0

KARFANCI RANAR SALLAH

Firgigit na farka sakamakon jin karar hayaniyar yara a tsakar gida kallona na farko kan agogo na kai shi karfe Takwas daidai agogon dakin ya nuna, cikin hanzari na mike na shiga bandaki domin wankan idi, ban fi minti biyar ba na fito har na gama wankan ni kaina nasan wankan Gwari na yi, (Kwaskwarima).

Turus na yi akan kayan sallar da zan sa gami fadin Allah ya tsinewa gugar dare, ashe jiya lokacin da nake goge kayan da zan sa yau duk na bata su da bakin gawayi kasancewar da Dutsin Chakwal na yi gugar.

Wasu tsofin kayana na sa ina wasu yan kunkuni.

Bakin titi na je na tsaya ina jiran mota zuwa masallacin idi, duk motar da ta zo a cike take zuwa ganin haka sai na yanke shawarar kawai in tafi a kafa.

Da gama wannan shawarar sai kawai na yanki hanya na somar tikar tafiya.

Kimanin minti talatin na kwashe a hanya sannan na isa masallaci, ina zuwa ana tayar da sallah.

Ana idar da sallar idi kawai sai na tuna ashe ban yi alwala ba na yi sallar, wani mugun abu ya zo ya tsaya min a wuya.

Can sai na ji wasu Mutane a bayana suna cewa ai kuwa masallacin hayin gangare basu tayar ba tunda nan sun idar ku zo mu je can.

Wani mai fiyawota na kira na sai na naira biyar na yi alwala.

Mun sha yar tafiya kafin zuwa masallacin duk na gaji tun kafin mu karasa masallacin na hangi mutane suna dawowa alamun an idar da sallah.

Tsaki na yi sannan na juyo na tsallako titi na hayo mota domin zuwa gida mun taba yar tafiya kenan sai kwandastan motar ya nemi da in bashi kudin mota Ras! Gabana ya fadi lokacin dana sanya hannuna a aljihu domin dauko kudin motar da zan ba yaron motar cikin hanzari na fara laluben sauren aljihunan kayana.

Babu inda ban duba ba amma babu kudin babu alamar su.

Wayet kwandastan ya fada, kiiii direban motar ya ja burki kana kwandastan yace dallah malam sauko irin wadannan mutanen barayine, ban iya ce masa komai ba na sauko, suka ja motar su suka yi gaba ni kuma na tsaya duk abin duniya ya dameni,

amma Allah ya tsine uwar barawon da ya sace min kudina domin duk kudin dana ke dasu ya kwashe.

Ganin tsayuwar bata da wani amfani sai na cigaba da tafiya a kafa zuwa gida, kasancewar jiya an kwana ana ruwa duk garin ya cabe babu dadin tafiya, fas ruwan kwatami ya wanke min jiki sakamakon wata katuwar mota da ta keta wani taron ruwa daya kwanta akan titi,

tsaye na yi ina kallon jikina duk ya 6aci ya yin da lokaci guda kuma na hangi motar can kan titi alamun direban motar bai san ya yi wannan abin ba, Allah ya isa na fada kana na ci gaba da tafiyata.

A gajiye likis na dawo gida duk raina a bace, wani karamin dana ya rugo a guje yana fadin baffa akuyar gidan su Talatu da barar da miyar mama.

Ina shiga gidan na tarar da katuwar tukunyar miyar a gefe ya yin da na hangi ruwan miyar a kasa.

Ka ga abinda shegiyar akuyar nan ta yi mana ko? wlh ina daki sai jin karar barewar miyar kawai na ji.

Duk wannan surutun da mai dakina take ni ban iya ce mata komai ba in banda kallonta kawai.

To yanzu sai ka kawo kudi a yi sauri a siyo wani kayan miyar kasan an jima su Amina(Kanwata) za su zo daukarwa Umma abincinta.(Mahaifiyata)

Wani mugun haushi ya kara turnike zuciyata yayinda na tuno bani da ko sisi a aljihuna...

Post a Comment

Dear readers, after reading the Content please ask for advice and to provide constructive feedback Please Write Relevant Comment with Polite Language.Your comments inspired me to continue blogging. Your opinion much more valuable to me. Thank you.

