya da waxannan harsuna shekaru dubbai da suka wuce. Masanin ya qara da cewa mai yiwuwa akwai dangantaka tsakanin harshen Berber da na Chadi, amma tun kafin sahara ta zama Hamada. Ya kara da cewa, babu shakka ba abu ne mai karvuwa ba a ce shekarau 960 da suka wuce babu Hausawa.
Shi kuma Adamu, (1978), a ra'ayinsa, Hausawa dai su ne daxaxxun mutane mazauna qasar Hausa da suke amfani da al'adun Hausawa kuma suna riqo da harshe Hausa da addininsu.
A nasa ra'ayin, Amfani, (2011) cewa ya yi, an tabbatar da cewa a can cikin tarihi akwai wani lokaci da mutane suka yi ta yin qaurace-qaurace daga yankin Tafkin Chadi suna yin yamma. Baban dalili yin waxannan qaurace-qaurace shi ne qeqashewar tafkin Chadi. Gulbin Kebbi da Tafkin Chadi akwai nisa qwarai kuma akwai makekiyar qasa. A lokacin qaurace-qauracen, waxansu mutane sun qarasa har gulbin Kebbi, waxansu kuwa iyakarsu tsaunukan Borno. Waxannan mutanen sun dade qwarai a wannan makekiyar kasa yadda har ma ba a san lokacin da suka zo ba. Ba a san su sosai ba sai a karni na sha biyar. Mutanen kabilu ne daban-daban, Hausawa da Bolawa da Ngizim da Manga da Margi da Buduma da Kotoko su ne manyan kabilun a ciki, Hausawa sun fi yawa kuma sun fi warwatsuwa cikin wannan makekiyar qasa.
Dangane da bayanan masana da aka kawo a sama, wannan bincike ya lura cewa kasar Hausa kasa ce mai fadi da yalwa. A halin da ake ciki, tana da al'ummomi daban-daban, kodayake dai Hausawa su ne mafi akasari a ciki. Kasar tana da yanayin rani bayan daukewat ruwan sama, lokacin kasar ke bushewa. Akwai kuma yanayin damina, lokacin da ake samun ruwan sama, ake kuma gudanar da noma. 
4.0 TASIRIN WAQOQIN AMINU ALA A CIKIN AL'UMMAR HAUSAWA
Waqoqin Aminu Ala sun yi tasiri a kusan duka fuskokin rayuwar al'ummar Hausawa tun daga haihuwa har i zuwa mutuwa. Domin zan iya bugun qirji in ce, waqoqin Aminu Ala sun tavo matakan rayuwar Hausawa a bisa haihuwa, aure da mutuwa. Kaxan daga cikin jigogin ginin waqoqin Aminu Ala sun haxa da Gargaxi da tunatarwa da yabo (Fulfulde Album da Angara Album), zumunci da wa'azi da farfaganda da son manzon Allah da tauhidi da tuba tare da kumawa ga Allah da zamantakewa da kyautayi da girmawa (Gwadabe Album da Fuju'a Album da JakadiyaAlbum), siyasa da kula da marayu da kyautatawa Malaman Addini da zaman lafiya da dogaro da kai da barin tadanci da barin shaye-shaye (Kamfa Album da Mulukiya Album da Zaman Lafiya da Lu'ulu'u Album da Bubukuwa Albuma) da sauran su. Bari na fara tsokaci a kan jigon ilimi wanda shi ne gishirin zaman duniya. Aminu Ala ya zayyano a cikin wata waqarsa mai taken "mu nemi ilimi" na xauko ta ne shekaran jiya ta layinsa na Istagaram, an nuno hoton Aminu Ala a cikin aji yana xaukar darasi, wanda sanadiyyara haka za mu iya cewa mai dokar barci bai yin gyangyaxi, inda yake kira ga al'umma da a je a nemi ilimi ga kaxan daga cikin abinda yake cewa:
"Mu nemi ilimi fitilar haskakawa
Haske na ilimi baya nashewa
Hasken da ko ina shi ke qyallawa
Ko wanda bai gani na fuskantowa"
A nan an fito qarara cewa ilimi fitilar haskakawa ce ga kowacce irin al'umma domin qarfin ilimin al'umma, qarfin arziqinta, mu dubi qasashen da suka ci gaba a duniyar yau a fagen qere-qere da kimiyya mene ne abin dogaronsu? Shi ne ilimi, misali qasashen Turai da Asia. Don haka a nan yana mai kira ga al'ummar Hausawa da a je a nemi ilimi, shi ma, duk da shekarunsa da hidindumu da ke gabansa bai hana shi komawa makaranta ba.
4.1 SIYASA (WAQAR BAQAR MALAFA)
Aminu Ala ya yi amfani da tunaninsa da fasaharsa wajen ba da gudunmuwarsa a fagen siyasar qasar Hausa a cikin al'ummarmu ta yau, a cikin wata waqa mai taken "Baqar Malafa Baqar Jarfa" wannan waqa ba qaramin tasiri ta yi ba a cikin al'ummar Hausawa domin jawo hankalin jama'a, lallai kar a sake zavar Jam'iyyar PDP a zaven shekarar 2015 da aka yi. Waqar tana mai nuni da lallai da ya kamata jama'a kan su ya waye, su yi amfani da quri'arsu domin a kawo sauyin sabuwar gwamnati APC wanda take kan mulki a wancan zamani.
