0

Ranar Alhamis 13 ga watan maris 2014 ina zauna a gida ina dan Nazari sai na ji wayata ta soma ruri alamun a kawo mata agaji cikin hanzari na dauki wayar na duba lambar sardaunan Agadez ce Dr. Abdulkadir koguna, cikin sauri na kara a kunne na tare da yin sallama.

Bayan ya amsa min sai yake gaya min wai takardar gayyata ce ta sallar Buzaye tare da wankan Sarauta aka aiko masa daga Tanhiya ta Nijar, kuma ba zai samu damar halarta ba dan haka yana so na wakilce shi.

Na amsa masa da insha Allah zan je a nan ne ma yake gaya min akwai abokin tafiya wato Abubukar Abdurrahman Dodo na Jaridar Aminiya shima zai je daukar rahoto,

muka aje magana akan da safe zan fito sai mu hadu a gidan Sardaunan mu tafi, haka kuwa aka yi tunda misalin karfe bakwai na safiyar ranar na gama shirin tafiya daga nan kai tsaye Gidan Sardauna na nufa ban dade da zuwa ba sai ga Abokin tafiyata Mal. Abubakar Dodo ya shima ya iso dauke da kayansa.

Mun bar garin garin Kano da misalin 11 zuwa garin Daura.

Da yake ranar ta juma'ace a Fago muka yi sallar juma'a.

Karfe biyu daidai muka shiga garin Daura wata sa'a da muka samu shine muna zuwa muka samu motar Damagaram sa'a kan sa'a mun soma tafiya sai direban motar yake tambayar mu daga Damagaram ina zamu?

Muka ce masa Tanout muka nufa ashe shima can za shi dan haka muka hada masa kudin motar zuwa Tanout.

Tafiya ta soma tafiya cikin yan sa'o'i kadan muka yada zango a Damagaram muka aje fasinjijo muka yi sallah muka ci abinci bayan mun dan huta kadan, sai yan kamasho suka karawa motarmu fasinja muka nausa hari sai Tanout.

Daga Damagaram zuwa Tanout tafiyar Sa'a uku ce amma da yake hanya ba kyau sai da muka shafe awa hudu a gajiye likis muka isa garin ba mu zame ko ina ba sai gidan Gwamnan Tanout, sojoji ne suka mana iso zuwa cikin Gidan, bayan mun gabatar da kanmu a wurin Gwamna sai yake gaya mana ai tuni sako ya zo masa akan zuwanmu, gaskiya mun samu kyakkyawar tarba a wurin Gwamna bayan gajeriyar hira kai tsaye masauki aka kaimu.

Da safe bayan mun kintsa mun yi karin kumallo sai mota ta zo ta dauke mu zuwa ofishin Gwamna inda a nan za'a taru zuwa Tanhiya a nan naga Manyan mutane Mahukunta daga sassa daban-daban na kasar nijar,

bayan mun gaisa da Gwamnan Tanout sai ya shiga gabatar damu a wurin manyan baki.

Cikin fara'a da barkwanci muka gaisa da kowa har suna tsokanarmu da cewa mun zo kenan basu barinmu mu koma Nijeriya,

Daga nan Gwamnan Tanout ya jagorinci walimar da aka shiryawa manyan baki nan muka sake cika cikinmu, bayan an gama walima sai aka shirya sansanin tafiya mu dama tuni Gwamna ya hada mu da abokanan aiki na Gidan Radiyo da Talabijin din kasar shiyyar Damagaram Mai suna ORTN.

To da yake ni ina tare da kyamarar daukar hoton bidiyo sai naki shiga motar da gwamna ya sani na shiga landirobar sojoji da nufin idan an soma tafiya na dinga daukar masu tafiya.

Sojojin motar suka nuna rashin yardar su akan zamana a motar amma ni sam naki nace a nan zan zauna ban san lokacin da direban motar ya je ya gayawa gwamna ba sai kawai ganin gwamna na yi ya zo ya ce na koma motarmu haka nan na sauko na koma motarmu ina yan kunkuni.

