0

Daga 

Yanayi mai dadi, a lokacin yammaci, an yi ruwa an dauke kalar sararin samaniya ya yi fari kal gwanin ban sha'awa.

Tafe nake ina tunani kala-kala kan abubuwan da suka faru dani a rayuwa.

Allah sarki Manila ina jin har in koma ga mahaliccina ba zan taba mantawa dake a rayuwata ba,

ina sonki so na hakika,

Insha Allahu ke yar Aljanna ce,

na rasa dalili kusan kullum rana ta Allah sai na tunata a raina sau shurin masaki yanzu haka tafe nake zuwa kushewarta dan yi mata addu'a.

Manila dai wata kyakyawar yarinya ce da aka yi a garinmu, kuma Allah ya yi mata farin jinin mutane sosai domin kusan ko wani saurayi a garinmu burinsa shine a ce yau Manila shi take so.

Duk wannan tarin samarin na Manila bai hanani zuwa wajenta ba domin jarraba sa'ata, ranar dana gayawa abokaina cewa zan je wurin Manila zance dariya suka yi ta yi min wai ba zata soni ba.

Duk da cewa jikina ya yi sanyi da maganganunsu amma haka na jure na je a ranar dana fara zuwa wurin Manila ranar na samu karbuwa.

Tun daga wannan rana na zama abin birgewa a wurin abokaina kuma abin tsana a wajen wadanda na kore a gunta.

Soyayya mai tsabta ta kullu tsakaninmu da manila, ni kaina har mamaki nake wai me yasa Manila take sona?

Watarana na taba yi mata wannan tambayar sai tace hakanan take sona ita kanta bata san me yasa take sona ba.

Wannan shi ake kira kurman SO.

A cikin wannan hali na so da kaunar juna ne, ni da Manila muka yi aure.

Mutane da yawa sun yi mamakin wannan aure ganin cewa Manila tana da samari masu rufin asiri amma ta je ta auri mutumin da ko jarin kirki bai dashi.

Tunda muka yi aure da Manila komai nawa ya ja baya dama sana'ar sayar da burodi nake sai jarin nawa ya karye, na shiga yan dabaru.

A cikin wannan halin Manila ta samu juna biyu mai wahalarwa, domin haka muka yi ta dawainiyar zuwa asibiti.

Ita Manilan ita ke dan taimaka min da wasu abubuwan mu samu mu ci abinci ashe kayan dakinta take sayarwa ban sani ba

sai daga karshe na gane.

Tsanani ya kai tsanani a zamantakewarmu ga kuma tarin bashi da ya yi min yawa.

Kowa ya ganni ya san ina cikin damuwa.

Babu abinda ya fi damuna fiye da yadda mutane suka canja basa son taimako duk inda nasan zan je na samu kudi na je ba labari.

Sannan ga aikin duk ba labari.

Amma kusan kullum Manila cikin bani hakuri take tare da nuna min komai ya yi farko yana da karshe.

Ta kan ce dani Ado wallahi Allah bai manta damu ba yana sane damu kuma ka sani cewa ko wani mutum da irin jarabawar da ake masa ka yi addu'a Allah yasa mu ci jarabawar da ake mana.

Wani abin burgewa da Manila shine tsakar dare zan farka sai na ganta tana ta Nafilfili, idan na kalli Manila sai in ji tausayinta ya kamani wallahi duk wanda ya santa a da idan ya ganta yanzu sai ya yi mamaki domin duk kamanninta sun canja ta rame.

Duk randa ta je asibiti sai an rubuto mata abubuwan da zata dinga ci domin inganta lafiyarta kasancewar an ce jini ya mata karanci a jiki.

Ganin komai nawa ya tsaya ga mutanen da suke bina bashi suna min barazanar dauri,

Sai na yanke shawarar mayar da Manila gida ni kuma na tafi birni neman kudi,

Ado ka ji tsoron Allah a duk inda ka tsinci kanka karka yarda ka ci abinda ba hakkinka ba.

Zan cigaba da yi maka addu'a a koda yaushe.

Ina maka fatan Alkhairi Allah ya zamo gatanka a duk inda kake Allah ya bada sa'a kan abinda aka je nema.

Wadannan sune maganganun da Manila ta gaya min a lokacin da zamu rabu da ita.

Ban san kuka nake ba sai dai na ji dandanon gishiri a bakina sannan na lura ashe hawaye ne ke zuba daga fuskata.

Cikin sa'a na shiga birni domin ina shiga kwanaki kadan na samu aikin kamfani a wani kamfanin sarrafa fata kuma Alhamdulillahi tsawon wata uku da na yi a kamfanin na samu alkahiri.

Dan haka na yanke shawarar komawa kauye domin kula da Manila duba da cewa watan Haihuwarta ya kama.

Wannan shine abinda bazan taba mantawa dashi ba a tarihin rayuwata ba.

Anya akwai wanda ya kaini dandanar bakin ciki a rayuwa kuwa.

Rayuwa me yasa zaki mani haka?

Wayyo Allah rayuwata shike nan na shiga uku.

Shikenan na yi bankwana da farin cikina?

Haba Manila me yasa zaki mani haka, kin san bamu yi haka dake ba, me yasa zaki tafi ki barni.

Wannan shine sumbatun dana rika yi lokacin dana samu labarin rasuwar Manila...

Post a Comment

Dear readers, after reading the Content please ask for advice and to provide constructive feedback Please Write Relevant Comment with Polite Language.Your comments inspired me to continue blogging. Your opinion much more valuable to me. Thank you.