TAFIYA TA MASALLACIN IDI


KARFANCI RANAR SALLAH

Firgigit na farka sakamakon jin karar hayaniyar yara a tsakar gida kallona na farko kan agogo na kai shi karfe Takwas daidai agogon dakin ya nuna, cikin hanzari na mike na shiga bandaki domin wankan idi, ban fi minti biyar ba na fito har na gama wankan ni kaina nasan wankan Gwari na yi, (Kwaskwarima).

Turus na yi akan kayan sallar da zan sa gami fadin Allah ya tsinewa gugar dare, ashe jiya lokacin da nake goge kayan da zan sa yau duk na bata su da bakin gawayi kasancewar da Dutsin Chakwal na yi gugar.

Wasu tsofin kayana na sa ina wasu yan kunkuni.

Bakin titi na je na tsaya ina jiran mota zuwa masallacin idi, duk motar da ta zo a cike take zuwa ganin haka sai na yanke shawarar kawai in tafi a kafa.

Da gama wannan shawarar sai kawai na yanki hanya na somar tikar tafiya.

Kimanin minti talatin na kwashe a hanya sannan na isa masallaci, ina zuwa ana tayar da sallah.

Ana idar da sallar idi kawai sai na tuna ashe ban yi alwala ba na yi sallar, wani mugun abu ya zo ya tsaya min a wuya.

Can sai na ji wasu Mutane a bayana suna cewa ai kuwa masallacin hayin gangare basu tayar ba tunda nan sun idar ku zo mu je can.

Wani mai fiyawota na kira na sai na naira biyar na yi alwala.

Mun sha yar tafiya kafin zuwa masallacin duk na gaji tun kafin mu karasa masallacin na hangi mutane suna dawowa alamun an idar da sallah.

Tsaki na yi sannan na juyo na tsallako titi na hayo mota domin zuwa gida mun taba yar tafiya kenan sai kwandastan motar ya nemi da in bashi kudin mota Ras! Gabana ya fadi lokacin dana sanya hannuna a aljihu domin dauko kudin motar da zan ba yaron motar cikin hanzari na fara laluben sauren aljihunan kayana.

Babu inda ban duba ba amma babu kudin babu alamar su.

Wayet kwandastan ya fada, kiiii direban motar ya ja burki kana kwandastan yace dallah malam sauko irin wadannan mutanen barayine, ban iya ce masa komai ba na sauko, suka ja motar su suka yi gaba ni kuma na tsaya duk abin duniya ya dameni,

amma Allah ya tsine uwar barawon da ya sace min kudina domin duk kudin dana ke dasu ya kwashe.

Ganin tsayuwar bata da wani amfani sai na cigaba da tafiya a kafa zuwa gida, kasancewar jiya an kwana ana ruwa duk garin ya cabe babu dadin tafiya, fas ruwan kwatami ya wanke min jiki sakamakon wata katuwar mota da ta keta wani taron ruwa daya kwanta akan titi,

tsaye na yi ina kallon jikina duk ya 6aci ya yin da lokaci guda kuma na hangi motar can kan titi alamun direban motar bai san ya yi wannan abin ba, Allah ya isa na fada kana na ci gaba da tafiyata.

A gajiye likis na dawo gida duk raina a bace, wani karamin dana ya rugo a guje yana fadin baffa akuyar gidan su Talatu da barar da miyar mama.

Ina shiga gidan na tarar da katuwar tukunyar miyar a gefe ya yin da na hangi ruwan miyar a kasa.

Ka ga abinda shegiyar akuyar nan ta yi mana ko? wlh ina daki sai jin karar barewar miyar kawai na ji.

Duk wannan surutun da mai dakina take ni ban iya ce mata komai ba in banda kallonta kawai.

To yanzu sai ka kawo kudi a yi sauri a siyo wani kayan miyar kasan an jima su Amina(Kanwata) za su zo daukarwa Umma abincinta.(Mahaifiyata)

Wani mugun haushi ya kara turnike zuciyata yayinda na tuno bani da ko sisi a aljihuna...

No comments:

Post a Comment