Cikin yan mintina mu ka soma tafiya na dauka tafiyar irin ta Kano zuwa Damagaram ce ashe ba ita bace,

daji muka nausa tafiya muke muna dada shiga cikin Sahara kamar ba zamu dena ba ga hanyar ba kwalta shahara ce kawai ga gwajab-gwajab ashe ba karamin sa'a ba na samu dana dawo motarmu dan har wuntsilawa muke idan muka shiga wani kwarin, duk karsashina ya ragu tun ina cewa an kusa ana da saura har na gaji na dena tambaya.

Ina ji ma'aikatan gidan talabijin suna magana da zabarmanci suna dariya da alamu dani suke, sun ga na gaji.

Ban san lokacin dana yi bacci ba sai kawai ji na yi ana cewa malam tashi an zo,

dandazon rakuma na hango can nesa damu bayan mun karasa gurin taron baka jin komai sai ihun buzaye.

Mun je har an soma gabatar da taron amma muna zuwa sai aka dakatar da taron aka dauke mu tare da manyan baki zuwa masaukai.

Kafin nan dama kowa an tanadar masa masaukinsa domin ko wani daki da sunan mutanen da za'a sa wadanda aka gayyata.

ALLAH DAYA GARI BAMBAM.

Ban taba tsammanin zan ga dan adam a wannan gurin ba bayan doguwar tafiya da muka sha a baya daji ne iya ganinka kuma sahara ce zalla.

Sai gashi mun cimma gari ciki har da mutane

wani abin mamaki shine yanayin dakunan mutanen garin ba irin na arewancin Nijar bane dakunan irin na bukkokin nan ne wanda kofofin kanana ne sosai sai ka sunkuya da kyau sannan zaka shiga daki wannan su ake kira dakunan bugaje.

Bayan mun huta mun ci abinci mun yi sallar azahar da la'asar sai kuma muka dunguma zuwa wajen bikin, a ranar na ga asalin buzaye irin wadanda ake kira buzaye duk su ne a wajen suna ta wasannin al'ada kala-kala bayan an gama wasanni sai kuma aka shiga gabatar da manyan baki tare da makasudin taron.

Da yake sallar manoma suke kiranta sai shugaban harkar noma ya mike ya gabatar da sabbin kayan noma da gwamnatin kasar ta samar da kuma magungunan dabbobi wanda za'a dinga basu kyauta don inganta kiwonsu.

Daga nan kuma sai gwamnan Damagaram ya mike ya yi jawabi kan zaman lafiya a kasar nijar.

Sannan aka shiga wakoki daga bakin mawaka wadanda aka gayyata irinsu duda mai waka da Aliyu sai kuma mawakan garin Tanhiya suma sun nishadantar da mahalarta a wajen taron.

Daga nan kuma kai tsaye sai aka fara kiran buzaye mahaya rakuma na gari -gari domin su gaida manyan baki.

Garuruwan da suka samu halartar taron akwai.

Agadez.

Taskir.

Goure.

Tanhiya.

Daga nan sai aka shiga babban al'amari wato yi wa sabon sarkin Tanhiya nadi a matsayin sarki mai gafaka ana gama nadawa sarki rawani sai na ji buzayen nan sun gauraye wajen da ihu alamun mubaya'a ga sabon sarkin nasu Ahmad Aghali Ibbah.

Daga nan sai magajin gari ya yi kira ga sabon sarkin akan ya rike yan kasar sa da amana kamar yadda suka san shi dama mai amana ne.

An kira gwamnan Tanout ya yi jawabi da godiya ga mutanen garin Tanhiya dangane da yadda suke zaune lafiya da junansu duk da cewa suna da bambancin jinsi.