"Baqar malafa Baqar jarfa
                      Mai shanye jinin jikin talaka
Allah kaxa guguwar sauyi
Buhari janaral ya karvi gari"
Mawaqin ya fito qarar inda yake nuna wa, al'umma cewa wannan karo, babu wani abu da ya rage face a zavi shugaba Muhammadu Buhari a matsayin shugaban qasa domin shi ne kawai wanda zai iya kawo waraka ga matsalolin Nijeriya. A qarshe waqar ta yi tasiri, jama'a sun bi, sun kuma zave shi. Domin an nuna Jam'iyar mai malafa, ba ta da wani aiki face shanye jinin talaka, don haka yana mai roqon Allah ya kaxa iskar goguwar sauyin da zai saukar da mulkin mai malafa, Buhari ya xare mulkin qasa, kuma Allah ya amsa.
4.2 TARIHI (WAQAR MASHIGAN KANO)
Waqar mashigan Kano, an rubuta wannan waqar don bayyana tarihin qofofin Kano da dalilin samuwarsu. A nan waqar ta yi tasiri wajen nusar da al'umma yadda akai qofofin Kano da dalilin kafa su misali qofar Nasarawa da qofar Xanagundi da Kabuga da qofar Na'isa da qofar Ruwa da sauransu. Misali ga wani baiti inda ya ce:
Bayarwa: Zan batu kan ababen tarihin Kanawa, wasu an banzantar wasu an bi an adanawa, mai yiwa yin hakan zai tinzirar da Kanawa a gurin kariya da abin da zan ambatuwa.
Amshi: Yau yabo zan yi wa abubuwan kambamawa, mashiga tak Kano abin gwanin armasawa.
Mawaqin ya fito kai tsaye yana mai nuni da cewa qofofin Kano yake son ya waqe su domin amfanin al'umma ga waxanda ba su san tarihinsu ba. Kuma qofofin nan abubuwan kambamawa ne da armasawa ga duk wanda ya san asalin yadda aka kafa su a tarihince. Haqiqa wannan waqa ta yi tasiri matuqa domin jama'a da dama waxanda ba su san tarihi ba, ko kuma waxanda ba su ma san tarihin yadda ake kafa qofofin ba, sun ilmantu da wannan waqa domin ta yi tasiri qwarai da gaske ga jama'a bayar da tarihi a baharance.
4.3 FAXAKARWA (WAQAR JAMI'A) 
Kamar yadda Lawal (2011) ya ce alqibla wannan waqa ta kalli rayuwar da ke faruwa a jami'a ne a nazarce, jami'a a halin da take ciki a yanzu, muhalli ne na ilmantarwa, tarbiyyantarwa da gina rayuwar xan Adam a kan wani ginshiqi mai xorewa zuwa gaba.
Haka kuma yake bigire ne na kamuwa da gurvatacciyar xabi'a ko samuwar vataccen ilimi mai kaiwa ga halaka a sakamakon tarayya ko musharaka da al'adu da xabi'u iri-iri a tare da mabambantan mutane da sukan halarci muhallai munana da na nagari. Shi ne abin da ya sa sai ka ga mutumin kirki ya je Jami'a halayyarsa ta sauya zuwa ta mutumin kawai. Mutumin banza kuma in ya yi katari sai ya koma nagari. Ba ana nufin ana zama a cikin aji a koyar da wani darasi na vatanci ba, face dai mu'amalar da ke kara-kaina a tsakanin Malami da xalibai yakan haifar da waxancan misalan da aka zayyano a sama. Alal misali a dubi wannan baiti:
"Na ga Lekcara mai koyarwa da faxar Allah
Na ga Lakcara mai koyarda don Allah
Na ga Lakcara mai tausan bayin Allah
Na ga Lakcara mai qaunar bayin Allah
Mai kwaikwayon halayen Manzon Allah"
Daga jin waxannan layukan waqa, za ka ji amon kalmomin faxakarwa na tsoron Allah da tausayin al'umma da qaunarsu tare da yin kwaikwayo da halayen Manzon Allah. Wannan waqa ta jami'a har yau tana mutuqar tasiri a cikin al'umma domin da zarar an sami wani Malami ya yi ba dai-dai ba ko xalibi a cikin jami'a, sai ka ji an ce daman Ala ya faxa a cikin waqarsa ta Jami'a.


4.4 BIJIREWA DA HANNUNKA MAI SANDA GA AL'UMMA (WAQAR      BUBUKUWA)
Waqar Bubukuwa tana daga cikin manyan-manyan waqoqin farko da Aminu Ala ya fito da ita ga al'umma, mai xauke da babban jigon Bijirewa shuwagabanni a bisa yadda sukan yi wa al'umma alqawari kafin su hau mulki, wanda daga baya idan kwalliya ta biya kuxin sabulu, sai na sama ya dinga danne na qasa. A dubi wannan baitin:
"Varayi a ban qasa atifishiyal muka qirqiro
Su ke addabarmu a ko'ina atifishiyal muka qirqiro
Musu fo wan nayin na arewa na qirqira muka qaqaro
Wahalar da muke ciki ita ta sakka suka bijjiro
Da rashin shuwagabanni adalai da rashin tsaro
Rayukanmu kamar kiyashi, fagen kulawa ba tsaro
Rabbi kai ne Rahimi, tsare qasar Nijeriya"
A nan mawaqin yana mai farkar da al'ummar arewa cewar varayin gwamnatin nan, ba fa Allah ne ya wajabta musu satar dukiyar al'umma ba, illa halin varnar nan an tsince ta ne a nan duniya wato atifishiyal ce. Matsalar da muke ciki na karyewar tattalin arziqi da hannun shuwagabanni, don su ke wawurar dukiyar qasa, su mayar da ita tasu.
