0

Daga 

A ranar larabar karshen shekarar 2014 ne mawakan hausa suka fara bikin ranar mawakan hausa na Afrika wanda suka saba yi duk daya ga watan janairun sabuwar shekara a dakin taro na tunawa da Sardaunan Sakkwato sa Ahmadu Bello kan titin Alkali Road jihar Kaduna, sai dai wannan karon bikin ya sha bamban da na shekarun da suka gabata, shi dai wannan biki an fara yin sa ne tun a shekarar 2013 wanda mawaki Aminudden ladan Abubakar (ALA) ya assasa bisa sahalewar Farfesa Sa'idu Muhammad Gusau na Jami'ar Bayero da Hakimin cikin Birnin kano babban dan majalisar Sarki, Wamban Kano Alhaji Aminu Ado Bayero tare wasu mawaka Inda aka yi taron farko a Taskar Ala Global da ke kan titin Manona cikin karamar hukumar Tarauni a jahar Kano.

Taro na biyu shi ma an gudanar da shi ne a jahar kano a Darul-Tauheed kusa da kantin sayar da kaya na Jifatu da ke kan titin zariya road.

Sai dai su kansu mawakan da suka saba halartar wannan biki na shekara-shekara sun ce bikin wannan shekara ya fi na dukkan sauran shekarun baya haduwa.

A zantawarmu da Mawaki Aminu Ala ya sake yin karin bayani game da yadda suka tsara taron na bana inda ya ce babu shakka sun fuskanci kalubale dab da taron saboda wanda ya yi musu alkawarin daukar nau'in taron na bana har ana saura mako guda taron basu samu damar ganawa dashi ba, amma cikin ikon Allah gashi a yau suna yin taron yadda basu yi tsammani ba.

Bikin wanda aka soma tun talatin da daya ga tsohuwar shekarar 2014 a daren ranar Gwamnan Kaduna Mukhtar Ramalan Yero ya halarci wajen taron inda yaba musu da bisa yadda suka hade kansu suka samar da wata rana ta musamman daga cikin ranakun shekara suke ganawa a junansu, kuma nuna damuwar bisa gayyatarsa da suka yi a kurarren lokaci, a karshen jawabinsa ya yi kira da mawakan hausa cewa su dinga yin wakokin fadakar da al'umma domin samun zaman lafiya a kasa ya kuma nuna jin dadinsa da kyauta ta musamman da wakar Tsumagiya wadda Adam Zango ya rera a wajen taron ya kuma bayar da gudummuwar naira miliyan biyu akan mujallar mawaka da aka sayar a wajen taron a karshen jawabin ya nemi ganawar sirri da duk mawakin da ya san ya yi masa waka ya kuma yi wa kungiyar mawakan Hausa alkawarin gwamnati zata kula da lamarinsu.

A washe garin ranar alhamis daya ga watan sabuwar shekarar 2015 ita ce ranar da mawakan hausa suke kira sallar mawaka ko ranar mawaka inda mawaka da yawa suka fito suka yi baje kolin fasaharsu, sannan a wannan rana an karrama wasu mawaka wadanda suke bada gudummuwa wajen ciyar da al'umma gaba a cikin wakokinsu daga cikin mawaka aka karrama akwai:

Fati Nijar.

Zayyanu Akilu Aliyu.

Abubakar Mai Bibiyu.

Maryam Sangadali.

Adamu Hassan Nagudu.

Adam A Zango da sauransu

hakanan an gabatar da takadu guda biyu domin karawa juna sani

inda Farfesa Sa'idu Muhammad Gusau na Jami'ar Bayero Kano ya gabatar da takardar farko Mai taken Mawaka a mahangar al'umma sai kuma Takarda ta biyu wadda Farfesa Salisu Ahmad Yakasai na jami'ar Usman Danfodiya Sakkwato, ya gabatar

har tauraruwar Dallatun Zazzau Uwar gidan Gwamnan Kaduna Hajiya Fatima Ramalan Yero ta halarci taron inda itama ta yi kira ga mawakan cewa su mai da hankali wajen yin wakokin ciyar da al'umma gaba.

An kammala taron a ranar alhamis da misalin karfe shida na yammaci:

daga cikin manyan bakin da suka halarci taron akwai:

-Wamban Kano Alhaji Aminu Ado Bayero.

-Alhaji Ado Ahmad Gidan Dabino MON

-Wakilin Sarkin Zazzau

- Alhaji Isa Bello Ja

-Hajiya Bilkisu Yusif Ali

taron dai ya samu sambarka daga bakin dukkan mahalarta taro an kuma zabi jihar Bauchi a matsayin da za'a yi taron shekara mai zuwa.

Post a Comment

Dear readers, after reading the Content please ask for advice and to provide constructive feedback Please Write Relevant Comment with Polite Language.Your comments inspired me to continue blogging. Your opinion much more valuable to me. Thank you.