Daga nan sai sarki Ahmad Aghali Ibbah ya amshi abin magana ya yi jawabin godiya ga mahalarta taro sannan ya yi kira ga gwamnatin kasar nijar akan ta kawo mu Sabis na wayar salula saboda su dinga gaisawa da dangin su na nesa kasancewar nan inda suke daji ne da kuma tsaro a yankin nasu dan maganin barayi masu satar musu bisashe(Rakuma) haka nan ya yi korafi game da rashin asibiti a yankin nasu, inda yace Tanhiya babban gari ne, kuma akwai mata da yawa suna haihuwa amma ba asibiti dan haka yana kira ga gwamnatin kasar Nijar ta gina musu asibiti a wannan yanki nasu.

Daga karshe ya yi kyautar rakuma ga gwamnan Tanout dana damagaram bisa jajircewarsu wajen ganin taron ya yi yadda ake so.

Daga nan aka buga tambari tare da jawabin godiya da nufin gobe a karasa abinda ya rage.

To ganin an yi duk abin za'a yi a wannan rana sai mafi yawa daga cikin manyan bakin da suka zo kowa ya kama hanyar komawa gida ciki har da gwamnan Damagaram.

Washe gari Lahadi aka cigaba da sha'anin bukuwan sallah dana sarauta da yake buzayen jinsi-jinsi ne sai ya zamana shigarsu ma daban-daban ce.

Buzayen sun kasu kashi uku.

Akwai makerin buzu akwai Jan buzu da kuma buzaye Abzinawa wani abin al'ajabi basa auratayya a tsakaninsu, kowa sai dai ya auri jinsin sa.

Sannan wani karin abin mamaki a garin shine ba'a sallar juma'a, dalili kuwa shine basu da masallacin juma'a, sai dai duk ranar juma'a mutanen garin su taru a fadar sarki a yi sallar azahar sannan a yi jawabai daga nan kowa ya koma gida.

A wannan rana aka kira mahaya rakuma da suka zo daga gari-gari aka musu kyauta.

Sannan aka shiga wake-wake a wannan ranar kuma mawakan da suka nishadantar sun hada da Mawaki Abdallah daga jahar Aghadez da kuma wata tsohuwar mawakiyar garin mai kidan goge.

NA TSALLAKE RIJIYA DA BAYA.

Dana ga ana ta shagali a wurin taro sai na zame na shiga gari neman ruwa da yake ruwan roba muka ta fi dashi kuma duk ya kare gashi kuma ana ta kwallah rana, duk inda na je da kyar ake ban ruwa amma sai inga ruwan bai yi min ba, na tambaya ina suke samun ruwan suka nuna min wata hanya wai idan na bi ta zan samu ruwa to da yake ina tare da kyamarata sai na ji dadin hakan domin ina son in dauko inda suke samun ruwa musamman yadda na lura ana wahalar ruwa a yankin.

Na jima ina tafiya sai na fara hangen wani tarin abu nesa dani, ina matsawa kusa sai na lura ashe tarin rakuma ne da dabbobin buzayen suka kewaye wani abu, da kyar na isa wajen duk na galabaita kishirwa ta kama ni da yawa da isata na tarar da buzaye ne rakwacam su da matansu da tarin dabbobi ko wani buzu fuska rufe kuma rataye da takobi.

Aradu sai da na gwammace ban je gurin ba, domin wata rijiya na gani ban taba ganin irin ta ba, sai ko a tarihi, katti hudu ne a bakin rijiyar suke dauko gugan, kuma shanu ake daurawa wata doguwar igiya a yi ta duka sai sun yi tafiya mai nisa sannan gugan zai zo gaba su kuma buzayen sai su kama da kyar su fito da shi su zuba a wani katon duro da suka tanada.

Yanayin kallon da naga suna min sai nasha jinin jikina na ce musu ni bakon sarki ne daga Nijeriya ruwa na zo sha, suka nuna min wajen da zan sha ruwan ina zuwa na tarar da mutane da jakuna da rakuma, har da tinkiyoyi gami shanu duk suna shan ruwa a wata kwatanniya mamaki ya kamani na ce a raina yanzu mutanen basa tsoron cuta suke shan ruwa tare da dabbobi?