  Ba su damu da kula da lafiyar al'umma ba, balle tsaron lafiyarsu da ta dukiyoyinsu,su dai kan su suka sani. Mawaqin ya fito fili ya ce:
Shuwagabanni na zamani
Masu hali na zamani
Malamai 'yan zamani
'Yan siyasar zamani
Talakawan zamani
Katankatanar zamani
Ta samu sakamakon Bubukuwa x 3
Wato sakon Bubukuwa aya ce ga dukan jama'a, ma'ana kowa ya shiga taitayinsa. A tsaya a yi aikin al'umma da kyau yadda za a amfana da juna, tare da samar wa kai kyakkyawar al'umma ta gari.
KAMMALAWA
A farkon wannan takarda an fara ne ta kawo ma'anar waqa rubutacciya da kuma waqar baka. An kuma bi diddigin asalin Kalmar Hausa da Hausawa da kuma iyakokin qasarta. Takardar ta tafi kai tsaye inda ta kawo tasirin waqoqin Aminu Ala a cikin al'umma a fagen ilimi da siyasa da tarihi da faxakarwa da kuma bijirewa. 






MANAZARTA
Adamu, U. M (2011). Sabon Tarihin Asalin Hauswa.Kaduna: Espee Printing and Advertising.
Adamu, M. (1978). Hausa Factor In West African History. Zaria: Ahmadu Bello University Press.
Adamu, M. (2010). The Major Landmarks in the Hisrory of Hausa Land. Sokoto:Trans-Akab Publishing Limited
Adamu, M. T. (1997). Asalin Hausawa Da Harshensu. Kano: Dan Sarkin Kura Publishers.
Bunza, A.M. (2006). Gadon Fexe Al'ada. Lagos: Tawal Nigeria Limited.
Xangambo, A. (2007). Xaurayar Gadon Fexe Waqa. Zaria: Amana Publishers.
Gusau, S.M. (2003). Jagoran Nazarin Waqa. Kano: Benchmark Publishers Limited.
Gusau, S.M. (2008). Waqoqin Baka A qasar Hausa: Yanaye-yanayensu da Sigoginsu. Kano: Benchmark Publishers.
Gusau, S. M. (1999). Tarbiyya A Idon Bahaushe. In Hausa Studies. Usman Danfodiyo University Sokoto. Vol.I No. I.
Gusau, S. M. (2005) Mawaxa Da Makaxan Hausa. Kano: Benchmark Publishers.
Smith, A. (1987). A Little New Light: Selected Historical Writings of Abdullahi Smith. Zariya: Abdullahi Smith Centre For Historical Research.
Lawal, M. (2011). Waqoqin Aminu Ladan Abubakar Alan Waqa. Littafi na Xaya. Kano: Iya Ruwa. Publishers.
Yahaya I. Y. Da Wani. (1986). Jagoran Nazarin Hausa. Zariya: Gaskiya Cooporation Limited.

Post a Comment

Dear readers, after reading the Content please ask for advice and to provide constructive feedback Please Write Relevant Comment with Polite Language.Your comments inspired me to continue blogging. Your opinion much more valuable to me. Thank you.

TASIRIN WAQA A CIKIN AL’UMMAR HAUSAWA: TSOKACI DAGA WASU WAQOQIN AMINU LADAN ABUBAKAR (ALAN WAQA).


     DAGA
               AHMAD S. BELLO 
        (08033551751)
                 SASHEN HAUSA
KWALEJIN ILIMI TA TARAYYA DA KE ZARIYA





TAKARDAR DA AKA GABATAR A WAJEN TARON MASOYA AMINU ALAN WAQA WANDA AKA YI A XAKIN TARO NA MAKARANTAR ADO   GWARAM DA KE KAN TITIN GIDAN NAMUN DAJI, KANO. 
                                         RANAR LAHADI, 08/10/2017.

1.0 GABATARWA
Wannan takarda za ta yi magana ne a bisa tasirin da waqa kan yi a cikin al'ummar Hausawa: Tsokaci daga wasu waqoqin Aminu Ala. Ko da yake ainihin batun da aka ba ni, an taqaita taken batun ne a kan tasirin waqa a cikin al'umma kawai. To, a nan sai na yi wa kaina tambaya, to, wace al'ummar ake so a nuna yadda waqa ta yi tasiri a kanta? Sannin kowa ne al'ummomin duniya suna da yawa, haka nan suke da yawa a Afirka, balle uwa uba Nijeriya. Nijeriyar ma ta arewaci al'ummominta suna da yawa, don haka wacce al'umma ake so mu xaura aikin nan a kai yanzu? Amsar ita al'ummar Hausawa. Don haka, na yi karambanin  qari a kan wannan batu da cewa, Tasirin Waqa a Cikin Al'ummar Hausawa: Tsokaci Daga Wasu Waqoqin Aminu Ala. Tun da taron nan an tsara shi domin karrama Aminu Ala da masoyansa, to, an taqaita tsokaci a bisa waqoqin nasa kawai a matsayin kadaddarta, domin ita ma takarda mai qaunar Aminu Ala ce, kuma tana mai nuna so da qauna tare da karramawa a gare shi a yau, tare da mu masoyan nasa baki xaya. Bigiren wannan takarda ya taqaita ne a bisa waqoqin da aka rubuta a cikin littafin Muhammad Lawal Barista, mai suna Waqoqin Aminu Ladan Abubakar Alan Waqa Littafi na Xaya. Don haka, me ake nufi da tasiri? Qamusun Hausa na Jami'ar Bayero (2007) ya ce tasiri yana nufin muhimmanci ko dangantaka ko qarfi. A nan za mu duba wane irin dangantaka waqoqoqin Aminu Ala suke da shi a cikin al'ummar Hausawa? Ina mai fata Allah Subhanahu wata'ala ya saka wa waxanda suka halarci wannan taro da alhairi, tare da waxanda suka yi qoqarin tabbatar da shi.Amin.
