0

Na kasance yar gidan masu akwai domin mahaifina mutumne mai tarin dukiya na yi aure cikin jin dadi da walwala duk da cewa bani kadai ba ce a gidan mijina akwai kishiyata amma kuma na fita fada a gunsa domin sai abinda na ce ganin bana rabo da yan silalla a tare dani kuma ana yawan aiko min da kayan alatu daga gidanmu.

Duk da cewa bani bace uwargida amma sai mijina ya mai dani uwargidan sai abinda na ce.

Duk duniya ba abinda na tsana irin kishiya na tsani koda jin labarinta sai gashi wai ni ce a gidan kishiya in banda kaddara.

Wannan damar dana samu a gurin mijina sai na yi amfani da ita wajen musguna mata ita da yaranta.

Ya'yan kishiyata uku biyu mata daya Namiji.

Ni kuwa ina da yara biyu duk maza

wannan ne dalilin da me gidana ya kara sona ganin daga zuwa na haifa masa yara biyu duk maza.

Na lura wannan al'amari ba karamin batawa kishiyata rai yake ba kawai sharewa take ni kuwa dana ga haka sai na shiga sabon salon kara kunsa mata bakin ciki domin kusan kullum sai na canja sabbin kaya kuma yawanci shi nake baiwa dinki ya kai min haka nan duk ranar da aka ce girki na ne sai in sa ya yo min cafane mai kyan gaske mu ci ni da yayana.

Haka kawai sai in kirkiri sharri in yi mata a gun mijinmu shi kuma ya yi ta mata masifu kala-kala har da barazanar saki, kullum ta Allah kafin in gaisheta ta gaishe ni.

Duk wani hakki da aka ce nawa ne kishiyata ta biya min kai hatta duk haihuwar dana yi kusan ita ke dawainiya da ni amma wannan bai sa na ji ina tausayinta ba kullum dada gallaza musu nake ita da ya'yanta.

Ana tsaka da wannan al'amari sai ciwo ya kamata wai ciwon zuciya da hawan jini an je asibiti sai aka ga ashe har zuciyarta ta kumbura kafin wani kwakkwaran mataki tace ga garinku nan.

Bayan rasuwarta da kamar wata biyu sai rikon yaranta ya dawo hannuna.

Ganin wannan damar ta dawo hannuna sai tsanar uwar yaran ta dawo kansu.

Na shiga gallaza musu ba dare ba rana kusan kullum sai na zane su haka kuma idan na ba 'ya'yana abinci da yawa su sai in basu kadan

kasancewar yaran suna zuwa makaranta sai Allah ya basu Nasibin haddace duk abinda aka koya musu kullum naga yaran nan sai in ji tsanar su ta kara kamani kai da abin ya ishe ni rana daya na fito na gayawa mijina cewa ni gaskiya ba zan iya zama da su ba dan haka yasan yadda zai yi dasu kasancewar babu yadda ya iya dani haka ya kwashi yaran ya mai da su can kauyensu wajen danginsa.

Wata rana na kwanta sai na yi mafarki wai gani na mutu an sanya ni a wuta ana ta yi min azaba kala-kala sakamakon tozarta kishiyata dana yi da kuma rukon sakainar kashin dana yiwa marayu.

Wannan mafarki ba karamin tsorata ni ya yi ba.

Kusan kullum cikin tunani nake wallahi abin ya tsaya min a rai.

Dan haka na rubuto muku wannan labarin nawa Aunty Lami ku bani shawara dan Allah ya zan yi?

Post a Comment

Dear readers, after reading the Content please ask for advice and to provide constructive feedback Please Write Relevant Comment with Polite Language.Your comments inspired me to continue blogging. Your opinion much more valuable to me. Thank you.

NADAMA


Na kasance yar gidan masu akwai domin mahaifina mutumne mai tarin dukiya na yi aure cikin jin dadi da walwala duk da cewa bani kadai ba ce a gidan mijina akwai kishiyata amma kuma na fita fada a gunsa domin sai abinda na ce ganin bana rabo da yan silalla a tare dani kuma ana yawan aiko min da kayan alatu daga gidanmu.

Duk da cewa bani bace uwargida amma sai mijina ya mai dani uwargidan sai abinda na ce.

Duk duniya ba abinda na tsana irin kishiya na tsani koda jin labarinta sai gashi wai ni ce a gidan kishiya in banda kaddara.

Wannan damar dana samu a gurin mijina sai na yi amfani da ita wajen musguna mata ita da yaranta.

Ya'yan kishiyata uku biyu mata daya Namiji.

Ni kuwa ina da yara biyu duk maza

wannan ne dalilin da me gidana ya kara sona ganin daga zuwa na haifa masa yara biyu duk maza.

Na lura wannan al'amari ba karamin batawa kishiyata rai yake ba kawai sharewa take ni kuwa dana ga haka sai na shiga sabon salon kara kunsa mata bakin ciki domin kusan kullum sai na canja sabbin kaya kuma yawanci shi nake baiwa dinki ya kai min haka nan duk ranar da aka ce girki na ne sai in sa ya yo min cafane mai kyan gaske mu ci ni da yayana.

Haka kawai sai in kirkiri sharri in yi mata a gun mijinmu shi kuma ya yi ta mata masifu kala-kala har da barazanar saki, kullum ta Allah kafin in gaisheta ta gaishe ni.

Duk wani hakki da aka ce nawa ne kishiyata ta biya min kai hatta duk haihuwar dana yi kusan ita ke dawainiya da ni amma wannan bai sa na ji ina tausayinta ba kullum dada gallaza musu nake ita da ya'yanta.

Ana tsaka da wannan al'amari sai ciwo ya kamata wai ciwon zuciya da hawan jini an je asibiti sai aka ga ashe har zuciyarta ta kumbura kafin wani kwakkwaran mataki tace ga garinku nan.

Bayan rasuwarta da kamar wata biyu sai rikon yaranta ya dawo hannuna.

Ganin wannan damar ta dawo hannuna sai tsanar uwar yaran ta dawo kansu.

Na shiga gallaza musu ba dare ba rana kusan kullum sai na zane su haka kuma idan na ba 'ya'yana abinci da yawa su sai in basu kadan

kasancewar yaran suna zuwa makaranta sai Allah ya basu Nasibin haddace duk abinda aka koya musu kullum naga yaran nan sai in ji tsanar su ta kara kamani kai da abin ya ishe ni rana daya na fito na gayawa mijina cewa ni gaskiya ba zan iya zama da su ba dan haka yasan yadda zai yi dasu kasancewar babu yadda ya iya dani haka ya kwashi yaran ya mai da su can kauyensu wajen danginsa.

Wata rana na kwanta sai na yi mafarki wai gani na mutu an sanya ni a wuta ana ta yi min azaba kala-kala sakamakon tozarta kishiyata dana yi da kuma rukon sakainar kashin dana yiwa marayu.

Wannan mafarki ba karamin tsorata ni ya yi ba.

Kusan kullum cikin tunani nake wallahi abin ya tsaya min a rai.

Dan haka na rubuto muku wannan labarin nawa Aunty Lami ku bani shawara dan Allah ya zan yi?

No comments:

Post a Comment