Ina tsaye sai na ji wata mata ta min magana cikin gurbatacciyar hausa "ke namiji jo ki sha ruwan" gaba na ya fadi yanzu wannan ruwan zan sha? Dana je wajen naga yadda ruwan yake sai da hantar cikina ta kada, ruwan ya zama kamar ruwan kwatami ga ledoji nan da yayi birjik a ciki,

duk da kishirwar da nake ji sai bazan iya shan ruwan nan ba, na ce mata na gode, na juyo zan dawo gida haba ai na ji kamar bazan iya taku goma ba zan fadi domin nasha rana ga kuma kishirwa, dole na juyo wajen matar nan na ce ta ban ruwan na sha, haka na rufe idununa ina addu'a, na sha ruwan nan sosai domin kishirwa ta ci karfina, bayan na gama sha sai dauko kudi na ba matar nan haba wa ashe ba'a matansu kudi sai na ji wani buzu ya kurma ihu ayyyiii "ya ce karya kake namiji ke bashi kudinshi yadda naga buzayen sun nufo ni sai na fara salati tsammani na tawa ta kare, suna zuwa sai suka amshi kudin dana bata suka dawo min dashi wani babba daga cikinsu "yace ka ce kai bakon sarki ne"?, na ce eh,

sai ya ce to ko bisashe(Rakuma) nawa ka kawo nan suka sha ruwa bakka biyan ko sisi je ka abinka, ni dai cikin tsoro na baro su.

Wata sabuwa in ji yan caca ina dawowa gari sai tarar da abokin tafiyata wato Abubakar dodo ya bi gwamnan Tanout sun tafi na kuma

dama tawagarmu ce kawai ta rage bata tafi ba, nan fa idona ya raina fata yanzu ya zan yi? Gashi kuma na ji sun ce ko a rakumi kafin mutum ya cimma babban gari sai ya kwana hudu a hanya.

Ina cikin zulumi sai na hangi mataimakin gwamnan Tanout can tare da sarki haba ai tuni raina ya yi fari, na je na tarbe shi muka gaisa ya yi mamaki da ya ganni ya ce, me kake a nan ba ta fi ba?

Na ce masa tafiya aka yi aka barni, sai ya ce to na yi hakuri na dan jira shi ya gama ganawa da sarki shi yanzu zai tafi, na masa to na koma gefe na zauna muka shiga hira ni da wani abokina buzu, yana ta bani labari garinsu da al'adunsu a nan na gane ashe idan suka ce fulani (Dosawa)Bararoji suke nufi, na ce masa wai zaman me suke a wannan daji ga gari can sun zo nan sun zauna?

Sai yace dani ai su nan zaman rakumansu suke, yanzu da zasu tatsi nono a jikin rakumi suka ba kamar yadda suka saba da tatsaba ko kuma suka ga rakumansu suna ramewa to a ranar zasu bar dajin su yi gaba, ya ce min a nan dana ke ganinsu akwai mai rakumi dari uku akwai mai dari biyu,

dana masa maganar abinci sai ya ce min indai da hatsi da kuma nonon rakuma su ai lafiya lau ne.

Muna tsaka da hira sai ga Mataimakin gwamnan Tanout ya fito muka yi sallama da sarki da abokina na shiga mota hari sai Tanout.

Ina zuwa Tanout na hadu da abokin tafiyata muka gaisa ya ce ai sun neme basu ganni ba, shine Gwamna ya ce su tafi za'a taho dani.

Daga nan muka yi sallama da Gwamnan Tanout tare da godiya muka shirya kayanmu hari sai gida Nijeriya.

Taron dai ya samu halartar mutane da dama daga kasashen ketare musamman yan yawon bude ido kuma an yi lafiya an gama lafiya.

Mun dawo gida iso gida Nijeriya lafiya, ranar litinin da misalin karfe daya na rana.

Post a Comment

Dear readers, after reading the Content please ask for advice and to provide constructive feedback Please Write Relevant Comment with Polite Language.Your comments inspired me to continue blogging. Your opinion much more valuable to me. Thank you.