2.0 MA'ANAR WAQA
Kamar yadda Xangambo (2007) ya ce ya kamata mu tuna cewa akwai waqoqi iri biyu: rubutacciyar waqa da waqar baka wato waqar makaxa. Shin me ce ce waqa? Sau da yawa mutane sukan yi wannan tambaya muhawara ta harqe. Ko da yake ba nufin wannan takarda ba ne a kawo wannan mahawara, a nan, waqa wani saqo ne da aka gina shi kan tsararriyar qa'ida ta baiti, xango, rerawa, kari (bahari) amsa-amo (qafiya) da sauran qa'idojn da suka shafi daidaita kalmomi, zavensu da amfani da su, cikin sigogin da ba lalle ne haka suke a maganar baka ba. Gusau (2003) ya nuna cewar waqa tana zuwa ne a sigar gunduwowin zantuka waxanda ake kira baitoci ko xiyoyi. Kuma ake rerawa da wani irin sautin murya ta musamman.
Shi ma Yahaya (1984:2-3) ya ce: "waqa maganar hikima ce da ake rerawa ba faxa kurum ba wadda ke da wani saqo da ke qunshe cikin wasu kalmomi zavavvu, tsararru kuma zaunannu.
Idan muka kalli ma'anar da waxannan masana suka bayar a bisa waqa za a ga sun yi tarayya a bisa tsarawa da hikima da rerawa da saqo da zavavvun kalmomi tare da zamansu ko direwa. Wannan yana nuna mana cewa waqa daban take da zancen baka na yau da gobe, kuma tana xauke da wani saqo da take son isar wa ga al'ummar da aka tsara wa ga al'ummar tata kuma dominta.
3.0 HAUSA, HAUSAWA DA QASARTA
Qasar Hausa tana da girma qwarai da gaske, tana da yanayi (hali da ake ciki) kamar na damina da kaka da bazara da sanyi. A nan yana da muhimmanci a san ko ina ne qasar Hausa, ina ne iyakokinta, su wane ne makwabtanta. Wannan shi zai taimaka mana wajen qara fahimtar yadda yanayin qasar Hausa take da kuma yadda yanayinta yake kasancewa a cikin shekara. (Adamu, 1997), ya ba da iyakokin qasar Hausa ta amfani da taswirar qwallon duniya, aka yi amfani da layuka da aka zana domin qara saukaka gano wurare a bisa qwallon duniya kamar haka:
"….za a sami qasar Hausa a tsakanin layi na goma sha biyar (150N) zuwa na goma sha takwas (180N) na arewa da ikwaita; kuma tana tsakanin layi na takwas (80E) da na goma sha biyu (120E) a gabas da layin Greenwic"
Masu nazari a fannin lammuran qasa (Geography) sun ce, wannan hanya ita ce mafi karvuwa wajen fayyace kowane muhalli da ainihin mazauninsa a bisa doron qasa. An kasa kwallon duniya zuwa gida-gida ta amfani da wasu layuka guda biyu, wato layin longtitude wanda ya faro daga arewa zuwa kudu a kan qwallon duniya; sai kuma layin latitude wanda ya faro tun daga gabas zuwa yamma a kan kwallon duniya.
Adamu, (2011) ya bayyana inda ake kira qasar Hausa a wata maqala da ya gabatar sai aka fassara kamar yadda yake cewa a Turance:
Qasar Hausa ta faro ne tun daga Abzin a tsaunuka Air a shiyyar arewa (a qasar Nijar ta yau) zuwa wasu kilomitoci kudu da kufena da Turunku a Zazzau (a qasar Nijeriya ta yau) daga sashen kudu ke nan; ta kuma soma daga tsakanin kwarin Neja a shiyar yamma har zuwa iyakokin Nijeriya da Nijar a gabas
Wannan bayani na Adamu (2011), ya ba mu haske a kan farfajiyar da qasar Hausa take a doron qasa, domin ya kawo mana mahallin da ita kanta qasar Hausar take, ta yadda idan mutum ya xauki littafin taswirar kwallon duniya (atlas) zai iya hasashen ko ina ne qasar Hausa. Adamu (1997) ya qara da cewa:
Kasar Hausa a yau tana cikin Afirka ta Yamma a arewacin Nijeriya. Kuma a kwance ta tavo har cikin qasar Nijar wajen su Maraxi da wasu 'yan garuruwa, haka kuma daga gabas ta yi iyaka da wani yanki na Jamhuriyar Binin a gabar da kogin kwara, daga wajen kudu kuma ta yi iyaka da qabilun Gwari da kuma qabilun kudancin Zariya da na kudancin Bauci.