BIKIN RANAR MAWAKAN HAUSA TA BANA YA SAMU TAGOMASHI.


Daga 

A ranar larabar karshen shekarar 2014 ne mawakan hausa suka fara bikin ranar mawakan hausa na Afrika wanda suka saba yi duk daya ga watan janairun sabuwar shekara a dakin taro na tunawa da Sardaunan Sakkwato sa Ahmadu Bello kan titin Alkali Road jihar Kaduna, sai dai wannan karon bikin ya sha bamban da na shekarun da suka gabata, shi dai wannan biki an fara yin sa ne tun a shekarar 2013 wanda mawaki Aminudden ladan Abubakar (ALA) ya assasa bisa sahalewar Farfesa Sa'idu Muhammad Gusau na Jami'ar Bayero da Hakimin cikin Birnin kano babban dan majalisar Sarki, Wamban Kano Alhaji Aminu Ado Bayero tare wasu mawaka Inda aka yi taron farko a Taskar Ala Global da ke kan titin Manona cikin karamar hukumar Tarauni a jahar Kano.

Taro na biyu shi ma an gudanar da shi ne a jahar kano a Darul-Tauheed kusa da kantin sayar da kaya na Jifatu da ke kan titin zariya road.

Sai dai su kansu mawakan da suka saba halartar wannan biki na shekara-shekara sun ce bikin wannan shekara ya fi na dukkan sauran shekarun baya haduwa.

A zantawarmu da Mawaki Aminu Ala ya sake yin karin bayani game da yadda suka tsara taron na bana inda ya ce babu shakka sun fuskanci kalubale dab da taron saboda wanda ya yi musu alkawarin daukar nau'in taron na bana har ana saura mako guda taron basu samu damar ganawa dashi ba, amma cikin ikon Allah gashi a yau suna yin taron yadda basu yi tsammani ba.

Bikin wanda aka soma tun talatin da daya ga tsohuwar shekarar 2014 a daren ranar Gwamnan Kaduna Mukhtar Ramalan Yero ya halarci wajen taron inda yaba musu da bisa yadda suka hade kansu suka samar da wata rana ta musamman daga cikin ranakun shekara suke ganawa a junansu, kuma nuna damuwar bisa gayyatarsa da suka yi a kurarren lokaci, a karshen jawabinsa ya yi kira da mawakan hausa cewa su dinga yin wakokin fadakar da al'umma domin samun zaman lafiya a kasa ya kuma nuna jin dadinsa da kyauta ta musamman da wakar Tsumagiya wadda Adam Zango ya rera a wajen taron ya kuma bayar da gudummuwar naira miliyan biyu akan mujallar mawaka da aka sayar a wajen taron a karshen jawabin ya nemi ganawar sirri da duk mawakin da ya san ya yi masa waka ya kuma yi wa kungiyar mawakan Hausa alkawarin gwamnati zata kula da lamarinsu.

A washe garin ranar alhamis daya ga watan sabuwar shekarar 2015 ita ce ranar da mawakan hausa suke kira sallar mawaka ko ranar mawaka inda mawaka da yawa suka fito suka yi baje kolin fasaharsu, sannan a wannan rana an karrama wasu mawaka wadanda suke bada gudummuwa wajen ciyar da al'umma gaba a cikin wakokinsu daga cikin mawaka aka karrama akwai:

Fati Nijar.

Zayyanu Akilu Aliyu.

Abubakar Mai Bibiyu.

Maryam Sangadali.

Adamu Hassan Nagudu.

Adam A Zango da sauransu

hakanan an gabatar da takadu guda biyu domin karawa juna sani

inda Farfesa Sa'idu Muhammad Gusau na Jami'ar Bayero Kano ya gabatar da takardar farko Mai taken Mawaka a mahangar al'umma sai kuma Takarda ta biyu wadda Farfesa Salisu Ahmad Yakasai na jami'ar Usman Danfodiya Sakkwato, ya gabatar

har tauraruwar Dallatun Zazzau Uwar gidan Gwamnan Kaduna Hajiya Fatima Ramalan Yero ta halarci taron inda itama ta yi kira ga mawakan cewa su mai da hankali wajen yin wakokin ciyar da al'umma gaba.

An kammala taron a ranar alhamis da misalin karfe shida na yammaci:

daga cikin manyan bakin da suka halarci taron akwai:

-Wamban Kano Alhaji Aminu Ado Bayero.

-Alhaji Ado Ahmad Gidan Dabino MON

-Wakilin Sarkin Zazzau

- Alhaji Isa Bello Ja

-Hajiya Bilkisu Yusif Ali

taron dai ya samu sambarka daga bakin dukkan mahalarta taro an kuma zabi jihar Bauchi a matsayin da za'a yi taron shekara mai zuwa.

No comments:

Post a Comment