ZIYARARMU GARIN TANHIYA JAMHURIYAR NIJAR


Ranar Alhamis 13 ga watan maris 2014 ina zauna a gida ina dan Nazari sai na ji wayata ta soma ruri alamun a kawo mata agaji cikin hanzari na dauki wayar na duba lambar sardaunan Agadez ce Dr. Abdulkadir koguna, cikin sauri na kara a kunne na tare da yin sallama.

Bayan ya amsa min sai yake gaya min wai takardar gayyata ce ta sallar Buzaye tare da wankan Sarauta aka aiko masa daga Tanhiya ta Nijar, kuma ba zai samu damar halarta ba dan haka yana so na wakilce shi.

Na amsa masa da insha Allah zan je a nan ne ma yake gaya min akwai abokin tafiya wato Abubukar Abdurrahman Dodo na Jaridar Aminiya shima zai je daukar rahoto,

muka aje magana akan da safe zan fito sai mu hadu a gidan Sardaunan mu tafi, haka kuwa aka yi tunda misalin karfe bakwai na safiyar ranar na gama shirin tafiya daga nan kai tsaye Gidan Sardauna na nufa ban dade da zuwa ba sai ga Abokin tafiyata Mal. Abubakar Dodo ya shima ya iso dauke da kayansa.

Mun bar garin garin Kano da misalin 11 zuwa garin Daura.

Da yake ranar ta juma'ace a Fago muka yi sallar juma'a.

Karfe biyu daidai muka shiga garin Daura wata sa'a da muka samu shine muna zuwa muka samu motar Damagaram sa'a kan sa'a mun soma tafiya sai direban motar yake tambayar mu daga Damagaram ina zamu?

Muka ce masa Tanout muka nufa ashe shima can za shi dan haka muka hada masa kudin motar zuwa Tanout.

Tafiya ta soma tafiya cikin yan sa'o'i kadan muka yada zango a Damagaram muka aje fasinjijo muka yi sallah muka ci abinci bayan mun dan huta kadan, sai yan kamasho suka karawa motarmu fasinja muka nausa hari sai Tanout.

Daga Damagaram zuwa Tanout tafiyar Sa'a uku ce amma da yake hanya ba kyau sai da muka shafe awa hudu a gajiye likis muka isa garin ba mu zame ko ina ba sai gidan Gwamnan Tanout, sojoji ne suka mana iso zuwa cikin Gidan, bayan mun gabatar da kanmu a wurin Gwamna sai yake gaya mana ai tuni sako ya zo masa akan zuwanmu, gaskiya mun samu kyakkyawar tarba a wurin Gwamna bayan gajeriyar hira kai tsaye masauki aka kaimu.

Da safe bayan mun kintsa mun yi karin kumallo sai mota ta zo ta dauke mu zuwa ofishin Gwamna inda a nan za'a taru zuwa Tanhiya a nan naga Manyan mutane Mahukunta daga sassa daban-daban na kasar nijar,

bayan mun gaisa da Gwamnan Tanout sai ya shiga gabatar damu a wurin manyan baki.

Cikin fara'a da barkwanci muka gaisa da kowa har suna tsokanarmu da cewa mun zo kenan basu barinmu mu koma Nijeriya,

Daga nan Gwamnan Tanout ya jagorinci walimar da aka shiryawa manyan baki nan muka sake cika cikinmu, bayan an gama walima sai aka shirya sansanin tafiya mu dama tuni Gwamna ya hada mu da abokanan aiki na Gidan Radiyo da Talabijin din kasar shiyyar Damagaram Mai suna ORTN.

To da yake ni ina tare da kyamarar daukar hoton bidiyo sai naki shiga motar da gwamna ya sani na shiga landirobar sojoji da nufin idan an soma tafiya na dinga daukar masu tafiya.