To idan muka kalli waxannan bayanai da suka gabata kallo irin na fahimta, muna iya kammalawa da cewa, yanzu kam mun fitar da muhalli ko farfajiya da ake kira qasar Hausa a fannin tarihi da fannin kimiyyar lamuran qasa (geography). Idan kuwa muka haxa waxannan bayani, za mu ga haqiqannin inda ita wannan qasa ta Hausa take a cikin farfajiyar Afirka.
A duk bayanan da muka gabatar, kowane xaya daga cikin su ya ba da muhallin da farfajiyar qasar Hausa take, ma'ana babu inda wani daga cikinsu ya yi takun saka da wani a wurin fayyace ta. Duk sun ba da bayani waxanda suka yi canjaras da juna. 
Masana ilimin labarin qasa, sun bayyana qasar Hausa da cewa wuri ne da ke da shimfixaxxiyar qasa a mafi yawanta, ana kuma samun wasu wurare masu tudu da kwari, akwai manyan duwatsu da tsaunuka. Daga arewacin qasar inda ake kira Sahara (Sahel), nan ne ake samun itatuwa marasa inuwa sosai. Sai kuma daga kudanci, wurin da ya fi yawan itatuwa masu duhu, wato sashen sabana (savannah).
Gusau, (2003) yana mai faxaxa wannan batu da cewa a arewacin qasar akwai wurare masu dausayi a sanadiyyar kusanci da tafkuna ko rafuka ko kuma xaya daga cikin gulaben da suka samu a sanadiyyar rarrabuwar igiyoyin manyan koguna da suka ratsa qasar wato; kogin Haxeja wanda ya faro daga Kano, ya yi gabas har zuwa tafkin Chadi. Akwai kuma kogin Rima wanda ya faro daga Zamfara ya gangara arewa zuwa Nijar sannan ya karkato kudu ya yi yamma da Sakkwato ya haxe da kogin Kwara. Shi kuwa kogin Kwara ya yi iyaka ne da qasar Hausa daga sashen yamma.
Adamu, (1997) ya yi bayani a kan yanayin qasar Hausa na shekara-shekara a inda yake cewa:
Qasar Hausa, tana da yanayin shekara-shekara iri biyu ne, lokacin damina da na rani. A lokacin damina ne wato tsakanin watan Mayu-Satumba ake samun ruwan sama, yawan ruwan da ake samu kima ne amma duk da haka yakan biya buqata wajen aikin gona. Lokacin rani yana farawa daga Oktoba zuwa Afrilu, rani ya kasu biyu; lokacin xari ko hunturu da lokacin zafi wato bazara. Bazara lokaci ne da rana take yin tsananin zafi iska takan tsaya cik. Sai dai kuma wani lokaci guguwa takan tashi daga wani wuri zuwa wancan.
Qasar Hausa ta kasance mai yanayi iri biyu wato damina da rani saboda irin halin da qasar take da shi, wato a wani vagare qasar tana da manyan itatuwa masu duhu kamar yankin qasar Zariya, sannan wani vangaren qasar tana da gajerun itatuwa kamar irin yankin qasar Sakkwato. Kasancewar hakan shi ya sa qasar Hausa take da yanayin shekara iri biyu. Bugu da qari, qasar Hausa wuri ne da ke da ma'adinai daban-daban a qarqashin qasa, kamar su kanwa da qarfe (jan karfe da bakin karfe da azurfa da sauransu), akwai kuma yumbu (qasa) wadda ake tubali na gini da kuma ginin tukwane da dai sauransu da ita.

3.1 Asalin Hausawa
Asalin Hausawa kamar yadda Smith (1984) ya bayyana cewa a tsakanin shekarar 1050 zuwa 1100 ta miladiya, waxansu 'yan qabilar Buzaye (Berbers) sun ratso sahara suka yi auratayya da wasu al'ummu daban. Wai a sanadin wannan cuxanya ne aka sami Hausawa da harshen Hausa.
Kazalika Smith (1984), ya kawo nasa ra'ayin mai kusanci da na Smith, wato ya amince da cewa akwai sauyin wurin zama da ya auku daga gabas zuwa kasar Tukururu, wanda ya yi sanadin samuwar Hausawa. Ya qara da cewa wannan qaura ta faru a shekarar 1350 miladiya.
Bunza, (1990) ya bayyana cewa, a wani ra'in, Hausawa dai suna zaune shekaru masu yawa da suka wuce, wai amma yarensu ba shi da suna, wai sai da Larabawa masu cinikin bayi suka zo qasar suka fara da yare mai kama da Larabci, amma yadda aka sauya wasu kalmomi a furucinsu sun sava da na Larabci.