KURMAN SO


Daga 

Yanayi mai dadi, a lokacin yammaci, an yi ruwa an dauke kalar sararin samaniya ya yi fari kal gwanin ban sha'awa.

Tafe nake ina tunani kala-kala kan abubuwan da suka faru dani a rayuwa.

Allah sarki Manila ina jin har in koma ga mahaliccina ba zan taba mantawa dake a rayuwata ba,

ina sonki so na hakika,

Insha Allahu ke yar Aljanna ce,

na rasa dalili kusan kullum rana ta Allah sai na tunata a raina sau shurin masaki yanzu haka tafe nake zuwa kushewarta dan yi mata addu'a.

Manila dai wata kyakyawar yarinya ce da aka yi a garinmu, kuma Allah ya yi mata farin jinin mutane sosai domin kusan ko wani saurayi a garinmu burinsa shine a ce yau Manila shi take so.

Duk wannan tarin samarin na Manila bai hanani zuwa wajenta ba domin jarraba sa'ata, ranar dana gayawa abokaina cewa zan je wurin Manila zance dariya suka yi ta yi min wai ba zata soni ba.

Duk da cewa jikina ya yi sanyi da maganganunsu amma haka na jure na je a ranar dana fara zuwa wurin Manila ranar na samu karbuwa.

Tun daga wannan rana na zama abin birgewa a wurin abokaina kuma abin tsana a wajen wadanda na kore a gunta.

Soyayya mai tsabta ta kullu tsakaninmu da manila, ni kaina har mamaki nake wai me yasa Manila take sona?

Watarana na taba yi mata wannan tambayar sai tace hakanan take sona ita kanta bata san me yasa take sona ba.

Wannan shi ake kira kurman SO.

A cikin wannan hali na so da kaunar juna ne, ni da Manila muka yi aure.

Mutane da yawa sun yi mamakin wannan aure ganin cewa Manila tana da samari masu rufin asiri amma ta je ta auri mutumin da ko jarin kirki bai dashi.

Tunda muka yi aure da Manila komai nawa ya ja baya dama sana'ar sayar da burodi nake sai jarin nawa ya karye, na shiga yan dabaru.

A cikin wannan halin Manila ta samu juna biyu mai wahalarwa, domin haka muka yi ta dawainiyar zuwa asibiti.

Ita Manilan ita ke dan taimaka min da wasu abubuwan mu samu mu ci abinci ashe kayan dakinta take sayarwa ban sani ba

sai daga karshe na gane.

Tsanani ya kai tsanani a zamantakewarmu ga kuma tarin bashi da ya yi min yawa.

Kowa ya ganni ya san ina cikin damuwa.

Babu abinda ya fi damuna fiye da yadda mutane suka canja basa son taimako duk inda nasan zan je na samu kudi na je ba labari.

Sannan ga aikin duk ba labari.

Amma kusan kullum Manila cikin bani hakuri take tare da nuna min komai ya yi farko yana da karshe.

Ta kan ce dani Ado wallahi Allah bai manta damu ba yana sane damu kuma ka sani cewa ko wani mutum da irin jarabawar da ake masa ka yi addu'a Allah yasa mu ci jarabawar da ake mana.

Wani abin burgewa da Manila shine tsakar dare zan farka sai na ganta tana ta Nafilfili, idan na kalli Manila sai in ji tausayinta ya kamani wallahi duk wanda ya santa a da idan ya ganta yanzu sai ya yi mamaki domin duk kamanninta sun canja ta rame.

Duk randa ta je asibiti sai an rubuto mata abubuwan da zata dinga ci domin inganta lafiyarta kasancewar an ce jini ya mata karanci a jiki.

Ganin komai nawa ya tsaya ga mutanen da suke bina bashi suna min barazanar dauri,

Sai na yanke shawarar mayar da Manila gida ni kuma na tafi birni neman kudi,

Ado ka ji tsoron Allah a duk inda ka tsinci kanka karka yarda ka ci abinda ba hakkinka ba.

Zan cigaba da yi maka addu'a a koda yaushe.

Ina maka fatan Alkhairi Allah ya zamo gatanka a duk inda kake Allah ya bada sa'a kan abinda aka je nema.

Wadannan sune maganganun da Manila ta gaya min a lokacin da zamu rabu da ita.

Ban san kuka nake ba sai dai na ji dandanon gishiri a bakina sannan na lura ashe hawaye ne ke zuba daga fuskata.

Cikin sa'a na shiga birni domin ina shiga kwanaki kadan na samu aikin kamfani a wani kamfanin sarrafa fata kuma Alhamdulillahi tsawon wata uku da na yi a kamfanin na samu alkahiri.

Dan haka na yanke shawarar komawa kauye domin kula da Manila duba da cewa watan Haihuwarta ya kama.

Wannan shine abinda bazan taba mantawa dashi ba a tarihin rayuwata ba.

Anya akwai wanda ya kaini dandanar bakin ciki a rayuwa kuwa.

Rayuwa me yasa zaki mani haka?

Wayyo Allah rayuwata shike nan na shiga uku.

Shikenan na yi bankwana da farin cikina?

Haba Manila me yasa zaki mani haka, kin san bamu yi haka dake ba, me yasa zaki tafi ki barni.

Wannan shine sumbatun dana rika yi lokacin dana samu labarin rasuwar Manila...

No comments:

Post a Comment