Sojojin motar suka nuna rashin yardar su akan zamana a motar amma ni sam naki nace a nan zan zauna ban san lokacin da direban motar ya je ya gayawa gwamna ba sai kawai ganin gwamna na yi ya zo ya ce na koma motarmu haka nan na sauko na koma motarmu ina yan kunkuni.

Cikin yan mintina mu ka soma tafiya na dauka tafiyar irin ta Kano zuwa Damagaram ce ashe ba ita bace,

daji muka nausa tafiya muke muna dada shiga cikin Sahara kamar ba zamu dena ba ga hanyar ba kwalta shahara ce kawai ga gwajab-gwajab ashe ba karamin sa'a ba na samu dana dawo motarmu dan har wuntsilawa muke idan muka shiga wani kwarin, duk karsashina ya ragu tun ina cewa an kusa ana da saura har na gaji na dena tambaya.

Ina ji ma'aikatan gidan talabijin suna magana da zabarmanci suna dariya da alamu dani suke, sun ga na gaji.

Ban san lokacin dana yi bacci ba sai kawai ji na yi ana cewa malam tashi an zo,

dandazon rakuma na hango can nesa damu bayan mun karasa gurin taron baka jin komai sai ihun buzaye.

Mun je har an soma gabatar da taron amma muna zuwa sai aka dakatar da taron aka dauke mu tare da manyan baki zuwa masaukai.

Kafin nan dama kowa an tanadar masa masaukinsa domin ko wani daki da sunan mutanen da za'a sa wadanda aka gayyata.

ALLAH DAYA GARI BAMBAM.

Ban taba tsammanin zan ga dan adam a wannan gurin ba bayan doguwar tafiya da muka sha a baya daji ne iya ganinka kuma sahara ce zalla.

Sai gashi mun cimma gari ciki har da mutane

wani abin mamaki shine yanayin dakunan mutanen garin ba irin na arewancin Nijar bane dakunan irin na bukkokin nan ne wanda kofofin kanana ne sosai sai ka sunkuya da kyau sannan zaka shiga daki wannan su ake kira dakunan bugaje.

Bayan mun huta mun ci abinci mun yi sallar azahar da la'asar sai kuma muka dunguma zuwa wajen bikin, a ranar na ga asalin buzaye irin wadanda ake kira buzaye duk su ne a wajen suna ta wasannin al'ada kala-kala bayan an gama wasanni sai kuma aka shiga gabatar da manyan baki tare da makasudin taron.

Da yake sallar manoma suke kiranta sai shugaban harkar noma ya mike ya gabatar da sabbin kayan noma da gwamnatin kasar ta samar da kuma magungunan dabbobi wanda za'a dinga basu kyauta don inganta kiwonsu.

Daga nan kuma sai gwamnan Damagaram ya mike ya yi jawabi kan zaman lafiya a kasar nijar.

Sannan aka shiga wakoki daga bakin mawaka wadanda aka gayyata irinsu duda mai waka da Aliyu sai kuma mawakan garin Tanhiya suma sun nishadantar da mahalarta a wajen taron.

Daga nan kuma kai tsaye sai aka fara kiran buzaye mahaya rakuma na gari -gari domin su gaida manyan baki.

Garuruwan da suka samu halartar taron akwai.

Agadez.

Taskir.

Goure.

Tanhiya.

Daga nan sai aka shiga babban al'amari wato yi wa sabon sarkin Tanhiya nadi a matsayin sarki mai gafaka ana gama nadawa sarki rawani sai na ji buzayen nan sun gauraye wajen da ihu alamun mubaya'a ga sabon sarkin nasu Ahmad Aghali Ibbah.

Daga nan sai magajin gari ya yi kira ga sabon sarkin akan ya rike yan kasar sa da amana kamar yadda suka san shi dama mai amana ne.

An kira gwamnan Tanout ya yi jawabi da godiya ga mutanen garin Tanhiya dangane da yadda suke zaune lafiya da junansu duk da cewa suna da bambancin jinsi.