Idan aka yi la'akari da bayanin wannan masanin, Hausawa dai mutane ne da suke zaune a qasar Hausa tun farkon ta. Ibrahim, da wasu (1982) suna da ra'ayin cewa, "Daxewar harshen Hausa a duniya ya dogara ne ga daxewar Hausawa. Wato ke nan tun a lokacin da 'yan Adam suka karkasu zuwa jinsi-jinsi, to a wannan ne aka sami qabilar Hausawa masu magana da Hausa. Bugu da qari wasu na da ra'ayin cewa Bayajidda (Abu Yazid) ya zo Daura ya tarar da mutane har da magajiyarsu a Daura. Abin nufi a nan dai, Hausawa suna da kafaffiyar daula. To a nan tambaya ita ce, kafin zuwan Bayajida da wane harshe suke amfani? Haka kuma, mutum zai iya tambayar yadda zance ya gudana tsakanin tsohuwar da Bayajida ya sauka a gidanta, wanda ya roqi ruwa a wurinta domin ya ba dokinsa. Ta kuma gaya masa cewa ba ta da ruwa, ta kuma labarta masa labarin Sarki macijiya, sannan ya nemi ta ara masa guga ya samo ruwa. Amsa a nan idan wannan batu haka yake, to Bayajida ya samu Hausa da Hausawa a mazauninsu, wato ba shi ne asalin Hausawa ba. Ashe ba abin mamaki ba ne idan mun ce Bayajida ya koyi Hausa kafin ya iso Daura ko kuma bayan ya zo Daura. 
Shi kuma Smith, (1987), ya nuna rashin amincewarsa da bayanin dangane da asalin Hausawa musamman ma cewa wai shekara dubu da suka wuce babu Hausawa. Shi yana ganin cewa kasa rarrabewa aka yi tsakanin asalin Hausawa da kuma asalin daular Hausawa da aka kafa a dalilin rashin fahimtar juna. Kazalika Malamin bai amince da cewa Hausawa sun samo asali a sakamakon auratayya tsakanin Berber (Buzaye) da kuma Tukururu da suka same su a wurin ba. Don haka ra'ayinsa ya karkata ko ya fi danganta Hausawa da harsuna 'yan gidan Chadi, irin su Margi da Bolawa da Ngizim da Buduma da Kotoko da jukun da Angas da Sayawa da sauransu. Haka nan yana ganin cewa Hausa ta raba hanya da waxannan harsuna shekaru dubbai da suka wuce. Masanin ya qara da cewa mai yiwuwa akwai dangantaka tsakanin harshen Berber da na Chadi, amma tun kafin sahara ta zama Hamada. Ya kara da cewa, babu shakka ba abu ne mai karvuwa ba a ce shekarau 960 da suka wuce babu Hausawa.
Shi kuma Adamu, (1978), a ra'ayinsa, Hausawa dai su ne daxaxxun mutane mazauna qasar Hausa da suke amfani da al'adun Hausawa kuma suna riqo da harshe Hausa da addininsu.
A nasa ra'ayin, Amfani, (2011) cewa ya yi, an tabbatar da cewa a can cikin tarihi akwai wani lokaci da mutane suka yi ta yin qaurace-qaurace daga yankin Tafkin Chadi suna yin yamma. Baban dalili yin waxannan qaurace-qaurace shi ne qeqashewar tafkin Chadi. Gulbin Kebbi da Tafkin Chadi akwai nisa qwarai kuma akwai makekiyar qasa. A lokacin qaurace-qauracen, waxansu mutane sun qarasa har gulbin Kebbi, waxansu kuwa iyakarsu tsaunukan Borno. Waxannan mutanen sun dade qwarai a wannan makekiyar kasa yadda har ma ba a san lokacin da suka zo ba. Ba a san su sosai ba sai a karni na sha biyar. Mutanen kabilu ne daban-daban, Hausawa da Bolawa da Ngizim da Manga da Margi da Buduma da Kotoko su ne manyan kabilun a ciki, Hausawa sun fi yawa kuma sun fi warwatsuwa cikin wannan makekiyar qasa.
Dangane da bayanan masana da aka kawo a sama, wannan bincike ya lura cewa kasar Hausa kasa ce mai fadi da yalwa. A halin da ake ciki, tana da al'ummomi daban-daban, kodayake dai Hausawa su ne mafi akasari a ciki. Kasar tana da yanayin rani bayan daukewat ruwan sama, lokacin kasar ke bushewa. Akwai kuma yanayin damina, lokacin da ake samun ruwan sama, ake kuma gudanar da noma. 
