0


A ranar Asabar 20 ga Disamba, 2014 , kungiyar Tsangayar Adabin Hausa ta gabatar da taron sanin makamar aiki ga matasa maza da mata su talatin da biyar, inda aka nuna musu hanyoyin dabarun kasuwancin zamani da ilmin na'ura mai kwakwalwa da kuma kalubalen da ke cikin gyaran wayar salula.

Sannan a karshen taron kungiyar ta karrama wasu fitattun mutane da ke bayar da gudunmawa a fannonin rayuwa dabam - dabam. Wadanda suka hada da:

- Dr. Abdulkadir Koguna, Sardaunan Agadez

- Ado Ahmad Gidan Dabino MON

- Aminu Alan Waka

-Alhaji Aliyu Dangida

-Hakimin Tarauni Alhaji Ado Kurawa

-Shugaban Karamar Hukumar Tarauni Injiniya Mukhtar Umar Yarima

-Metron Salamatu Mu'azu

- Hajiya Bilkisu Yusuf Ali

- Hajiya Lami Sumayya Murtala

An gabatar da takardu ga mahalarta taron. Inda Malam Nasiru Wada Khalil, a takardarsa mai taken 'Matakan kafa kasuwanci da samun nasara' ya zayyano hanyoyin da ake bi a samu nasara a kasuwancin zamani. Ya nuna muhimmancin bincike da jajircewa da tunanin kawo wani abu sabo a matsayin hanyoyin kaiwa ga nasara.

Injiniya Yunusa Sha'aibu, a tasa takardar mai taken Kalubalen da ke cikin sana'ar gyaran waya' ya lissafo irin kalubalen da ke cikin sana'ar gyaran waya da irin fadi tashin da masu sana'ar ke shiga a yau da gobe. Sannan ya bukaci gwamnati ta samar da wani tallafi na musamman ga matasa domin samun ingantaccen ilmin gyaran wayar ta salula.

Takardar da Danladi Haruna ya gabatar mai taken, 'Ilimin kwamfuta a takaice', ya bayyana yadda na'urar kwamfuta ke aiki da abubuwan da ta kunsa da kuma takaitaccen bayani akan fasahar intanet. A karshe ya fadi cewa, ilmin kwamfuta ya zama wajibi ga kowa da kowa a wannan zamani.

Taron wanda aka gudanar a birnin Kano inda mahalarta suka nuna jin dadinsu game da ayyukan wannan kungiya. Da dama daga cikinsu, sun bukaci a sake samun wata rana domin a maimaita musu irin wannnan taron.

Shugaban kungiyar, Rabiu Muhammad Abu Hidaya, ya godewa Allah da ya ba su ikon gudanar da irin wannan taron a karo na uku. Ya kara da cewa nan ba da jimawa ba kungiyar za ta sake lalubo wani bangare daga al'ummar hausawa domin ta basu horo na musamman bisa al'amuran ci gaban rayuwa.

Malam Farouk Lawan Da'u wanda shine gabatarwa kuma sakataren tsare-tsare na kungiya shima ya nuna jin dadinsa da godiya ga Allah da ya basu damar yin wannan taro na lafiya ya kuma bukaci gwamnati da ta dinga shiga sha'anin kungiyoyi irin wadannan domin tallafa musu duba da cewa suna aiki tukuru wajen wayarwa da al'umma kai game da abinda ya shige musu duhu.

A jawabinsa na godiya kuwa a madadin wadanda aka karrama, Sardaunan Agadaz Dk Abdulkadir Koguna, ya yabawa wannan kungiya da ke hobbasa wajen bullo da abubuwan ci gaba a koda yaushe, sannan ya yi alkawarin ba da hadin kansa a dukkan abin da kungiyar ta sa a gaba.

An kammala taro da misalin karfe biyar na yamma.

Post a Comment

Dear readers, after reading the Content please ask for advice and to provide constructive feedback Please Write Relevant Comment with Polite Language.Your comments inspired me to continue blogging. Your opinion much more valuable to me. Thank you.