Daga nan sai sarki Ahmad Aghali Ibbah ya amshi abin magana ya yi jawabin godiya ga mahalarta taro sannan ya yi kira ga gwamnatin kasar nijar akan ta kawo mu Sabis na wayar salula saboda su dinga gaisawa da dangin su na nesa kasancewar nan inda suke daji ne da kuma tsaro a yankin nasu dan maganin barayi masu satar musu bisashe(Rakuma) haka nan ya yi korafi game da rashin asibiti a yankin nasu, inda yace Tanhiya babban gari ne, kuma akwai mata da yawa suna haihuwa amma ba asibiti dan haka yana kira ga gwamnatin kasar Nijar ta gina musu asibiti a wannan yanki nasu.

Daga karshe ya yi kyautar rakuma ga gwamnan Tanout dana damagaram bisa jajircewarsu wajen ganin taron ya yi yadda ake so.

Daga nan aka buga tambari tare da jawabin godiya da nufin gobe a karasa abinda ya rage.

To ganin an yi duk abin za'a yi a wannan rana sai mafi yawa daga cikin manyan bakin da suka zo kowa ya kama hanyar komawa gida ciki har da gwamnan Damagaram.

Washe gari Lahadi aka cigaba da sha'anin bukuwan sallah dana sarauta da yake buzayen jinsi-jinsi ne sai ya zamana shigarsu ma daban-daban ce.

Buzayen sun kasu kashi uku.

Akwai makerin buzu akwai Jan buzu da kuma buzaye Abzinawa wani abin al'ajabi basa auratayya a tsakaninsu, kowa sai dai ya auri jinsin sa.

Sannan wani karin abin mamaki a garin shine ba'a sallar juma'a, dalili kuwa shine basu da masallacin juma'a, sai dai duk ranar juma'a mutanen garin su taru a fadar sarki a yi sallar azahar sannan a yi jawabai daga nan kowa ya koma gida.

A wannan rana aka kira mahaya rakuma da suka zo daga gari-gari aka musu kyauta.

Sannan aka shiga wake-wake a wannan ranar kuma mawakan da suka nishadantar sun hada da Mawaki Abdallah daga jahar Aghadez da kuma wata tsohuwar mawakiyar garin mai kidan goge.

NA TSALLAKE RIJIYA DA BAYA.

Dana ga ana ta shagali a wurin taro sai na zame na shiga gari neman ruwa da yake ruwan roba muka ta fi dashi kuma duk ya kare gashi kuma ana ta kwallah rana, duk inda na je da kyar ake ban ruwa amma sai inga ruwan bai yi min ba, na tambaya ina suke samun ruwan suka nuna min wata hanya wai idan na bi ta zan samu ruwa to da yake ina tare da kyamarata sai na ji dadin hakan domin ina son in dauko inda suke samun ruwa musamman yadda na lura ana wahalar ruwa a yankin.

Na jima ina tafiya sai na fara hangen wani tarin abu nesa dani, ina matsawa kusa sai na lura ashe tarin rakuma ne da dabbobin buzayen suka kewaye wani abu, da kyar na isa wajen duk na galabaita kishirwa ta kama ni da yawa da isata na tarar da buzaye ne rakwacam su da matansu da tarin dabbobi ko wani buzu fuska rufe kuma rataye da takobi.

Aradu sai da na gwammace ban je gurin ba, domin wata rijiya na gani ban taba ganin irin ta ba, sai ko a tarihi, katti hudu ne a bakin rijiyar suke dauko gugan, kuma shanu ake daurawa wata doguwar igiya a yi ta duka sai sun yi tafiya mai nisa sannan gugan zai zo gaba su kuma buzayen sai su kama da kyar su fito da shi su zuba a wani katon duro da suka tanada.

Yanayin kallon da naga suna min sai nasha jinin jikina na ce musu ni bakon sarki ne daga Nijeriya ruwa na zo sha, suka nuna min wajen da zan sha ruwan ina zuwa na tarar da mutane da jakuna da rakuma, har da tinkiyoyi gami shanu duk suna shan ruwa a wata kwatanniya mamaki ya kamani na ce a raina yanzu mutanen basa tsoron cuta suke shan ruwa tare da dabbobi?