4.0 TASIRIN WAQOQIN AMINU ALA A CIKIN AL'UMMAR HAUSAWA
Waqoqin Aminu Ala sun yi tasiri a kusan duka fuskokin rayuwar al'ummar Hausawa tun daga haihuwa har i zuwa mutuwa. Domin zan iya bugun qirji in ce, waqoqin Aminu Ala sun tavo matakan rayuwar Hausawa a bisa haihuwa, aure da mutuwa. Kaxan daga cikin jigogin ginin waqoqin Aminu Ala sun haxa da Gargaxi da tunatarwa da yabo (Fulfulde Album da Angara Album), zumunci da wa'azi da farfaganda da son manzon Allah da tauhidi da tuba tare da kumawa ga Allah da zamantakewa da kyautayi da girmawa (Gwadabe Album da Fuju'a Album da JakadiyaAlbum), siyasa da kula da marayu da kyautatawa Malaman Addini da zaman lafiya da dogaro da kai da barin tadanci da barin shaye-shaye (Kamfa Album da Mulukiya Album da Zaman Lafiya da Lu'ulu'u Album da Bubukuwa Albuma) da sauran su. Bari na fara tsokaci a kan jigon ilimi wanda shi ne gishirin zaman duniya. Aminu Ala ya zayyano a cikin wata waqarsa mai taken "mu nemi ilimi" na xauko ta ne shekaran jiya ta layinsa na Istagaram, an nuno hoton Aminu Ala a cikin aji yana xaukar darasi, wanda sanadiyyara haka za mu iya cewa mai dokar barci bai yin gyangyaxi, inda yake kira ga al'umma da a je a nemi ilimi ga kaxan daga cikin abinda yake cewa:
"Mu nemi ilimi fitilar haskakawa
Haske na ilimi baya nashewa
Hasken da ko ina shi ke qyallawa
Ko wanda bai gani na fuskantowa"
A nan an fito qarara cewa ilimi fitilar haskakawa ce ga kowacce irin al'umma domin qarfin ilimin al'umma, qarfin arziqinta, mu dubi qasashen da suka ci gaba a duniyar yau a fagen qere-qere da kimiyya mene ne abin dogaronsu? Shi ne ilimi, misali qasashen Turai da Asia. Don haka a nan yana mai kira ga al'ummar Hausawa da a je a nemi ilimi, shi ma, duk da shekarunsa da hidindumu da ke gabansa bai hana shi komawa makaranta ba.
4.1 SIYASA (WAQAR BAQAR MALAFA)
Aminu Ala ya yi amfani da tunaninsa da fasaharsa wajen ba da gudunmuwarsa a fagen siyasar qasar Hausa a cikin al'ummarmu ta yau, a cikin wata waqa mai taken "Baqar Malafa Baqar Jarfa" wannan waqa ba qaramin tasiri ta yi ba a cikin al'ummar Hausawa domin jawo hankalin jama'a, lallai kar a sake zavar Jam'iyyar PDP a zaven shekarar 2015 da aka yi. Waqar tana mai nuni da lallai da ya kamata jama'a kan su ya waye, su yi amfani da quri'arsu domin a kawo sauyin sabuwar gwamnati APC wanda take kan mulki a wancan zamani.
"Baqar malafa Baqar jarfa
                      Mai shanye jinin jikin talaka
Allah kaxa guguwar sauyi
Buhari janaral ya karvi gari"
Mawaqin ya fito qarar inda yake nuna wa, al'umma cewa wannan karo, babu wani abu da ya rage face a zavi shugaba Muhammadu Buhari a matsayin shugaban qasa domin shi ne kawai wanda zai iya kawo waraka ga matsalolin Nijeriya. A qarshe waqar ta yi tasiri, jama'a sun bi, sun kuma zave shi. Domin an nuna Jam'iyar mai malafa, ba ta da wani aiki face shanye jinin talaka, don haka yana mai roqon Allah ya kaxa iskar goguwar sauyin da zai saukar da mulkin mai malafa, Buhari ya xare mulkin qasa, kuma Allah ya amsa.
4.2 TARIHI (WAQAR MASHIGAN KANO)
Waqar mashigan Kano, an rubuta wannan waqar don bayyana tarihin qofofin Kano da dalilin samuwarsu. A nan waqar ta yi tasiri wajen nusar da al'umma yadda akai qofofin Kano da dalilin kafa su misali qofar Nasarawa da qofar Xanagundi da Kabuga da qofar Na'isa da qofar Ruwa da sauransu. Misali ga wani baiti inda ya ce:
Bayarwa: Zan batu kan ababen tarihin Kanawa, wasu an banzantar wasu an bi an adanawa, mai yiwa yin hakan zai tinzirar da Kanawa a gurin kariya da abin da zan ambatuwa.
Amshi: Yau yabo zan yi wa abubuwan kambamawa, mashiga tak Kano abin gwanin armasawa.
Mawaqin ya fito kai tsaye yana mai nuni da cewa qofofin Kano yake son ya waqe su domin amfanin al'umma ga waxanda ba su san tarihinsu ba. Kuma qofofin nan abubuwan kambamawa ne da armasawa ga duk wanda ya san asalin yadda aka kafa su a tarihince. Haqiqa wannan waqa ta yi tasiri matuqa domin jama'a da dama waxanda ba su san tarihi ba, ko kuma waxanda ba su ma san tarihin yadda ake kafa qofofin ba, sun ilmantu da wannan waqa domin ta yi tasiri qwarai da gaske ga jama'a bayar da tarihi a baharance.
4.3 FAXAKARWA (WAQAR JAMI'A) 
Kamar yadda Lawal (2011) ya ce alqibla wannan waqa ta kalli rayuwar da ke faruwa a jami'a ne a nazarce, jami'a a halin da take ciki a yanzu, muhalli ne na ilmantarwa, tarbiyyantarwa da gina rayuwar xan Adam a kan wani ginshiqi mai xorewa zuwa gaba.