TARON TSANGAYAR ADABIN HAUSA



A ranar Asabar 20 ga Disamba, 2014 , kungiyar Tsangayar Adabin Hausa ta gabatar da taron sanin makamar aiki ga matasa maza da mata su talatin da biyar, inda aka nuna musu hanyoyin dabarun kasuwancin zamani da ilmin na'ura mai kwakwalwa da kuma kalubalen da ke cikin gyaran wayar salula.

Sannan a karshen taron kungiyar ta karrama wasu fitattun mutane da ke bayar da gudunmawa a fannonin rayuwa dabam - dabam. Wadanda suka hada da:

- Dr. Abdulkadir Koguna, Sardaunan Agadez

- Ado Ahmad Gidan Dabino MON

- Aminu Alan Waka

-Alhaji Aliyu Dangida

-Hakimin Tarauni Alhaji Ado Kurawa

-Shugaban Karamar Hukumar Tarauni Injiniya Mukhtar Umar Yarima

-Metron Salamatu Mu'azu

- Hajiya Bilkisu Yusuf Ali

- Hajiya Lami Sumayya Murtala

An gabatar da takardu ga mahalarta taron. Inda Malam Nasiru Wada Khalil, a takardarsa mai taken 'Matakan kafa kasuwanci da samun nasara' ya zayyano hanyoyin da ake bi a samu nasara a kasuwancin zamani. Ya nuna muhimmancin bincike da jajircewa da tunanin kawo wani abu sabo a matsayin hanyoyin kaiwa ga nasara.

Injiniya Yunusa Sha'aibu, a tasa takardar mai taken Kalubalen da ke cikin sana'ar gyaran waya' ya lissafo irin kalubalen da ke cikin sana'ar gyaran waya da irin fadi tashin da masu sana'ar ke shiga a yau da gobe. Sannan ya bukaci gwamnati ta samar da wani tallafi na musamman ga matasa domin samun ingantaccen ilmin gyaran wayar ta salula.

Takardar da Danladi Haruna ya gabatar mai taken, 'Ilimin kwamfuta a takaice', ya bayyana yadda na'urar kwamfuta ke aiki da abubuwan da ta kunsa da kuma takaitaccen bayani akan fasahar intanet. A karshe ya fadi cewa, ilmin kwamfuta ya zama wajibi ga kowa da kowa a wannan zamani.

Taron wanda aka gudanar a birnin Kano inda mahalarta suka nuna jin dadinsu game da ayyukan wannan kungiya. Da dama daga cikinsu, sun bukaci a sake samun wata rana domin a maimaita musu irin wannnan taron.

Shugaban kungiyar, Rabiu Muhammad Abu Hidaya, ya godewa Allah da ya ba su ikon gudanar da irin wannan taron a karo na uku. Ya kara da cewa nan ba da jimawa ba kungiyar za ta sake lalubo wani bangare daga al'ummar hausawa domin ta basu horo na musamman bisa al'amuran ci gaban rayuwa.

Malam Farouk Lawan Da'u wanda shine gabatarwa kuma sakataren tsare-tsare na kungiya shima ya nuna jin dadinsa da godiya ga Allah da ya basu damar yin wannan taro na lafiya ya kuma bukaci gwamnati da ta dinga shiga sha'anin kungiyoyi irin wadannan domin tallafa musu duba da cewa suna aiki tukuru wajen wayarwa da al'umma kai game da abinda ya shige musu duhu.

A jawabinsa na godiya kuwa a madadin wadanda aka karrama, Sardaunan Agadaz Dk Abdulkadir Koguna, ya yabawa wannan kungiya da ke hobbasa wajen bullo da abubuwan ci gaba a koda yaushe, sannan ya yi alkawarin ba da hadin kansa a dukkan abin da kungiyar ta sa a gaba.

An kammala taro da misalin karfe biyar na yamma.

No comments:

Post a Comment