Ina tsaye sai na ji wata mata ta min magana cikin gurbatacciyar hausa "ke namiji jo ki sha ruwan" gaba na ya fadi yanzu wannan ruwan zan sha? Dana je wajen naga yadda ruwan yake sai da hantar cikina ta kada, ruwan ya zama kamar ruwan kwatami ga ledoji nan da yayi birjik a ciki,

duk da kishirwar da nake ji sai bazan iya shan ruwan nan ba, na ce mata na gode, na juyo zan dawo gida haba ai na ji kamar bazan iya taku goma ba zan fadi domin nasha rana ga kuma kishirwa, dole na juyo wajen matar nan na ce ta ban ruwan na sha, haka na rufe idununa ina addu'a, na sha ruwan nan sosai domin kishirwa ta ci karfina, bayan na gama sha sai dauko kudi na ba matar nan haba wa ashe ba'a matansu kudi sai na ji wani buzu ya kurma ihu ayyyiii "ya ce karya kake namiji ke bashi kudinshi yadda naga buzayen sun nufo ni sai na fara salati tsammani na tawa ta kare, suna zuwa sai suka amshi kudin dana bata suka dawo min dashi wani babba daga cikinsu "yace ka ce kai bakon sarki ne"?, na ce eh,

sai ya ce to ko bisashe(Rakuma) nawa ka kawo nan suka sha ruwa bakka biyan ko sisi je ka abinka, ni dai cikin tsoro na baro su.

Wata sabuwa in ji yan caca ina dawowa gari sai tarar da abokin tafiyata wato Abubakar dodo ya bi gwamnan Tanout sun tafi na kuma

dama tawagarmu ce kawai ta rage bata tafi ba, nan fa idona ya raina fata yanzu ya zan yi? Gashi kuma na ji sun ce ko a rakumi kafin mutum ya cimma babban gari sai ya kwana hudu a hanya.

Ina cikin zulumi sai na hangi mataimakin gwamnan Tanout can tare da sarki haba ai tuni raina ya yi fari, na je na tarbe shi muka gaisa ya yi mamaki da ya ganni ya ce, me kake a nan ba ta fi ba?

Na ce masa tafiya aka yi aka barni, sai ya ce to na yi hakuri na dan jira shi ya gama ganawa da sarki shi yanzu zai tafi, na masa to na koma gefe na zauna muka shiga hira ni da wani abokina buzu, yana ta bani labari garinsu da al'adunsu a nan na gane ashe idan suka ce fulani (Dosawa)Bararoji suke nufi, na ce masa wai zaman me suke a wannan daji ga gari can sun zo nan sun zauna?

Sai yace dani ai su nan zaman rakumansu suke, yanzu da zasu tatsi nono a jikin rakumi suka ba kamar yadda suka saba da tatsaba ko kuma suka ga rakumansu suna ramewa to a ranar zasu bar dajin su yi gaba, ya ce min a nan dana ke ganinsu akwai mai rakumi dari uku akwai mai dari biyu,

dana masa maganar abinci sai ya ce min indai da hatsi da kuma nonon rakuma su ai lafiya lau ne.

Muna tsaka da hira sai ga Mataimakin gwamnan Tanout ya fito muka yi sallama da sarki da abokina na shiga mota hari sai Tanout.

Ina zuwa Tanout na hadu da abokin tafiyata muka gaisa ya ce ai sun neme basu ganni ba, shine Gwamna ya ce su tafi za'a taho dani.

Daga nan muka yi sallama da Gwamnan Tanout tare da godiya muka shirya kayanmu hari sai gida Nijeriya.

Taron dai ya samu halartar mutane da dama daga kasashen ketare musamman yan yawon bude ido kuma an yi lafiya an gama lafiya.

Mun dawo gida iso gida Nijeriya lafiya, ranar litinin da misalin karfe daya na rana.

No comments:

Post a Comment