Haka kuma yake bigire ne na kamuwa da gurvatacciyar xabi'a ko samuwar vataccen ilimi mai kaiwa ga halaka a sakamakon tarayya ko musharaka da al'adu da xabi'u iri-iri a tare da mabambantan mutane da sukan halarci muhallai munana da na nagari. Shi ne abin da ya sa sai ka ga mutumin kirki ya je Jami'a halayyarsa ta sauya zuwa ta mutumin kawai. Mutumin banza kuma in ya yi katari sai ya koma nagari. Ba ana nufin ana zama a cikin aji a koyar da wani darasi na vatanci ba, face dai mu'amalar da ke kara-kaina a tsakanin Malami da xalibai yakan haifar da waxancan misalan da aka zayyano a sama. Alal misali a dubi wannan baiti:
"Na ga Lekcara mai koyarwa da faxar Allah
Na ga Lakcara mai koyarda don Allah
Na ga Lakcara mai tausan bayin Allah
Na ga Lakcara mai qaunar bayin Allah
Mai kwaikwayon halayen Manzon Allah"
Daga jin waxannan layukan waqa, za ka ji amon kalmomin faxakarwa na tsoron Allah da tausayin al'umma da qaunarsu tare da yin kwaikwayo da halayen Manzon Allah. Wannan waqa ta jami'a har yau tana mutuqar tasiri a cikin al'umma domin da zarar an sami wani Malami ya yi ba dai-dai ba ko xalibi a cikin jami'a, sai ka ji an ce daman Ala ya faxa a cikin waqarsa ta Jami'a.


4.4 BIJIREWA DA HANNUNKA MAI SANDA GA AL'UMMA (WAQAR      BUBUKUWA)
Waqar Bubukuwa tana daga cikin manyan-manyan waqoqin farko da Aminu Ala ya fito da ita ga al'umma, mai xauke da babban jigon Bijirewa shuwagabanni a bisa yadda sukan yi wa al'umma alqawari kafin su hau mulki, wanda daga baya idan kwalliya ta biya kuxin sabulu, sai na sama ya dinga danne na qasa. A dubi wannan baitin:
"Varayi a ban qasa atifishiyal muka qirqiro
Su ke addabarmu a ko'ina atifishiyal muka qirqiro
Musu fo wan nayin na arewa na qirqira muka qaqaro
Wahalar da muke ciki ita ta sakka suka bijjiro
Da rashin shuwagabanni adalai da rashin tsaro
Rayukanmu kamar kiyashi, fagen kulawa ba tsaro
Rabbi kai ne Rahimi, tsare qasar Nijeriya"
A nan mawaqin yana mai farkar da al'ummar arewa cewar varayin gwamnatin nan, ba fa Allah ne ya wajabta musu satar dukiyar al'umma ba, illa halin varnar nan an tsince ta ne a nan duniya wato atifishiyal ce. Matsalar da muke ciki na karyewar tattalin arziqi da hannun shuwagabanni, don su ke wawurar dukiyar qasa, su mayar da ita tasu.
  Ba su damu da kula da lafiyar al'umma ba, balle tsaron lafiyarsu da ta dukiyoyinsu,su dai kan su suka sani. Mawaqin ya fito fili ya ce:
Shuwagabanni na zamani
Masu hali na zamani
Malamai 'yan zamani
'Yan siyasar zamani
Talakawan zamani
Katankatanar zamani
Ta samu sakamakon Bubukuwa x 3
Wato sakon Bubukuwa aya ce ga dukan jama'a, ma'ana kowa ya shiga taitayinsa. A tsaya a yi aikin al'umma da kyau yadda za a amfana da juna, tare da samar wa kai kyakkyawar al'umma ta gari.
KAMMALAWA
A farkon wannan takarda an fara ne ta kawo ma'anar waqa rubutacciya da kuma waqar baka. An kuma bi diddigin asalin Kalmar Hausa da Hausawa da kuma iyakokin qasarta. Takardar ta tafi kai tsaye inda ta kawo tasirin waqoqin Aminu Ala a cikin al'umma a fagen ilimi da siyasa da tarihi da faxakarwa da kuma bijirewa. 






MANAZARTA
Adamu, U. M (2011). Sabon Tarihin Asalin Hauswa.Kaduna: Espee Printing and Advertising.
Adamu, M. (1978). Hausa Factor In West African History. Zaria: Ahmadu Bello University Press.
Adamu, M. (2010). The Major Landmarks in the Hisrory of Hausa Land. Sokoto:Trans-Akab Publishing Limited
Adamu, M. T. (1997). Asalin Hausawa Da Harshensu. Kano: Dan Sarkin Kura Publishers.
Bunza, A.M. (2006). Gadon Fexe Al'ada. Lagos: Tawal Nigeria Limited.
Xangambo, A. (2007). Xaurayar Gadon Fexe Waqa. Zaria: Amana Publishers.
Gusau, S.M. (2003). Jagoran Nazarin Waqa. Kano: Benchmark Publishers Limited.
Gusau, S.M. (2008). Waqoqin Baka A qasar Hausa: Yanaye-yanayensu da Sigoginsu. Kano: Benchmark Publishers.
Gusau, S. M. (1999). Tarbiyya A Idon Bahaushe. In Hausa Studies. Usman Danfodiyo University Sokoto. Vol.I No. I.
Gusau, S. M. (2005) Mawaxa Da Makaxan Hausa. Kano: Benchmark Publishers.
Smith, A. (1987). A Little New Light: Selected Historical Writings of Abdullahi Smith. Zariya: Abdullahi Smith Centre For Historical Research.
Lawal, M. (2011). Waqoqin Aminu Ladan Abubakar Alan Waqa. Littafi na Xaya. Kano: Iya Ruwa. Publishers.
Yahaya I. Y. Da Wani. (1986). Jagoran Nazarin Hausa. Zariya: Gaskiya Cooporation Limited.

No comments:

Post a Comment